Ticker

6/recent/ticker-posts

Kalmomin Aro a Hausar Malaman Zaure: Nazarin Wasu Yankunan Sakkwato Da Kabi

Citation: Gwandu, B. A. (2025). “Kalmomin Aro a Hausar Malaman Zaure: Nazarin Wasu Yankunan Sakkwato da Kabi ” in Ɗunɗaye Journal of Hausa Studies, Vol. 03, No. 02, Pp. 120 – 127. www.doi.org/10.36349/djhs.2025.v03i02.015.

KALMOMIN ARO A HAUSAR MALAMAN ZAURE: NAZARIN WASU YANKUNAN SAKKWATO DA KABI

Na

Buhari Atiku Gwandu

PhD Candidate, Department of Nigerian Languages, Sokoto State University, Sokoto

Tsakure:

Wannan takarda ta yi nazarin wasu kalmomi da harshen Hausa ya ara daga harshen Larabci, waɗanda Malaman zaure ke amfani da su a yayin karatukansu a zaure ko majalisi a masallaci. Wannan takarda ta fito da waɗansu misalai da aka fi yawan jin Malaman zaure ke yawan furtawa a lokacin karantarwarsu, tare da tasirin karin harshen Yamma. Haka kuma an ɗora wannan takarda kan ra’in hulɗa tsakanin harsuna wanda Greenberg (1962) ya yi amfani da shi. An tattara waɗannan bayanai ta hanyar zama a majalisin karatu zaure da masallaci da sauraren karatukan waɗansu malamai na zaure, da kuma waɗansu ayyukan da aka wallafa masu alaƙa da wannan bincike. Samakon nazarin ya tabbatar da cewa: (i) Ana samun aro na kaitsaye ta fuska uku; (a) aron lafazi da ma’ana sukutum; da (b) aron lafazi ban da ma’ana da kuma (c) aro da faɗaɗa ko karkatar da ma’ana. (ii) takardar ta lura da ana samun tasirin shaddantawa a mafi yawan Hausar Malaman zaure na Sakkwato da Kabi. 

Gabatarwa

Malaman zaure mutane ne waɗanda suke koyar da al’umma addinin Musulunci, musamman karatun Alƙur’ani mai girma da waɗansu ilmuka. Babban dalilin gabatar da wannan takarda, ita ce fitowa da waɗansu kalmomi na aro da malaman zaure ke amfani da su wajen karantarwa irin ta su da hulɗarsu da abokan mu’amala. Wannan ya haifar da yawaitar yin amfani da wasu kalmomin aro na harshen Larabci a zaure. Harshe yana aron kalmomi kai tsaye daga wani harshe zuwa wani ta hanyar fassara da kwaikwayo tare da sarrafa kalmomin. Aro na faruwa ne yayin da hulɗa da cuɗanya ta haɗa harsuna mu’amala da juna. Ta wannan hulɗar da cuɗanya da juna za su samar ma junansu hanyar sadarwa kowace iri. Wannan takarda za ta fito da waɗansu kalmomi da harshen Hausa ya ara ga Larabci da yadda aron ya kasance. Domin Hausa, harshe ne wanda ya kasance ɗaya daga cikin manyan harsuna da yake taka rawa a nahiyoyin duniya, kuma harshe ne da masu magana da shi ƙaruwa da yaɗuwa suke. Harshen Hausa yana cikin jerin gwanon harsuna da duniya ta lisafta na goma shɗaya (11) a duniya, cikin harsuna 70,250, NTI (2020). Girman darajarsa da hulɗarsa ya haifar da aron kalmomi ga harshen Larabci ta sanadiyyar cinikayya da karɓar addinin Muslunci.

Harshe na nufin hanyar magana tsakanin al’umma iri ɗaya (CNHN, 2006). Irin abubuwan da harshe yakan bayyana a sarari don a fahimci mutum, shi ake kira magana ko zance (Yero, 2012). Harshe wata baiwa ce wadda Allah ya halicci mutum da ita, domin ya bayyana tunaninsa zuwa ga sauran ‘yan uwansa mutane ta hanyar furucin waɗansu sautukan magana masu ma’ana da kuma amfani (Yakasai, 2012).

