TAMBAYA:❓
Mece ce Kaffarar Rantsuwa kuma yaya ake yin ta?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Kaffarar rantsuwa Allah ya
bayyana ta a cikin fadinsa:
لا يُؤَاخِذُكُمُ اللَّهُ بِاللَّغْوِ فِي أَيْمَانِكُمْ وَلَكِنْ يُؤَاخِذُكُمْ بِمَا عَقَّدْتُمُ الأَيْمَانَ فَكَفَّارَتُهُ إِطْعَامُ عَشَرَةِ مَسَاكِينَ مِنْ أَوْسَطِ مَا تُطْعِمُونَ أَهْلِيكُمْ أَوْ كِسْوَتُهُمْ أَوْ تَحْرِيرُ رَقَبَةٍ فَمَنْ لَمْ يَجِدْ فَصِيَامُ ثَلاثَةِ أَيَّامٍ ذَلِكَ كَفَّارَةُ أَيْمَانِكُمْ إِذَا حَلَفْتُمْ وَاحْفَظُوا أَيْمَانَكُمْ كَذَلِكَ يُبَيِّنُ اللَّهُ لَكُمْ آيَاتِهِ لَعَلَّكُمْ تَشْكُرُونَ
Allah bazai kamaku da laifin
rantsuwa da kuke yi a cikin Zancenku Na wasa, Zai kamaku da laifin rantsuwar da
kuka ƙullah ne kaɗai,
to irin wannan rantsuwar kaffararta shi ne: "Ciyar da Miskinai Abunci
tsaka tsakiya wanda kuke ciyar da iyalanku, ko tufatar dasu, Ko 'yanta
Baiwa," Wanda bai Samu ba kaffararsa shi ne Azumin kwana uku wannan shi ne
kaffarar rantsuwarku idan kuka rantse ba ku cikaba, Ku kiyaye rantsuwarku kada
kudinga yin rantsuwa barkatai, Haka Allah yake bayyana Muku ayoyinsa danku zama
Masu godiya.
Mutum Yana da Zaɓi
tsakanin Abubuwa Guda Uku:
1. Ciyarda miskinai goma,
Tsaka tsakiyar Abin da mutum yake ciyarda iyalinsa, Kowanne miskini Abashi
rabin sa'i na mafi rinjayen irin Abuncin da Mutanen garin suka fi ci, kamar
shinkafa da sauransu, Idan kahada miskinai goma kaciyar dasu kashayar dasu ya
wadatar.
2. Tufatar da Miskinai goma,
kowanne miskini zakai masa tufar da zai iya sallah da ita (wadatacciyar tufa)
namiji zakai Masa riga da wando, mace zakai mata Riga doguwa da kuma Hijabi.
3. 'Yanta Baiwa Mumina.
Wanda bai Samu wani Abu daka
cikinsu ba, sai ya yi Azumin kwana uku Ajere..
Jamhurdin Malamai suntafi
akan Bai halatta fitar da Kaffarar rantsuwa da kudi ba.
Ibun Ƙudama Allah yajikansa ya ce: Fitar da ƙimar Abunci ko tufafi da kuɗi
baya isarwa ga mai kaffara, domin Allah abunci ya Ambata, kaffara ba ta samuwa
sai idan da Abunci aka yita, saboda kuma Allah yabada Zaɓi
tsakanin Abubuwa uku, daya halatta bayar da ƙimar
ciyarwa ko tufatarwa dabai bayar da zaɓi
cikin Abubuwa ukun nan ba. Al-Mugny (11/256)
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance damu cikin wannan group domin Fadakarwa...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.