𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaiku Mal. Khamis Ina maka fatan Alkhairi 🙌🏽 Ubangiji Allah ya saka maka da Alkhairi irin kokari da kake yi da jama'a, Allah ya kara maka lafiya da nisan kwana mai Albarka.👏🏼 Mal. Khamis ina da tambaya ina so sanin falalar da fa'idan yin Aure Bisa Alkur'ani Da Sunnah.?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Walaikum sallam warahmatahi
wabarkatahu;
Aure yana da falala da
alkhairai masu yawa a musulunci da kuma rayuwar ɗan
adam ta yau da kullum. Shari'ar musulunci ta kwadaitar da yin aure domin yana
kawo albarka, tsari, da kuma lada mai yawa ga ma'aurata waɗanda
suka yi shi a matsayin Sunnar Ma'aiki (Sallallahu Alaihi Wa Sallam), kuma suka
kiyaye dokokin shi.
Manzon Allah (Sallallahu
Alaihi Wasallam) ya kwaɗaitar da al'ummarsa akan
suyi aure. Ya ce: "Ku auri Mafi soyuwa agareku cikin mata kuma masu
haihuwa, domin dayawanku zanyi alfahari ranar alkiyama" kuma ya ce:
"aure sunna-ta ne, duk wanda ba ya kwaɗayin
sunnah-ta, to ba ya tare dani".
An ruwaito Daga cikin manyan
ɗaliban
Abdullahi ɗan Abbas wato Abdullahi bn Jubairi Ya ce
Abdullahi ɗan Abbas ya tambaye shi shin kayi aure?
Sai ya ce bai yi ba, sai ya ce masa kayi aure domin mafi alherin wannan al'umma
yana da aure. Wato yana nufin Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) da manyan
sahabbansa duk suna da aure don haka idan so kake kabi sunnar su to kayi aure.
An karɓo
hadisi daga Abdullahi ɗan Mas'ud (Allah Ya kara
masa yarda), Manzon Allah (Sallallahu Alaihin Wasallam) Ya ce, ya ku taron
matasa duk wanda ya samu iko daga cikin ku, toh yayi aure domin shi ne yafi
taimakawa wajan rintse gani kuma shi ne yafi taimakawa wajan kare farji daga
aikata zina, wanda bai samu iko ba toh na umarce shi da yin azumi domin azumi
garkuwace gare shi. Bukhary da Muslim ne suka ruwaito shi. Bukhari 5065.Muslim
1400.
Allah Ya faɗa a
cikin Suratun Nisaa, inda Ya ce;
...فَانْكِحُوۡا
مَا طَابَ لَـكُمۡ مِّنَ النِّسَآءِ مَثۡنٰى وَثُلٰثَ وَرُبٰعَ ۚ فَاِنۡ خِفۡتُمۡ
اَلَّا تَعۡدِلُوۡا فَوَاحِدَةً اَوۡ مَا مَلَـكَتۡ اَيۡمَانُكُمۡ ؕ ذٰ لِكَ
اَدۡنٰٓى اَلَّا تَعُوۡلُوۡا ؕ
...ku auri abin da ya yi
muku daɗi
daga mata; biyu-biyu, da uku-uku, da huɗu-huɗu.
Sa'an nan idan kun ji tsoron ba za ku yi adalci ba, to, (ku auri) guda ko kuwa
abin da hannayenku na dama suka mallaka. Wannan shi ne mafi kusantar zama ba ku
wuce haddi ba. (Surah: An-Nisaa, Ayat: 3).
وَمِنۡ
اٰيٰتِهٖۤ اَنۡ خَلَقَ لَكُمۡ مِّنۡ اَنۡفُسِكُمۡ اَزۡوَاجًا لِّتَسۡكُنُوۡۤا
اِلَيۡهَا وَجَعَلَ بَيۡنَكُمۡ مَّوَدَّةً وَّرَحۡمَةً ؕ اِنَّ فِىۡ ذٰ لِكَ
لَاٰيٰتٍ لِّقَوۡمٍ يَّتَفَكَّرُوۡنَ
"Kuma akwai daga ayoyinsa,
Ya halitta muku matan aure daga kanku, domin ku natsu zuwa gare ta, kuma Ya
sanya soyayya da rahama a tsakaninku. Lalle a cikin wancan akwai ayoyi ga mutane
masu yin tunani. (Surah: Ar-Room, Ayat: 21).
وَلَقَدۡ
اَرۡسَلۡنَا رُسُلًا مِّنۡ قَبۡلِكَ وَ جَعَلۡنَا لَهُمۡ اَزۡوَاجًا وَّذُرِّيَّةً
ؕ وَمَا كَانَ لِرَسُوۡلٍ اَنۡ يَّاۡتِىَ بِاٰيَةٍ اِلَّا بِاِذۡنِ اللّٰهِ ؕ
لِكُلِّ اَجَلٍ كِتَابٌ
"Kuma lalle ne haƙĩƙa Mun aika waɗansu
manzanni, daga gabaninka, kuma Muka sanya matan aure a gare su da zuriyya, kuma
ba ya kasancẽwa ga wani Manzo ya
zo da wata aya, sai da iznin Allah. Ga kowane ajali akwai littafi. (Surah:
Ar-Ra'd, Ayat: 38).
Manzon Allah (Sallallahu
Alaihin Wasallam) Ya ce; "Wanda yayi aure, hakika ya kammala rabin Addinin
sa, toh ya ji tsoron Allah a sauran rabin" Watau ibadar da aka halicce ka
don kayi ta, idan kayi aure, Allah Subhanahu Wa Ta'ala Ya ba ka rabin ta Ƙyauta.
