DALIBI:
Malam Allah ya kai mu
aljannah wlh malam ina son aljannah
Malam wato aljannah waii ka san mene ne sirin cikin gidan aljannah hmm saboda akwaii manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam
SHIN MUSULMAI ZA SU GA ALLAAH
IDAN AN SHIGA ALJANNAH
USMANNOOR ASSALAFY
Dan uwa - ina kyautata zaton
ba ka karanta littafin: "Hadil Arwah ila biladil Afrah" ba wallafar
Imam Ibn al - Ƙayyum al - Jauziyya
da kuma littafin: "Paradise and Hell Fire" wallafar Imam al - Ƙurtubi da kuma littafin: "Albidaya
wan Nihaya" na Ibn Khathir (Allaah ya jikansu da rahama baki daya)
Da a ce ka karanta su kuma
ka fahimce su to da tabbas za ka gasgata cewar da akwai sirrin da ya fi ganin
Annabi (Sallallahu alaihi wasallam)
Wato ganin wanda ya halicci
Manzon Allaah (Sallallahu alaihi wasallam)
Wato Allaah Azzawajallah
Hujja:
(وُجُوهٌ يَوْمَئِذٍ نَّاضِرَةٌ )
القيامة (22)
Al-Ƙiyaama
Wasu huskõki, a rãnar nan,
mãsu annuri ne.
(إِلَىٰ رَبِّهَا نَاظِرَةٌ )
القيامة (23)
Al-Ƙiyaama
Zuwa ga Ubangijinsu mãsu
kallo ne.
Da kuma
(لِّلَّذِينَ أَحْسَنُوا الْحُسْنَىٰ وَزِيَادَةٌ ۖ وَلَا يَرْهَقُ وُجُوهَهُمْ قَتَرٌ وَلَا ذِلَّةٌ ۚ أُولَٰئِكَ أَصْحَابُ الْجَنَّةِ ۖ هُمْ فِيهَا خَالِدُونَ )
يونس (26)
Yunus
Waɗanda
suka kyautata yi, sunã da abu mai kyãwo kuma da ƙari,
wata ƙũra bã ta rufe fuskõkinsu, kuma haka wani ƙasƙanci.
waɗancan
ne abokan Aljanna, sunã madawwama a cikinta.
Wannan ayar ni da kaina na
ga mu'ujizarta, shekaru 3 baya lokacin da muna zaune da abokaina da damina an
hado hadari, ina karanta daidai inda Allaah ya ce: "Wata kura ba ta rufe
fuskokonsi a Aljannah"
Sai kawai kura ta rufe mana
fuskokinmu, sai kowa ya fara rufe fuskarsa, masu furzar da kasa na yi - mai
Subhanallah na yi, anan take na nunawa abokaina cewar a daidai lokacin da nake
karanta wannan ayar kuma a daidai kokacin da kurar duniya ta rufe mana
fuskokinmu. Kowa ya cika da mamaki, muna firta Allaahu Akbar.
Ibn al - Ƙayyum ya ce: "Babbar ni'imar da za
a bawa yan Aljannah ita ce ganin fuskar Allaah"
Shi kansa Annabi (Sallallahu
alaihi wasallam) ba abin da ya fi so sama da Allaah ya lullube shi da rahamarSa
ya saka shi a Aljannah, wannan ne ma yasa yake yawaita karanta adduar son ganin
fuskar Allaah Azzawajallah:
اللَّهُمَّ إنِّي أسألكَ لذَّةَ النَّظرِ إلى وجْهِكَ والشَّوقَ إلى لقائِكَ في غيرِ ضرَّاءَ مُضِرَّةٍ، ولا فتنةٍ مُضِلَّةٍ، اللَّهُمَّ زيِّنَّا بزينةِ الإيمانِ، واجعلنا هداةً مهتدينَ
— (An rawaito shi daga
Nasa’i da Ahmad, Albani ya inganta shi).
“Ya Allah! Ina roƙonka ni’iman kallon FuskarKa, da ƙaunar saduwa da Kai, ba tare da wata
cutarwa ba, kuma ba tare da wata fitina ta bata ba. Ya Allah! Ka ƙawata mu da kayan ado na imani, ka sanya
mu shuwagabanni masu shiryarwa.”
Duk da waɗannan
ayoyin da sahihan hadisan amman fa akwai wadansu mutanen da ba su yarda cewar
za a ga Allaah ba. Majority dinsu yan Ƙur'aniyyun
ne.
Last week, da na halarci
Daurah Ilimiyya a Bayero Umiversity Kano musamman na yiwa Shaikh Dr. Magaji
Fadlu Zarewa (Hafizahullah) tambaya akan makomar irin waɗannan
mutanen idan suka mutu ba su yarda za a ga Allaah ba a Aljannah, har na kawo
misalin wani dan Ƙuraniyyun
a anguwanmu da mukaita tafka muƙabala
da shi akan hakan
Ya ce idan misunderstanding
din hujjoji daga ayoyi da hadisai sukai to ana musu uzuri amman indai take
sanin sukai to anan suna karyata ayar Allaah ne wanda hakan kafirci ne
Muna rokon kamar yanda muka
hadu a wannan zaure na gyaran suratul fatiha, Allaah ya sa mu ga mahiliccinmu a
Aljannah baki daya😅🤲
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.