Ticker

6/recent/ticker-posts

Azumin Tasu'a Da Ashura

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum malam barka da wannan lokaci tare da fatan antashi lafiya Amin. Na ce Malam Ina da tambaya don Allah. Malam tambayar game da azumin yau Laraba dana gobe Alhamis wanda ake kira da ashura da tashua. Malam na kwanta bacci da niyyar azumin sai kuma na samu kaina a makare ma'ana namakara gurin sahur yadace na cigaba da azumin ko na ajeshi shi ne tambayar Allah ta'ala ya sa mudace 🙏

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikumussalam warahmatullahi wabarakatuhu

Ya dace ka cigaba da azuminka na Tasu'a da Ashura tunda har ka kwanta da niyyar azumin tun da daddare. Makara wajen cin abincin Sahur ko rashinsa ba ya karya ko ɓata azumi, domin Sahur Sunna ce mai girman lada amma ba sharadi ba ne don ingancin azumi.

An karɓo daga Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) cewa idan musulmi ya yi niyyar azumin nafila (kamar na Tasu'a da Ashura) tun kafin alfijir ya fito, azuminsa ya inganta kuma zai samu cikakken ladan azumin koda kuwa bai tashi cin Sahur ba.

Muharram wata ne mai alfarma, kuma azumi a cikinsa shi ne mafi falala bayan na watan Ramadan.

TASU'A: Ita ce rana ta tara (9) ga watan Muharram.

ASHURA: Ita ce rana ta goma (10) ga watan Muharram, ranar da Allah ya ceci Annabi Musa (A.S) da mutanensa daga hannun Fir'auna.

Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: "Ina kyautata zaton lada a wurin Allah, azumin ranar Ashura yana kankare zunuban shekarar da ta gabata." (Sahih Muslim). Wannan ya shafi kananan zunubai.

Haka kuma Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya kasance yana azumtar ranakun 13, 14 da 15 na kowane wata (Ayyamul-Bidh), kuma ladan kwanaki uku a wata kamar ladan azumin wata gaba ɗaya ne.

An ruwaito a hadisin Sahihul Bukhari, Ibn Abbas ya bayyana cewa Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) bai taɓa kwadayin azumtar wata rana ba saboda falalarta kamar ranar Ashura.

Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce: "Idan na rayu zuwa shekara mai zuwa, zan azumci rana ta tara (Tasu'a)" domin mu bambanta da Yahudawa da ke azumtar rana ta 10 kaɗai.

WALLAHU A'ALAM

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.

   ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam 

Post a Comment

0 Comments