Aron Kalmomi a Harshe

Aron kalma ba gazawa ba ce ko kasawa ba ko kuma cikas ba ne ga harshe da ya ari wata kalma kaitsaye ko ya ɓalli wani ɓangare na ta, ko ya yi ma ta kwaskwarima don ta dace da furucinsa (Umar, 2019). Kalmar ‘aro’ a rarrar kalma ce da aka aro daga harshen Larabci, wato ‘Isti’aara, Yusti’iiru ‘Isti’aaratan’ Almu’ijamu al-Lugah. Hausawa sun yi wa kalmar kwaskwarima ta koma aro, Daurawa (2023). Irin yadda ma’anar ta take a harshen Larabci, su ma Hausawa haka suka ari kalmar sautin da ma’anar sukutum. Aro na nufin karɓar wani abu don a yi amfani da shi a mayar wa mai shi (CNHN, 2006). Aron kalma yana nufin ɗauko wata kalma daga wani harshe zuwa wani harshe (Adamu, 2016).

A wani ƙauli kuma aro na nufin harshen da ya yi aro yana ɗaukar wannan kalma ya cigaba da amfani da ita a mu’amalarsa ta yau da kullum (Abubakar, 2007). Kalmomin aro su ne kalmomi ko sassan jumla da aka ɗauko daga wani harshe domin amfani da su ga wani harshe, (Umar, 2019).

Bayan waɗannan ma’anoni da aka hikaito daga bakunan masana da manazarta daban-daban, an lura da cewa aro a nan, na harshe ake nufi. Aro shi ne amfani da wata kalma ko yankin jumla ta wani harshe domin inganta sadarwa da abinda harsunan biyu suka yi matsaya na manufa ko ma’ana. Tarihi ya nuna dukan harsunan duniya sun samo asali ne daga kaka ɗaya, Annabi Adamu da Hauwa’u (Alaihis salam), saboda faɗar Allah “…lalle ne Mu, Mun halitta ku daga namiji da mace, kuma Muka sanya ku dangogi da ƙabiloli, domin ku san juna ….”, (Gumi: Suratul Hujirat, aya ta 13). Wannan aya ta Alƙur’ani an bayyana alaƙa ta ƙut-da-ƙut da mu’amala da hulɗar harsuna na daɗa tasiri da bunƙasuwa da haɓakar aro a harsuna.

Dalilai da dama sun haifar da aro a harsuna mabam-banta, don masana da manazarta sun yi ishara da tsokaci a kai, saboda harsuna na dogaro da taimakekeniya ga junansu don samar da wadatattun kalmomi da za a iya isar da saƙo babu wata tantama ko tangarɗa. Daga cikin dalilan da masana ke hasashen sun haifar da yin aro sun haɗa da:

·  Alaƙar sautuka ta ƙut-da-ƙut

·  Addini

·  Ɓacewar tsofaffin kalmomi na asali

·  Cuɗanya ko hulɗa

·  Auratayya, (Junju, 1990).

Masana sun nuna wani harshe zai zo ya ari kalma ko sashe domin waƙiltar wani abu da babu a wancan harshen da ake hulɗa ko mu’amala da shi, don haka, amfani da baƙin kalmomi dole ne don cike gurbin waɗanda babu ga harshe, shi ake kira aro ga harshe. Ta haka ne Hausawa suka samu himma wajen koyon kalmomin Larabci da kuma Hausance wasu, saboda tasirin kalmomin Larabci a mu’amalarsu da hulɗarsu da Hausawa (Yakasai, 2012). Harshen Larabci, harshe ne da ya fi kowane harshe matsayi da daraja a duniya, domin shi ne ya game kowa da kowa na duniya, kuma shi ne ake amfani da shi a wurin bautar Allah, wato baƙi ne kai ko farar fata ne kai, matsaya guda ku ke a wurin Allah, subhanahu wa ta’ala. 

Harshen Hausa harshe ne mai tafiya tare da zamani ta fuskar addini da kimiyya da fasaha da kasuwanci da neman ilimi da sauran fannonin rayuwar al’umma. Harshen Hausa ya ari sautukan Larabci baki-ɗayansu ya mayar da su hanyar salon rubutunsa na Ajami. Wasu sautukan aron kaitsaye ne, wasu kuma kwaskwarima ya yi musu don su dace da sautukansa na Hausa da Larabci ba ya da su (Adamu, 2002).

