𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
A Shari'ance Mene ne hukuncin Sakon Gaisuwar Juma'a, da ake yi wa Mutane ta Text ko Social Media??
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Ko
shakka babu cewa Ranar-Jūma'a rana
ce ta īdi a wajen Musulmai, kamar
yadda ya zo a Hadīsi
cewa Mαnzon Aʟʟaн (Sallallahu
Alaihi Wasallam) Yace:
إن هذا يوم عيد جعله الله للمسلمين، فمن جاء إلي المسجد فليغتسل..........
(رواه إبن ماجه/1098)
MA'ANA: Lallai
wannan rana ce (Jūma'a)
da Aʟʟaн (ﷻ) ya
sanyata amatsayin īdi ga Musulmai, danhaka idan Mutum zaije Masallaci to ya yi wanka.
Danhaka
kenan Musulmai sunada ranekun īdi ne
guda uku kawai a Muslunci:
①-Īdin-Ranar-Jūma'a:
②-Īdin-Babbar-Sallah:
③-Īdin-ƙaramar-Sallah:
Sai
dai Īdin-Babbar-Sallah da Īdin-ƙaramar-Sallah
sukan maimaitune aduk Shēkara,
amma Īdin-Ranar-Jūma'a yakan
maimaitune duk Sati-Sati,
Amma
dangane da abin da yashafi hukuncin Sakonu-Gaisuwar-Jūma'a, da
Mutane sukeyi a tsakaninsu,
kamar irin su: Jūma'at-Karīm, Jūma'at-Mufīdat, Jūma'at-Mubarak, Jūma'at-Ɗayyibat, Dadai
sauran makamansu, sai ariƙa
aikawa 'Yan'uwa da abokan arziƙi ta hanyar Text-Message, ko
kuma ta Social
Network, Abin
da yake a Shari'ance
kamar yadda Malamai
suka faɗa shi
ne, Asali Muslunci ya yardane kawai da Gaisuwar
Ranekun Īdin-ƙaramar-Sallah da Babbar-Sallah, sūma a bisa ga wasu lafuzza da Shari'a ta
yarda a yi amfani
dasu, amma gameda Gaisuwar-Jūma'a, babu inda Shari'a ta
yi bayanin cewa ayi, danhaka da
yawa daga cikin Malamai suka
ce yin Gaisuwar-Jūma'a Bid'ace,
musamman idan ya kasance masu
yin hakan suna ƙudurta
cewa akwai wani lada da za a samu
ga duk wanda yayi, to ko Shakka babu
cewa ya zama Bid'a,
domin ba a samu hukuncin yin hakan a cikin wani Nassi ko
aikin magabata ba.
Sai
dai akwai Malaman da
suke ganin cewa idan Mutum ya yi Gaisuwar-Jūma'a, tare
da cewa yasan
bata da asali a cikin addīni sannan kuma bai ƙudurta cewa yin hakan Sunna ba ne, ko
kuma idan Mutum yayi
zai samu wani lada akaiba, kawai suna yine
amatsayin al'ada
bawai da sunan addīniba,
suka ce to babu
wani laifi akansu dan sun yi, sai dai duk da haka suka ce barin yinsa ɗin
shīne ya fi zama alkhairi, saboda gudu kada Jahilai su rūɗu da
cewa hakan adiīnine,
wanda kuma galibin
masu aika Sakon-Gaisuwar-Jūma'a,
awannan zamanin
zaka samu cewa suna yīne danufin samun lada bawai suna yine amatsayin
al'adaba, Aʟʟaн (ﷻ) dai
Ya ganar damu gaskiya kuma yabamu īkon binta Amīn-Ya-Rabbi.
Doмυп пεмαп ƙαяıп вαчαпı sαı αdυвα шαɗαппαп
ʟıтαттαғαı καмαя нακα: ↓↓↓
"زاد المعاد"
(1/380)
"الفتاوي الكبري"
(2/228)
шαʟʟαнυ-тα'αʟα
α'α'αʟαмυ
AMSAWA
Mυѕтαρнα Uѕмαn
08032531505
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
Tambaya:
A shari’ance, mene ne hukuncin sakon gaisuwar Juma’a da ake
yi wa mutane ta Text ko Social Media?
Amsa:
Ranar Juma’a rana ce mai daraja sosai a Musulunci, kamar
yadda Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce:
النصّ بالعربي:
"إن هذا يوم عيد جعله الله للمسلمين، فمن جاء
إلى المسجد فليغتسل..." (رواه ابن ماجه 1098)
Hausa:
“Lallai wannan rana ce ta īdi da Allah
ya sanya wa Musulmai, wanda ya zo masallaci to ya yi wanka...”
Musulmai sun san ranakun īdi guda uku ne kawai:
Īdin Babbar-Sallah
Īdin Ƙaramar-Sallah
Īdin Ranar Juma’a
Īdin Babbar-Sallah da Ƙaramar-Sallah sukan maimaitu
shekara-shekara.
Īdin Ranar Juma’a yakan maimaitu duk sati-sati.
Hukuncin Sakon Gaisuwar Juma’a:
Sakon kamar “Juma’a Mubarak”, “Juma’a Kareem”, ko
makamancinsu, ba shi da asali daga Al-Qur’ani ko Sunnah.
Masana sun ce yin hakan Bid’a ne idan mutum ya ƙudurta
cewa yin sa yana da lada musamman.
Duk da haka, wasu masana sun ce idan mutum ya yi sakon yana ɗaukar shi kawai a matsayin
al’ada, ba tare da ƙudurin samun lada ko nuna ibada ba, babu laifi a kansa.
Amma mafi kyau shi ne kar a zamar da wannan sako al’ada ta
addini, domin mutane kada su ɗauka
cewa ibada ce ko sunnah ce.
Kammalawa:
Sakon Juma’a ba daga sunnah ba ne.
Yin sa da nufin lada ko ibada yana zama Bid’a.
Yin sa kawai a matsayin gaisuwa da al’ada ba laifi, amma
mafi alkhairi shi ne a bar shi.
A mayar da hankali kan karatun Qur’ani, sallar nafila, da
zikiri a ranar Juma’a, wanda yake da asali a addini.
Mabooki:
“زاد المعاد”
(1/380)
“الفتاوي الكبري”
(2/228)
Allah Ya bamu ikon aikata abin da Ya yarda, Amin.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.