𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum, malam dapatan kuna lafiya ya iyali, dan Allah malam addu'a nake so a taimaka man da ita ta haɗin kan iyali saboda duba da yana yin da muke ciki a yanzu kana zaune lafiya da mai-gidanka da yaranka a lokacin da zai kara aure wata ta yi abin da zai rabaka da mijinka da yaranka baki ɗaya Dan Allah a taimaka Kuma wasu mazajen sukan rinka kule-kulen ‘yanmata musamman a social media har takai ana yin abin da bai dace bah Kuma ba aurensu zai yi bah Saboda lokacin iyalinsa a taimaka mana da addu'a da shawarwari, Na gode.,Allah ya ƙara ƙaunar SAYYADINA RASULULLAHI SALALLAHU ALAIHI WASALLAM.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikis salam wa
rahmatullahi wa barakatuhu.
Tabbas da yawa daga cikin
mazaje basu fahimci irin Ƙunar
zuciyar da matayensu ke fuskanta ba ne a lokacin da suka Ƙi basu lokacinsu, kuma ba wai saboda sun
yi musu wani laifi ba, kuma ba don saboda wani muhimmin aikin da ya ɗauke
hankalinsu ba, sai don saboda yin chatting da 'Yan mata a facebook ko whatsapp.
Allah Maɗaukakin
Sarki ya umurci mazaje cewa wajibi ne su rike matayensu bisa amana kuma su
kyautata mu'amalarsu dasu. Hakanan kuma ya faɗa a
cikin Suratul Baƙarah
cewa "SU MA (MATAYEN AURE) SUNA DA HAKKI (AKAN MAZAJENSU) KWATANKWACIN
IRIN HAƘƘIN da ke KANSU NA
MAZAJENSU".
Wato kamar yadda ya zama
wajibi akan mace ta girmama mijinta kuma ta kyautata masa, ta bashi dukkan
lokacinta, to shi ma wajibi ne ya girmamata amatsayin ta na mutum, ya girmamata
amatsayin ta na musulma muminah, sannan ya girmamata amatsayin ta na amanar
Allah da ke karkashin kulawarsa, kuma ya ba ta dukkan lokacinsa aduk lokacin da
yake gida, sannan ya rika kiyaye abin da zai kawo zargi da zubewar mutunci
tsakaninsa da iyalinsa.
Shawarar da zan baki awannan
yana yin shi ne ki yi iyakar bakin kokarinki wajen ɗaukar
hankalinsa ta hanyar tsafta da Ƙayatar
da Girkinki, jikinki da dakinki da shimfidarki, da gidan ma baki ɗaya.
Sannan ki lalubo duk wani
laifin da kika san baya so, ki gyara, ki kyautata duk wata mu'amala tsakaninki da
shi, sannan kema ki rika tura masa kalaman soyayya ta hanyar text ko da yana
wajen aiki ko kasuwarsa.
Idan ya dawo gida kuma ki
tarairayi abinki, ki nuna masa tamkar baki da wani uzuri aduniyar nan bayan
ibadunki na farilla sai kula da mijinki. Mafiya yawan matan hausa/fulani kamar
wani irin girman kai ke damunsu. Suna ganin tamkar sunfi karfin su bawa namiji haƙuri idan sun yi masa laifi, kuma suna
jin nauyin su rika tarairayarsa.
Ba wani abu ba ne yake ɗauke
hankalin wasu mazajen auren daga kan matayensu, har su koma yin chatting da
'yan mata fache rashin samun tausasan kalamai daga matansu na aure, da rashin
jituwa, da rashin saurin warware matsalolin gida ta hanyar laluma da sulhu.
Daga ƙarshe kuma ina baki shawarar ki Ƙara haƙuri
da juriya da kuma mayar da hankali wajen kyautata zance da mu'amala da
maigidanki, sannan ki yawaita kula da karatun Alƙur'ani
da nafilfilin dare, da zikirin Allah ako yaushe.
WALLAHU A'ALAM.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
Tambaya:
Assalamu alaikum malam. Ina roƙon shawara da addu’a saboda wani lokaci mijina yana kallon wasu mata
musamman a social media, wanda hakan yana damuna sosai. Ina neman hanyar haɗin kan iyali da tabbatar da
zaman lafiya da mijina da yarana.
Amsa:
Wa alaikumus salam wa rahmatullahi wa barakatuhu.
Tabbas, irin wannan matsala tana damun matayen aure sosai,
musamman idan mijin yana kula da wasu mata a social media ko wasu wurare. A
Musulunci, akwai hakki da wajibi tsakanin miji da mata a aure:
Hakkin Miji Akan Matar Aure:
Allah Ya umurci mazaje su rike matayensu bisa amana kuma su
kyautata mu’amala da su.
وَعَاشِرُوهُنَّ
بِالْمَعْرُوفِ
(Surah An-Nisa: 19)
“Ku zauna da matanku cikin kyakkyawar
mu’amala.”
Hakkin Matar Aure Akan Miji:
Mata ma suna da hakki kan mazajensu. Suratul Baqarah ta
bayyana cewa:
لَهُنَّ
مِثْلُ الَّذِي عَلَيْهِنَّ بِالْمَعْرُوفِ
(Surah Al-Baqarah: 228)
“Mata suna da hakki irin wanda ke kansu,
cikin kyakkyawar mu’amala.”
Wannan yana nufin cewa, kamar yadda mace ke mutunta miji, ta
kula masa da lokaci, ya zama wajibi ga miji ya girmama matar aure, ya ba ta
lokaci, kulawa da tausayi, da gujewa abubuwan da zasu kawo shakku da rashin
jituwa.
Shawarwari na Aiki
Kyautata Zance da Mu’amala:
Ki yi iyakar kokarinki wajen jan hankalinsa ta tsafta, kyau
da girkinki, da dakinki da gidan baki ɗaya.
Ki gyara duk wani hali ko laifi da kika san yana damun shi.
Tura Kalaman Soyayya:
Ki tura masa kalamai na soyayya ta text ko saƙo,
koda yana wajen aiki ko kasuwanci, domin ya ji ƙaunar ki.
Tarairayi Mijin:
Idan ya dawo gida, ki tarairayi shi, ki nuna masa farin ciki
da kasancewar sa, kamar dai babu wani uzuri na duniyar nan bayan ibadunki.
Haƙuri da Juriya:
Haƙuri shine mabuɗin
warware matsalolin gida. Yin haƙuri da juriya da kyakkyawar mu’amala zai sa mijinki ya
koma zuwa gare ki.
Ibada da Karatun Qur’ani:
Ki yi ƙoƙari wajen karatun Qur’ani,
nafilfilin dare, da zikirin Allah a ko da yaushe. Wannan yana kare zuciya daga
sharrin shaiɗan da
tunani mara kyau.
Guji Girman Kai:
Wasu mata suna jin tamkar sun fi karfin haƙuri
wajen gyara mu’amala,
wanda hakan yana sa mijin ya nemi wani abu a waje. Kyautata haƙuri da
girman kai yana taimakawa wajen jituwa da aure.
Kammalawa
Yin waɗannan
abubuwa in shaa Allah zai ƙara haɗin
kai da zaman lafiya a cikin gidan aure.
Haka zalika, addu’a tana da muhimmanci sosai: ki nemi Allah
Ya tsare mijinki daga duk wani abin da zai kawo rarrabuwar kai da iyali.
WALLAHU A’LAM.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.