Malamai da masana sun gabatar da ayyuka mabambanta dangane da abin da ya shafi aro tsakanin harshen Larabci da na Hausa kamar su Ramlat (2002) da Salama (2011) da Suleiman (2014) da Adamu (2016) da Muhammad (2024) da makamantansu. Dukansu sun yi bayani kan alaƙa da dangantaka da abubuwan da suka haifar da aro a tsakanin harshen Larabci da Hausa. Kuma kowanensu da abinda ya kalla dangane da aron kalmomin Larabci zuwa harshen Hausa. Ramlat ta nazarci aron kalmomi da ƙirar kalma. Ita ma Salama ta yi nazarinta ne kan kalmomin da harshen Hausa ya ara. Muhammad ma ya kawo rabe-raben aro aƙalla uku da Malaman Zaure kan yi da makamantansu. Aron lafazi da ma’ana kaitsaye da aron lafazi ban da ma’ana da aron lafazi da faɗaɗa ko karkatar da ma’ana

Malaman Zaure a Sakkwato da Kabi

Kalmar ‘Malamai’ jam’i ce ta Maalam ko Mallam a matsayin tilo da Hausawa suka ara daga harshen Larabci. Malam na nufin masanin wani ilimi na addini, ko kuma ilimin zamani a yanzu.

Ita ma kalmar ‘Zaure’ Bahaushiyar kalma ce da ta samo asali daga harshen Hausa wadda ke nufin wani ɗaki da aka shiga a kwanta ko a yi karatu ko wani abu makamancin haka.

Zaure na nufin ɗaki mai ƙofa biyu wanda ake fara shiga ta cikinsa kafin a shiga cikin gida Adamu (2016).

Zaure na nufin ɗakin hayi (CNHN 2006).

Zaure a ƙasar Hausa wani ɗaki ne kewayayye mai kama da da’ira wanda aka gina da laka mai ɗauke da itace a sama kewaye da shi tare da hakin baibaya na bunu. Kazalika duk wani wuri da aka keɓe ana karantar da manya ɗalibai masu neman ilimi a bakin garka ko ɗaki ko shigifa. Amma yankin Sakkwato da Kabi, zaure shi ne wurin shiga da aka yi a bakin garka don saukar da baƙo ko kwanan yara ko kuma karantar da yara da manya masu karatun ilimi (Abubakar 2007).

Hanyoyin da aka yi amfani da su a wajen tattara waɗannan bayanai na wannan takarda sun haɗa da:

1. Ziyartar zaurukan ɗaukar ilimi na malamai. An samu halartar waɗansu zauruka na Malamai a yayin gudanar da karatuka kamar irin su Zauren Malam Babi Gangare Sakkwato da Malam Abubakar Gwandu Digar Agere Sakkwato da Zauren Modibbon Gwandu B/Kebbi da Zauren Malam Walu Adarawar Borno Gwandu da Zaurukan Lungun Malamai Gwandu.

2. Kafafen yaɗa labarai da suka ƙunshi, kafafen yaɗa zumunci kamar su Fesbuk (facebook) da watsaf (WhatsApp) da tit-tof (Tik-tok) da Yutub (You tube) da Istagiram (Instagram) da makamantansu.

3. Wallafe-wallafen ayyukan masana da manazarta da suka shafi aron kalmomin harshen Larabci da harshen Hausa suka yi. 

An zaɓi garuruwan Sakkwato da Kabi ne domin irin alaƙa da dangantaka da ke tsakanin garuruwan tun zamanin masu jihadi. Garuruwan biyu tankar Ɗanjumma ne da Ɗanjummai ne. Saboda Daula ɗaya ce suka raba, Gabasci kulawar Muhammadu Bello Ɗan Sheikh Usmanu Bin Fodiyo, Yamma kuma kulawar Sheikh Abdullahi Bin Fodiyo Gwandu. Haka kuma Malumman waɗannan garuruwan sun yi musayar neman ilimi a tsakaninsu da junansu. Sakkwato ita ce babbar cibiyar Daular Usmaniyya, haka nan kuma ko bayan zuwan Turawa ‘yan mulkin mallaka Sakkwato ita ce uwa ga Kabi, Ambursa (2013). Waɗannan dalilai ne ya sa aka zaɓi Sakkwato da Kabi ga wannan binciken. An lura da karin harshensu iri ɗaya ne, malummansu ɗaya ne, kuma sun fi ba da ƙarfi da kulawa a ɓangaren Fiƙhu da Luggah.