Manzon Allah (Sallallahu
Alaihin Wasallam) Ya ce hakika idan ɗayan
ku ya ga wata mace sai ta kayatar da shi toh ya tafi wajan iyalin sa, hakika
yin hakan zai mayar da abin da ya ji a zuciyar sa. Muslim ne ya ruwaito shi
(hasanun sahihun).
Daga Abdullahi ɗan
Amr RA ya ce : Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) Ya ce: Duniya wani jin
daɗi
ce, amma mafi alherin jin daɗinta shi ne auren mace ta
gari. Muslim 1467.
Abu zarrin RA ya ruwaito,
Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) Ya ce: Idan kuka sadu (jima'i) da iyalanku
za a baku lada, sai sahabbai suka ce, yaya ɗayanmu
zai biya sha'awar sa kuma a bashi lada? Sai ya ce ku bani labari, idan yayi
zina ba za a rubuta masa alhakki ba? Sai suka kwarai, sai ya ce to haka za a
bashi lada idan ya kwanta da iyalansa. Muslim 1006. Abu Dauda 1286.
Abdullahi ɗan
Masud yana cewa Da zai zama saura kwana ɗaya
duniya ta tashi, zan so ace nayi aure a wannan lokacin (Musannnaf Ibn abi
Shaibah 3/454 ).
Ibn Abbas R.A, sahabin
Annabi (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) Ya ce "Ku yi aure, domin kwana guda
da aure shi ne mafi alheri daga ibadar shekara dubu". Waɗannan
hadisan akwai su cikin Buguyatul Muslimina.
Fa’idodin da suke cikin aure
ba za su Kididdigu ba amma ga wasu kaɗan
daga ciki za mu lissafo kamar haka;
1. Yin aure biyayya ne ga
Umurnin Allah da Manzon Allah (Sallallahu Alaihin Wasallam).
2. Yin aure yana sanya
Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wa Sallam) farin ciki a ranar lahira. Ya ce “Ku
yi aure ku hayayyafa domin ni zan yi ma sauran al’ummomi alfahari da ku a ranar
Alkiyamah”.
3. Ta dalilin aure za ka
samu wanda zai fito ta jikin ka, har ya girma yana kalmar Shahada!!
4. Ta dalilin aure ne za ka
samu zuriyar da za su yi maka addu’a bayan rasuwar ka wannan yana daga cikin
ayyukan da ladan su ba zai yanke ba har abada.
5. Yin aure ya kan zama
dalilin runtsewar idanun mutum daga kalle kallen haramun, sannan ya kare masa
al’aurar sa daga Zina.
6. Ta dalilin aure ne za ka
samu damar taimaka ma ƴar
uwar ka Musulma, ka aure ta, ka kiyaye ta kenan daga Zina.
7. Ta dalilin aure ne za ka
samu cikar Addinin ka, da ninkawar ladan ka fiye da wanda ba su da aure.
8. Ta dalilin aure ne za ka
samu ladan ciyar da Matar ka, da daukar nauyin ta, da ladan samar mata da
Mazaunin da za ta rayu.
9. Ta dalilin aure ne za ka
samu damar Qara yawan Musulman duniya ta hanyar haihuwar da za ka samu.
10. Ta dalilin aure ne za ka
samu damar karkatar da himmar ka daga kan nemen biyan bukatar ka ta hanyar
haram izuwa ga hanyar halal. Da kuma samun ladan saduwa da iyalan ka.
11. Za ka samu lada mai
girma sosai idan har Allah Ya azurta ka da ƴa’ya mata guda biyu, kuma kayi
hakuri da su ka kyautata musu, ka kyautata tarbiyyar su, su za su zama garkuwar
ka daga shiga wuta.
12. Idan har ƴa’yan
ka guda biyu suka rasu, kuma kayi hakuri, toh Allah zai shigar da kai Aljannah
saboda wannan.
13. Ta dalilin aure za ka
samu Qaruwar mutuncin ka da darajar ka a cikin al’ummah, ka shiga sahun mutanen
da za su iya jagorantar lamuran rayuwar al’ummah.
14. Ta dalilin aure ne zaka
samu taimakon Allah cikin lamarin ka. Kamar yadda Manzon Allah (Sallallahu
Alaihi Wa Sallam) Yake cewa: mutum uku, hakki ne akan Allah ya taimake su. ① wanda zai yi aure don nufin
kame mutuncin sa. ②
bawa wanda yake neman ‘yancin sa saboda ya samu daidaituwa (a cikin addini). ③ mujahidi (mai yakin daukaka
addinin Allah).
Muna tunatar da matasa da ƴan mata da suke da ikon yin aure, lallai
a je ayi aure, a rage burin duniya. Kullum rayuwa tafiya take yi mutuwa zuwa
yake yi babu notice, ku dubi duk waɗannan
garaɓasar
amma ban da Tuzurai da Gwagware Mata da Maza, su ba za su samu ba. Fatan mu duk
masu niyyar Aure irin mu Allah Ya Mana jagoranci, Ya hore mana daga falalar Sa Ameen.
Ya Allah ga bayin Ka suna
son Ɗabbaka umarnin Manzon Ka (Sallallahu
Alaihin Wasallam) Ya Allah, wanda ba Shi da kuɗin
yin Aure Ya Allah Ka ba shi, irin mu kenan, wanda kuma yake da shi amma bai
samu halin yi ba Ya Allah Ka ba shi Ikon yi. Ya Allah Ka sa mu Auri masu Taqwa
da kwantar mana da hankalin mu a duk lokacin da muke cikin wani hali sannan su
zama hanyar shigar mu Aljannah Ameen Ya Yayyu Ya Qayyum.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.