𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamualaikum malam fatan an wuni lafiya malam inada tambaya malam akwai wata kawata da take cikin wani hali malam tace Dan Allah mene ne makomarta ta aikata san zuciyarta ne ta je wurin wata hajiya ta yi amfani da ita mace da mace Wanda amma daga wannan Rana ta yi nadama ba kuma tasakeyi ba ta ji tsoron Allah yashigeta shi ne tace shin Allah zai karbi tuban ta na gode
HUKUNCIN MAƊIGO
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumussalam
warahmatullahi wabarakatuh.
A shari'ar Musulunci, madigo
wanda ake kiran SIHAQ babban zunubi ne kuma laifi ne dake tattare da sauraran
hukunce-hukunce na TA'AZEER (hukuncin da alkali ya yanke domin hana saɓo),
domin babu takamaiman hukuncin Haddi da ya zo a Nassoshi kai tsaye kamar na
zina.
Saduwa tsakanin namiji da
namiji (luwadi) ko saduwa tsakanin mace da mace (madigo) ko ta wani ɓangare
saduwar ta kasance suka aikata ta gaba ne ko baya, shi ne mafi munin zunubi
wanda saboda tsananin munanar sa har ALLAH ya hallaka al'umma akai, al'ummar
Annabi luɗu (AS).
Manzon Allah (Sallallahu
Alaihi Wasallam) Yace'; ALLAH ya la'anci duk wanda ya aikata aiki irin na
mutanen Annabi luɗu (AS) Wato luwadi, har sau
uku Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) yana maimaita wa. Ahmad ya
ruwaito.
Daga jabir Bin Abdillahi
(RTA) Yace'; Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) Yace: Lallai mafi tsoron
abunda nake jiye wa al'umma ta tsoro, aiki irin na mutanen Annabi luɗu
(AS) ! Wato luwadi. [Ibnu majah albani ya inganta].
Manzon Allah (Sallallahu
Alaihi Wasallam) Yace'; Duk wanda kuka tarar yana aikata aiki irin na mutanen
Annabi luɗu (AS), to ku kashe wanda ke aikatawan
da wanda ake aikatawa da shi ɗin.
Manzon Allah (Sallallahu
alaihi Wasallam) Yace "Idan Mace Tazo Ma Mace (Wato Sukayi Madigo) To Su
Biyun Mazinata Ne".
Madigo yana ɗaya
daga cikin manyan laifukan da Ubangiji ya kyamata, sai dai shari’ah bata bada
ainihin wani hukuncin da za’ayi wa masu madigo ba. Sai dai mafi yawan malamai
suna ganin za’ayi masu hukunci dai-dai da na yan luwadi. wato kashe duk wanda
ke aikatawan da wanda ake aikatawa da shi.
Masana ilimin fiqihu sun
tafi a kan cewa malami ko alkali yana da ikon yanke wa mai aikata madigo
hukuncin bulala mai zafi, daurin kurkuku, ko kuma wulaƙantarwa domin ya azabtar da ita ta yadda
za ta hana wani ko ita sake aikatawa.
To ya zama wajibi gareta ta
tuba kuma ta yawaita istigifari tare da nadama bisa abinda ta aikata, kuma ta
nisanci duk wata kawarta ko wata hanyar da za ta mayar da ita ga wannan dabi'a.
Allah mai gafara ne mai jin qai. Yana karɓar
tuban bayinsa aduk sanda suka tuba zuwa gareshi. Mutukar sunyi irin tuban da
yake so.
Ta yawaita ayyukan alkhairi
tare da rokon gafarar Ubangiji mutukar tana raye aduniya. Domin bata da
tabbacin shin Allah ya karɓi tubanta ne ko bai karɓa
ba!!!. Don haka kada ta ɗauki abun kamar Qaramin abu.
Anan nake jan hankalin 'yan
uwa Mata cewa duk matar da tasan acikin Qawayenta akwai mazinata da 'yan madigo
cewa ta nisancesu ta dena Qawance dasu. Domin Allah ya kawomu wani irin zamani
wanda mutane basu ganin girman kowanne irin saɓon
Allah mutukar zasu samu biyan bukata.
Wajabi ne ga duk masu irin
wannan dabi’ar ta madigo da suji tsoron Allah su nisantar da kan su ga barin
yinsa. Su tuna ko wane lokaci za su iya riskar mahaliccin su bayan suna aika
wannan mummunar aikin.
Ya Allah muna tawassali da
sunayen ka kyawawa da ka kiyaye mu da fadawa cikin wannan halin, ka shiryar da
masu yi, ka gafarta mana ka kuma anshi tuban mu. Ameen Ya Hayyu Ya Qayyum 🤲
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.