Yadda Malaman Zaure Suke Amfani da Kalmomin Aro a Kabi da Sakkwato

Masana ilimin nazarin harshe da kimiyyarsa, sun bayyana duk harshe yana da hanyar da yake amfani da ita wajen bayyana kalmomin da ya ara ta ba su ma’ana ta sarari da ta ɓoye (Ramlat, 2002). Saboda haka duk maganar da aka furta sai an yi nazarin ma’anarta da kuma inda ta dosa kafin a yanke ma ta hukunci a fannin nazarin ma’ana (semantics). Wannnan ya nuna kalmomin da harshen Hausa ya aro akwai yadda ake amfani da su, ko dai su ɗauki ma’anar kaitsaye ko su faɗaɗa ta, ko ma su yi watsi da ma’anar ta asali su ba da tasu ma’anar ta daban don wata manufa da suka ɓoye ko sakaya ga wasu da ba abokan hulɗa ba. Har ila wa yau, harshen Hausa yana aron kalmar Larabci ya ba ta ma’ana mai dangantaka da ma’anar kaitsaye ko kuma ta karkace ma ma’anar ta asali (Salama, 2011). A wani lokaci ma za a iya samun ma’anonin babu alaƙa ko dangantaka ta kusa ko nesa.

Baya ga la’akari da bayanan da suka gabata a baya, kalmomin da harshen Hausa ya aro kuma yake ci gaba da aro a halin yanzu ana kallonsu da nazarinsu ta fuska uku 3 kamar haka:

Aro na Kai Tsaye Tsakanin Malaman Zaure a Kabi da Sakkwato

Aro na nufin ɗaukar kalma daga wani harshe a shiga da ita cikin jerin kalmomin wani harshen a daban. Aro wata fasaha ce da Ɗan’adam ke amfani da ita ta hanyar ɗauko gudan kalma ko gudajen kalmomi daga wani harshe a shigar a shigar cikin jerin kalmomin wani harshe a daban, Suleiman (2014).

Aro na kai tsaye, wani salon aron kalma ne da harshen Hausa ya yi na tarewar ma’anar harshen Larabci da harshen Hausa ko ta sauti ko kuma Hausance sautin kalmar da ma’anar. Wato ma’anar fili ko sarari daga ma’ana ta asali wadda Larabci yake amfani da ita, kana Malaman Zaure na Kabi da Sakkwato suka Hausantar da kalmomin kamar haka:

a. Aron lafazi (sauti) sukutum da ma’anarsa

b. Aron lafazi (sauti) ban da ma’ana

c. Aron lafazi (sauti) da juyar da ma’anarsa, Muhammad (2024)

Ataƙaice dai an fahimci aro kaitsaye na nufin yin amfani da wata kalma ta wani harshe don sauƙin isar da saƙo a tsakanin harsunan biyu da niyyar faɗaɗawa ko bunƙasawa. Wannan aron kalmomi ne da ke ɗauke da lafazi da sautin kalma (Hausancewa) da ma’ana ta Larabci. Wato ma’anar da harshen Larabci ke nufi, haka su ma Hausawa ke nufi a harshensu. 

