Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Cin Yankan Ahlul-Kitabi Da Auren Matansu

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu Alaikum malam Su waye Ahlul-kitabi? Kuma shin akwai su a wannan Zamani? Kuma ya halatta aci yankansu ko a auri matansu?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikumussalam warahmatullahi wabarakatuhu

Ahlul-Kitabi (Ma'abota Littafi) su ne Yahudawa da Kiristoci. Su ne wadanda Allah Ya saukarwa da littafi (kamar Attaura da Injila) a zamanin da, kodayake addinin na su ya shiga sauye-sauye kafin zuwan Annabi Muhammad (Sallallahu Alaihi Wasallam).

Shin Ahlul-Kitabi akwai su a wannan zamani?Eh, suna nan har yanzu a wannan zamani. Kiristoci da Yahudawa da muke gani a yau su ake nufi da Ahlul-Kitabi. Duk wata aya a cikin Alƙur'ani mai girma da ta yi magana kan Ahlul-Kitabi, tana shafarsu ne a kowane zamani.

Ya halatta a ci yankan da Ahlul-Kitabi suka yanka matukar dai sun yanka shi a kan tsarin da addininsu ya tanada. Haka zalika, ya halatta a ci dukkan abincinsu (kamar kayan lambu da sauransu) matukar ba a tabbatar da cewa sun hada da wani abu da Musulunci ya haramta ba (kamar naman alade ko giya).

Cin yanke-yankensu yana halatta, matukar dai ba a san da cewa an yanka dabbar ne ta hanyar da ba ta dace da Shari'a ba, saboda asalin lamari shi ne halaccin cin sa, kamar dai yankan musulmi, saboda faɗin Allah Maɗaukaki:

اَلۡيَوۡمَ اُحِلَّ لَـكُمُ الطَّيِّبٰتُ ؕ وَطَعَامُ الَّذِيۡنَ اُوۡتُوۡا الۡكِتٰبَ حِلٌّ لَّـکُمۡ وَطَعَامُكُمۡ حِلٌّ لَّهُمۡ وَالۡمُحۡصَنٰتُ مِنَ الۡمُؤۡمِنٰتِ وَالۡمُحۡصَنٰتُ مِنَ الَّذِيۡنَ اُوۡتُوا الۡـكِتٰبَ مِنۡ قَبۡلِكُمۡ اِذَاۤ اٰتَيۡتُمُوۡهُنَّ اُجُوۡرَهُنَّ مُحۡصِنِيۡنَ غَيۡرَ مُسَافِحِيۡنَ وَلَا مُتَّخِذِىۡۤ اَخۡدَانٍؕ وَمَنۡ يَّكۡفُرۡ بِالۡاِيۡمَانِ فَقَدۡ حَبِطَ عَمَلُهٗ وَهُوَ فِى الۡاٰخِرَةِ مِنَ الۡخٰسِرِيۡنَ

A yau an halatta muku abũbuwa mãsu dãɗi kuma abincin waɗanda aka bai wa Littãfi halal ne a gare ku, kuma abincinku halal ne a gare su, da mãtã mãsu kãmun kai daga muminai da mãtã 'yã'ya daga waɗanda aka bai wa Littãfi a gabãninku idan kun je musu da sadãkõkinsu, kuna mãsu yin aure, ba masu yin zina ba, kuma bã mãsu riƙon abõkai ba. Kuma wanda ya kãfirta da ĩmãni to, lalle ne aikinsa yã ɓãci, kuma shĩ, a cikin Lãhira, yanã daga mãsu hasãra. (Surah: Al-Maaida, Ayat: 5)

Haƙiƙa Shari'ar Muslunci ta halattawa Musulmi ya auri Mace Kirista ko Bayahudiya, wannan ita ce Maganar mafi yawa daga cikin Malamai Ma'abota Ilimi, kuma halaccin hakan ya samo Asaline daga cikin Alƙur'āni faɗin Allah() kamar yadda Suratul Ma'idah aya ta 5 ta tabbatar.

An samu wasu daga cikin sahabai, sun aure Ahlul-kitabi kamar Usman ɗan Affan - halifa na uku a musulunci- ya auri Banasariya, haka Dalhatu ɗan Ubaidillah ya auri Banasariya, sannan Shi ma Huzaifa masanin sirrin Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya auri Bayahudiya, Allah ya kara musu yarda. Duba: Ahkamu-ahlizzimah 2\794.

Haka nan wannan Halacci ya taƙaita ne kaɗai akan Maza Musulmai, amma baya halatta ga Mace Musulma ta auri Kirista, ko kuma dukkan wani wanda ba Musulmi ba.

Dan haka Malamai sukace idan Ahlul-kitabi (Kirista ko Bayahudiya) ta kasance ta kame kanta bata aikata zina, to ya halatta a aureta, duk da cewa suma Ahlul-Kitabi kafirai ne Mushrikai da Nassin Alƙur'ani Mai girma, to amma waccan aya ta keɓance su da wannan hukunci, dan haka su kaɗai ne Allah() ya halatta mana muci yankan su da abincin su kuma mu auri Matan su, shi ya sa wannan halacci ya taƙaita ne kaɗai akan Ahlul-kitabi (Yahudu da Nasara), amma sauran Kafirai da suke bautar waɗansu abubuwa dabam-dabam kokuma waɗanda ma basu da wani abin bauta (Majusawa) haramun ne a aure su, saboda faɗin Allah():

وَلَا تَنكِحُوا الْمُشْرِكَاتِ حَتَّىٰ يُؤْمِنَّ وَلَأَمَةٌ مُّؤْمِنَةٌ خَيْرٌ مِّن مُّشْرِكَةٍ وَلَوْ أَعْجَبَتْكُمْ...

Kada ku auri Mata Mushrikai (Kafirai), domin (ku auri) Baiwa Mumina shi yafi alkhairi akan ku auri Mushrika koda kuwa kyawunta ya ƙayatar daku…… (suratul Bakara aya 221)

Danhaka Malamai sukace idan Musulmi ya aminta da cewa wannan Matar Kirista da zai aura ba zata iya rinjayarsa ba yayi Ridda kokuma ta iya rinjayar 'ya'yansa zuwa ga addinin ta to shikenan ya halatta ya aureta, danhaka ana buƙatar Mutum ya kasance yana da Ƙarfin imani dakuma ilimin addini atare dashi, sannan ya kasance niyyarsa ta yin auren ita ce yayi ta ƙoƙarin nuna mata addinin Musulnci har ta gane ta karɓa, to amma duk dahaka Malamai sukace barin auren su ɗin shi ne yafi alkhairi, Musamman ma a irin wannan zamanin da muke cikinsa wanda galibi idan an yi irin wannan auren to Kallabi ne yake jan Rawani a madadin Rawani yaja Kallabi, abin nufi da yawa mazan sukan yi ridda ne, kuma koda Mutum yana da ƙarfin imanin da ba zata iya rinjayar sa ba, to abu ne mai sauƙi awajenta ta iya rinjayar 'ya'yan da suka haifa tare dashi, shi ya sa Malamai sukace barinsa ɗin zaifi sa Mutum yatsira da imaninsa da kuma na 'ya'yansa, danhaka gara Mutum yaje ya nemi 'yar'uwar sa Musulma ya aura.

WALLAHU A'ALAM

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.

  ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam 

Post a Comment

0 Comments