𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
As-Salaam Alaikum Wa Rahmatul Laah. Mun samu saɓani da mijina, har ya rantse cewa ba zai ƙara nema na ba, sai idan ni ce na neme shi. Ni kuma yau shekaru biyu kenan ban je wurinsa don nemansa ba. To, ko ina da laifi a kan ƙin nemansa da na yi?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus Salaam
Wa Rahmatul Laah Wa Barakaatuh.
Ƙwarai kuwa kina da
laifi a kan wannan matsayin da kika ɗauka, ko dayake a asali ba mace ce aka ɗora wa neman miji don
biyan buƙata ba. A nan kin kayar da haƙƙinsa da Allaah Ta’aala
ya ɗora a kanki ta fuska
biyu:
1. Biya masa buƙatarsa na ’ya
mace haƙƙinsa ne a kanki, wanda kuma shi ne babban maƙasudin ƙulla aure a
tsakaninke da shi. Idan kuwa ba haka ba, to kin yarda kenan cewa: Ya je ya nemi
wata a waje. Wannan kuwa ba ƙaramin laifi ba ne. Shiyasa ma Manzon
Allaah (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:
« إِذَا بَاتَتِ الْمَرْأَةُ هَاجِرَةً
فِرَاشَ زَوْجِهَا لَعَنَتْهَا الْمَلاَئِكَةُ حَتَّى تُصْبِحَ ».
Idan mace ta kwana
alhalin tana mai ƙaurace wa shimfiɗar mijinta, Mala’iku za su yi ta la’antar ta
har zuwa asubah. (Sahih Muslim: 3611).
2. Sannan kuma haƙƙinsa ne a kan ki
cewa: Ki kare shi daga yin kaffaran alwashi ko rantsuwarsa idan ya karya shi, a
matsayinsa mijinki kuma musulmi, kamar yadda Sahabi Al-Baraa’u
Bn Azib (Radiyal Laahu Anhu) ya ce: Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa
Sallam):
أَمَرَنَا بِاتِّبَاعِ الْجَنَائِزِ ، وَعِيَادَةِ الْمَرِيضِ ،
وَإِجَابَةِ الدَّاعِى ، وَنَصْرِ الْمَظْلُومِ ، وَإِبْرَارِ الْقَسَمِ ، وَرَدِّ
السَّلاَمِ ، وَتَشْمِيتِ الْعَاطِسِ .
Ya umurce mu da raka
gawa, da dubo mara lafiya, da amsa gayyata, da taimakon wanda aka zalunta, da
rayar da rantsuwa, da mayar da sallama, da gai da mai atishawa. (Sahih
Al-Bukhaariy: 1239).
3. Amma shi ma
mijinki bai halatta gare shi ya ɗauki irin wannan tsattsauran matakin ba tun
farko. Domin ƙa’idar da addini ya sanya ita ce: Duk lokacin
da miji ya rantse cewa ba zai sadu da matarsa ba, to za a duba a gani: Idan
lokacin da ya sa bai kai watanni huɗu ba, sai a bar shi har zuwa cikan lokacin.
Amma idan kuwa lokacin ya wuce watanni huɗu, to idan watannin huɗun sun cika dole ne a
tsayar da shi: Ko dai ya komo ya cigaba da saduwa da ita, ko kuma ya sake ta.
(Surah Al-Baqarah: 226).
Don haka, wajibinku
ne ku yi taka-tsantsan a kan al’amarin aurenku, ku riƙe shi da muhimmanci,
kuma ku kusanci malamai domin ƙara samun ilimi da gogewa a cikin
dokoki da hukunce-hukuncensa.
Allaah ya ƙara mana fahimta.
Wal Laahu A’lam.
Sheikh Muhammad
Abdullaah Assalafiy
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.