 

Kalmar Aro Daga harshen Larabci

Hausantar da Kalmar a Harshen Hausa

Ma’anar Kalmar a Harshen Hausa

1

Yardwáá

Yaddáá

Aminééwââ

2

Khasarah 

Hasaaraa

Taasarii

3

Al-turaab

Turɗaa/Turɓaaya

Ƙasa laƙai-laƙai

4

Al-ramadwaan

Ramalaanaa

 watan azumii

5

Gaafilun

Gahwalallee

Rafkanannee

6

Jidaal

Jidaalii

Faɗaa

7

Daƙiiƙ

Daƙiiƙii

Bin diddigii ko naacii

8

Ƙaimii

Ƙaimii

Linzaamin dookii

9

Ƙiimatun

Kiimaa

Kwatantaa abu

10

Muflis

muhulisii

Wanda aka rabee ma laadaa

11

Dwaririyyu

Laluurii

Ƙurarren lookacii

12

Mu’allim

Mallaam

Masanii

13

Fitnatun

hitinaa

Taashin hankalii

14

Al-aalah

Aalaa

Kayan ɗimaamaa ruuwaa

15

Harakaat

Harkaa

Wasulaa

16

Al-laun

Launii

Launii

 

Kalmar ‘khasaarah’ an aro ta ne daga harshen larabci, kana daga baya Malaman zaure suka Hausantar da kalmar ta koma ‘hasaaraa’, saboda Bahaushe ba ya da harafin ‘kha’ sai dai harafin ‘ha’. Malaman Zaure sun Hausantar da kalmar ta koma ‘Hasaaraa’ saboda tsohuwar kalmar fassararta ta nisanta. 

Ita ma kalmar ‘Ramadwaan’ Balarabiyar kalma ce da aka aro daga harshen Larabci, amma Malaman Zaure suka Hausantar da ita ta koma ‘Ramalaana’, saboda harafin ‘dwa’ ya koma ‘la’ na da wuyar furuci ga Bahaushe. Saboda haka Malaman Zaure suka Hausantar da kalmar ta ‘Ramalaana’ 

Kalmar ‘Jidaal’ ararrar kalma ce da aka aro daga harshen Larabci, amma Malamai suka Hausantar da lafazinta da ma’anarta a harshen Hausa ta koma ‘Jidaalii’. Bambancinsu shi ne harshen Larabci na ɗaure hafin ƙarshe na kalma, saboda aikin nahawu. Malaman Zaure suna yi ma mafi yawan kalmomin aro wasli a ƙarshen kalma.

Ita ma kalmar ‘fitnatun’ aro ta aka yi ga harshen Larabci, kana daga baya Malaman Zaure suka Hausantar da lafazinta da ma’anarta ta koma ‘Hitinaa’. Nan ma an samu musayar harafin ‘f/p’ ya koma ‘h’ a Hauasar Yamma. Saboda harafin kalmar na farko Balaraben harafi ne, ba Bahaushe ba. Shi yassa Malaman Zaure suka sauya harafin na Larabci.

Duk waɗannan kalmomi da aka kawo suna nuna yadda harshen Larabci ya yi tasiri ga harshen Hausa, domin Malaman Zaure sun Hausance mafi yawan waɗansu kalmomin Larabci ta la’akari da tsarin lafazi (sauti) da ma’anar kalma. Sai dai waɗansu kalmomin sun ɗan bambanta da lafazin asali na Larabci da yadda Hausawa suka Hausantar da su. Waɗansu kalmomi sun yi canjaras da lafazin (sauti) da ma’anar sai inda ba a rasa ɗan wani abu ba.

Duk waɗannan kalmomi aro ne na kaitsaye da Hausawa suka ara ba tare da an canza musu salon rubutu da ma’ana ba, saboda tasirin harshen Larabci a wajen karatu a makarantu da mu’amala da zamantakewa tsakanin Hausawa da Larabawa. Saboda daɗewa ana amfani da su har ma sun zama ‘yan gida wato kalmomin din-din-din na harshen Hausa.

Aron Lafazi (sauti) Ban da Ma’ana, Sai Dai Faɗaɗa Ma’ana Tsakanin Malaman Zaure a Kabi da Sakkwato

Faɗaɗa ma’ana na nufin ƙarawa wani abu faɗi (CNHN, 2006). Faɗaɗawa na nufi buɗe wani abu da yake tsuke ko ƙuƙunce a cikin wani mayuwacin hali, ko yalwata wani zance ko magana ko wani wuri ko wani abu na zahiri (Gwandu, 2021). A nazarin ma’ana kamar yadda aka gani a baya, a kan sami yanayin da ma’anar wata magana ko kalma ta faɗaɗa ko yaɗu ko ma ta fanɗare daga ma’anar ta asali. Wannan na faruwa ne ga ma’anar ko dai don tsawon lokacin amfani da kalmar da ya sa ma’anarta ta gurɓata ko ta sauya, wani lokacin ma don ma’anar ta tafi da zamani (Abubakar, 2014).

 

Kalmar Aro Daga Harshen Larabci

Hausantar da Kalmar a Harshen Hausa

Ma’anar Kalmar a Hausa

da Faɗaɗa Ma’ana

1

Farj

Hwarji/ farji

Gaban macee ko namijii

2

Tasbii

Tasbahaa

Abinda akee ƙidan zikirii da shii

3

Ajamiyyun

Ba’ajamee

Boobaawaa

4

Al-imam

Liiman

Jaagooraa

5

Al-suurah

Suuraa

Alaamaa ko hootoo

6

Haajah

Haajaa

Buƙaataa ko kaayan tallaa

7

Al-jariidah

Jariida

Gangaamee ko abin karantawa

8

Al-hisaab

Hisaabi

Lisahi ko bin diddigi, sakamako

9

Al-akhdwariyyu

Ahlarii

Mazauni gida, mahalarci

10

Al-swahaabah

sahabbai

Mabiyan Annabi Muhammad

11

Al-sheikh

Sheehu

Tsoho ko babban maalamii

12

Al-zamanu

Zaamanii

Lookacii ko yanayii ko yanzu

13

Lakaa’i

Lalatattaa

Halakakkiyaa ko karkatacciyaa

14

Abdullah

Audullahi

Bawan-Allah

 

Kalmar ‘Farj’ ta samo asali ne daga harshen Larabci, amma saboda kalmar tana da nauyin faɗi ga al’adar Hausawa. Wannan ne ya sa aka yi amfani da sunaye daban-daban don sakaya kalamar a harshen Hausa. Hausawa na fassara wannan kalmar kamar haka; gindii ko guutsuu ko matuucii ko gatoo ko zakarii ko kuma al’auraa da sauransu. Kana daga baya Malaman Zaure suka sakaya kalmar da sunan ‘gaban namijii ko gaban macee. Malaman Zaure sun yi wannan fassara ce don ɓoye ma’anonin da al’adar Hausa ta zarga.

Kalmar ‘Tasbih’ ararrar kalmace da aka aro daga harshen Larabawa, kuma aikatau ce. Malaman Zaure sun Hausantar da kalmar ta koma ‘Tasbahaa’ daga tasbih ta dawo sunan abinda ake amfani da shi wurin tasbih. Wannan ya nuna hikimar Malaman Zaure sun ƙara samar da faɗaɗuwar ma’ana daga ajin aikatau zuwa ajin suna.

Ita ma kalmar ‘Al-ajamiyyun’ kalma ce da ta samo asali daga harshen Larabci, kuma tana nufin duk wanda ba Balarabe ba. Malaman Zaure sun Hausantar da kalmar ta koma ‘Ba’ajamee’. Wato an samu ɗafa ƙeyar da ya haifar da faɗaɗuwar kalmar, wanda kuma aka kira da sunan ‘Boobaawaa ko Boobooniyaa’. Wato wanda ba ya jin ko iya magana da wani harshe.

Haka kuma kalmar ‘Al-suurah’ an aro ta ne daga harshen Larabci. Ita wannan kalma tana nufin wani dunƙulallen saƙo mai ɗauke da hikimomi tare da kanun labarai a cikinsa. Malaman Zaure sun faɗaɗa ma’anar wannan kalma kamar haka; zatin wani abu ko ƙwangarangwal ko hoto ko makamancin wani abu.

Bisa la’akari da misalan da suka gabata za a fahimci Malaman Zaure na da ƙwarewa da fasaha a wajen aron kalmomin harshen Larabci da yi musu kwaskwarimar Hausantarsuwa. Malaman Zaure sun yi amfani da hulɗa da zamantakewa sun faɗaɗa ma’anar kalmomin harshen Larabci. Haka kuma sun sakaya waɗansu ma’anoni da al’adar ke zargin furtawa duk da kasancewarsu kalmomin asali na harshen Hausa.

Aron Lafazi (sauti) da Karkatar da Ma’ana Tsakanin Malaman Zaure a Kabi da Sakkwato

Malaman zaure na aron kalma daga baya su karkartar da ma’anarta ko faɗaɗa ta la’akari da waɗansu abubuwa da kalmar ta ƙunsa da kuma ma’anar da suka ba ta. Wannan yana faruwa ne ko dai don ɓadda bami ko ɓoyewa ko sakaya ma’anar. Karkatar da ma’anar aro na nufin aron kalma daga wani harshe, sannan a karkatar da manufarta ta asali zuwa wata manufa ta daban da ba ita ba in an fassara ko tarjama (Ramlat, 2002). Akwai wasu kalmomin Larabci da yawa waɗanda ma’anarsu ta bambanta da na harshen Hausa ta sanadiyyar karkatar da ma’anar asali da aka fassara ta da ita. Mu’amalar Hausawa da Larabawa ta yi tasiri ƙwaran gaske wajen baddala ma’anar waɗansu kalmomin Larabci. Harshen Larabci, harshe ne mai faɗi, a kan faɗin ƙunshiyar ma’anarsa ne ma ya haifar da Hausawa na karkatar da ma’anar waɗansu kalmomin Larabcin.

 

Kalmar Aro Daga Harshen Larabci

Hausantar da Kalmar a Harshen Hausa

Karkatar da Ma’anar Kalmar a Harshen Larabci da Faɗaɗa Ma’ana

1

Al-daƙiiƙ

Daƙiiƙii

Takkwalii ko kidaahumii

2

Zuuƙu

Zuƙuu

Kwaraaree ko zarceewaa

3

Al-guluul

guluuluu

Suruutuu

4

Li’iilafi-ƙuraish

Li’iilahi-ƙuraishi

Annaniyar koowaa ta bii shi

5

Inkaar

Ankara

Luura ko guduu/sheeƙaa

6

Haajah

Haajaa

Kaayan sayarwaa

7

Al-muhaajir

Almaajirii

Mabaraacii

8

Al-zakaat

Zakkaa

Korarree cikin dangii

9

Albarakaat

Albarka

Ba a barii haka nan baa

10

Sayaws

sayas

Addu’ar sayar da abin sayarwa a kasuwa

11

Al-salaamu

An sallama

An bar abin sayarwar nan haka nan

12

Al-adah

La’adaa

Abinda mai sayee da sayarwaa kee baa wanda yaa shiga tsakaanii

12

Al-magrib

Magariibaa

Ƙasaashen yammaa

13

Al-haal

Alhaalii

Sabooda ko doomin ko don

14

Al-geb

Gaaɓaa/gaɓaa

Geebee ko Koogii

 

Kalmar ‘Al-daƙiiƙ’ aro ta aka yi a harshen Larabci, Sannan daga baya aka Hausance Kalmar sai ta koma ‘Daƙiiƙii’. Larabawa sun fassara ma’anar wannan kalma da naci ko ƙwalailaicewa. Amma Malaman Zaure sun faɗaɗa ma’anar ko karkatar da ma’anarta da fassarar takkwali ko kidahumi, wato wanda bai gane komai a karatu ko a rayuwa.

Kalmar ‘Zuuƙuu’ ma ararriya ce daga harshen Larabci, kuma aikatau ce. Larabawa na fassara wannan kalmar da ‘ɗanɗana’ ko ‘lasa’ ko ‘ka ji da kanka’. Malaman zaure sun ƙara ma wannan kalma gudu da faɗaɗa ko karkatar da ma’anarta, don sun fassara ta da ‘Kwarare’ ko ‘Zarcewa’ ko ‘Zurare’ ko kuma ‘Wuce gona da iri’ da makamantansu.

Kalmar ‘Al-magrib’ ta samo asalinta ne daga harshen Larabci, kuma tana nufin Sallar Magariba, wato bayan faɗuwar rana. Amma su Malaman Zaure na fassara wannan kalmar da ma’anar ‘Ƙasashen Yamma’ ko ‘ wani salon rubutu da aka gada ga Malamai’. Wannan ya nuna Malaman Zaure na ƙara faɗaɗa ma’anar kalmomin Larabci don sadarwar yau da kullum.

Ita ma kalmar ‘Al-guluul’ Balarabiyar kalma ce da aka aro ga harshen Larabawa mai ɗauke da ma’anar ‘Ɗaukar wani abu cikin kayan rabo, kamin a raba’. Wato wannan abin da aka ɗauka na kayan, shi ake kira ‘guluul’. Malaman Zaure sun ari sauti da lafazin kalmar suka faɗaɗa da karkatar da ma’anarta kamar haka; ‘Surutu’ ko ‘Magangannun da ba su da amfani’ ko kuma ‘yasassun zanzantuka’ da makamantansu.

Kammalawa

Bayanai sun gabata masu matuƙar muhimmanci dangane da abinda ya shafi aron kalmomi a Hausar malaman zaure a wasu ɓangarorin rayuwar al’umma. Takardar ta bayar da haske kan yadda furucin waɗansu kalmomi ke bambanta da juna, sanadiyyar tasirin harshen Larabci wajen koyon addinin Muslunci. Haka zalika kuma, takardar ta yi nuni da yadda Hausawa masu alaƙa da karatun zaure ke aron kalmomi kaitsaye da faɗaɗa ma’ana da karkatar da ma’ana.

Manazarta

Abubakar N. (2007). Nazarin Hausar Malaman Zaure a Garin Sakkwato Kundin Digiri na Ɗaya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.

Abubakar N. (2014). Malaman Zaure da Gudummuwarsu a Harshen Hausa. Taron Ƙara wa Juna Sani na Ƙasa da Ƙasa, Jami’ar Bayero, Kano

CNHN, (2006). Ƙamusun Hausa na Jami’ar Bayero Kano. Ahmadu Bello University Press Ltd. 

Galadanci M.K.M, (1992). Hausa Don Ƙananan Makarantun Sakandare 2. Longman Nigeria.

Greenberg J.R. (1962). Languages of Africa. Bloomington.

Gwandu A.B. (2021) Kalmomin Fannu na Magungunan Kyamis a Kasuwar Dodoru. Kundin Digiri na Uku. Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sokoto.

Junju H.M. (1990). Garkuwar Hausa da Tafarkin Ci gaba. Fisbas Media Services Publications.

N.T.I, (2020). Course Book on Primary Education, Second Semester Year 4. N.T.I Press

Ramlat J.D. (2002). Morphological and Phonological Adaptation of Arabic Loan Words to Hausa. Algaita: Journal of Current Research in Hausa, Bayero University, (2)1.

Salama S.I. (2011). Kalmomin Aro: Nazari a Kan Wasu Kalmomi da Hausa ta Ara Daga Larabci. Takardar da Aka Gabatar a Taron Ƙarawa Juna Sani. Sashen Harsunan Nijeriya. Katsina : Jami’ar Umaru Musa Yar’adua.

Umar, M.M. (2019) Nazarin Hausar Wasu Rukunnan ‘Yan Kasuwa a Garin Sakkwato. Kundin Digiri na Uku. Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo Sakkwato.

Yakasai, A.S. (2012). Jagoran Ilimin Walwalar Harshe. Garkuwa Media Services Ltd.

Zainab Y. (2012) Nazarin Hausar Yaron Mota a Garin Zaria. Kundin Digiri na Biyu Jami’ar Ahmadu Bello Zaria.

 Ambursa U. R, (2013). Tarihin Shehu da Abdullahi, Ambursa Printing Press Ltd.

Muhammad A. A (2024). Muhadara: Yadda Aka Zakkah da Waƙafi, Taron Ƙarawa Juna Sani. Ma’aikatar Lamurran Addinin Muslunci ta Jihar Katsiona.

Adamu M. (2016). Kalma Ɗaya Ma’ana Bamban: Nazari Kan Wasu Kalmomin Aro Daga Larabci Zuwa Hausa. Takardar da Aka Gabatar a Taron Ƙarawa Juna Sani a Jami’ar Jihar Kaduna. 

Daurawa, A. I. (2023). Tafsir Suratul Fatiha, Gombe State, a Ranar 07 ga Watan Ramadwaana, Shekara ta 1444, Shekarar 2023.

 Dundaye Journal

Post a Comment

0 Comments