TAMBAYA (38)❓
Salãmun alaikum warahmatullah, Uncle barka da yamma, Dan Allah uncle meye hukuncin alwalar Wanda arashin sani konace bada wata manufaba wani bangare najikinshi yataba wani bangare na jikin mace. Misali idan Dr ya zo yiwa yaro allura Sai manar yaron tariƙe yaron to Sai ko hannunta kowani bangare najikinta yataba jikin Dr, ko hannunsa kafin yadauke daga inda yama yaron allura itakuma takawo hanu donta massaging din wajen,
Komisalin yataba jikin
yarinya ƙarama ya ji yana yin temperature jikin
ta, Amma ranshi lafiya ƙalau
Babu wata manufa Kota misƙala
zarratin
HUKUNCIN LIKITAN DA YAKE TAƁA
JIKIN MACE MARA LAFIYA
AMSA:
Haramun ne mutum namiji ya
taba wadda ba muharramarsa ba
An rawaito daga Ma'ƙil ibn Yassar RA ya ce: Annabi SAW ya ce:
"A samu ƙusar ƙarfe a bugawa mutum a kansa shi ne ya fi
masa sauƙi akan ya taba macen da bata halatta a
gareshi ba"
Dabarani ne ya rawaitoshi a
cikin al-Kabeer, 486. Shaykh Albani ya ingantashi a cikin Saheeh al-Jaami' 5045
An karbo daga Urwah, Nana
Aisha RA ta ce masa: Lokacinda matan Muhajirun sukai hijira zuwa Madina sun
kasance suna Mubaya'a ne ba da musaffah ba (Gaisuwar hannu da hannu), ta ce:
Annabi SAW bai taba shafa hannun wata mace da hannunsa ba. Saidai yana bayanine
akan ga abin da Mubaya'a take nufi idan mace ta amince sai ya ce: Je ki an
amshi Mubaya'ar ki"
Sahih Muslim (1866)
Haka kuma an karbo hadisi
daga Umaymah RA yar Raƙeeƙah RA ta ce: Annabi SAW ya ce:
"Bana gaisawa (musafaha) da mata"
al-Nasaa'i (4181) da ibn
Majaah (2874). Shaikh Albani ya ingantashi a cikin Saheeh al-Jaami' (2513)
Hadisin da al-Tabaraani ya
rawaito a cikin al-Kabeer da kuma al-Awsat da aka rawaito cewar Annabi SAW yana
gaisawa da mata da karkashin hannun riga, wannan hadisi da'ef ne (Al-Haytham ya
ce bai ingantaba saboda a cikin isnadin hadisin da akwai 'Ataab ibn Harb
shikuma a ilimin hadisi da'eef ne)
Majma' al-Zawaa'id, 6/39
Shaykh Ibn Baaz (Rahimahullah)
ya ce: fadin Annabi SAW: "Bana gaisawa (musafaha) da mata" kadai
hujjace dake kawarda duk wani hadisi wanda zai kawo shubha
(Hashiyat Majmoo'at Rasaa'il
fi'l-Hijaab wa'l-Sufoor, p. 69)
Al-Zayla'i ya ce: Gameda
riwayar da akace Sayyadina Abu Bakr RA yana gaisawa da tsofaffin mata, wannan
ghareeb hadis ne"
(Nasab al-Raayah, 4/240)
Ibn Hajar ya ce: "Ban
ga wannan hadisin ba"
(al-Diraayah fi Takhreej
Ahaadeeth al-Hidaayah, 2/225)
Gaba daya mazhabobin
Hanafiyya, Malikiyya da Hanbaliyya duk sun tafi akan hukuncin taba mace ko yin
musafaha da ita haramunne
Mazhabain Shafi'iyya kuma
Imam an-Nawawi ya ce: "Haramunne taba mace ta kowacce siga". Shi kuma
Wali al-Deen al-'Iraaƙi ya
kara da cewar saidai idan ya zamana idan har Annabi SAW wanda yake gudun fadawa
zargi zai yi taka tsantsan to sauran mutane su ya fi cancanta su nesanta da
hakan
Manyan malamai sun karawa
juna sani akan cewar haramun ne taba jikin wadda ba muharrama ba ko da kuwa
fuskarta ce. Amman sun samu banbancin ra'ayi ta bangaren kallon mace idan babu
sha'awa kuma hakan bazai haifar da wata fitina. Idan ya zamana akwai ad-darurat
(larura) misali: rashin lafiya, cire haƙori.
Idan babu macen da za ta iya wannan aikin to ba matsala idan mutum ya taba
wadda ba muharramarsa ba (misali: ya ji jikinta akwai zafi ko wani abu
makamancin haka)
Tarh al-Tathreeb, 7/45,46
Don haka a takaicedai indai
har babu wani abu da ya fita daga jikinsa silar sha'awa to alwalarsa tananan in
sha Allahu saboda a bisa babin larurane ya taba wadda ba muharramar ta sa ba
Hadisin "Innamal
a'amali binniyati" shi ne zai aiki anan
Idan ya yi ne a bisa
ad-darurat (larura) to ba matsala amman idan da niyyar jin sha'awa ya yi to
haramun ne
Amsawa:
Usman Danliti Mato (Usmannoor
As-salafy)
Zauren Fatawoyi Bisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
🕌 1. Asalin Hukuncin Taba
Mace
A cikin shari’a, haramun ne namiji ya taba mace da ba
muharramarsa ba (wato wadda ba halalinsa ba), saboda fadin Annabi ﷺ:
"Lain yuṭ’ana fī ra’si ahadikum bi makhīṭin min
ḥadīd
khayrun lahu min an yamassa imra’atan lā taḥillu lahu."
(A Tirmizi, Al-Ṭabarāni, da Al-Albāni ya inganta – Sahih
Al-Jāmi’, 5045)
Ma’ana: “A soka wa mutum ƙarfen ƙusa a kansa ya fi alheri gare shi fiye da
ya taɓa mace da ba
halalinsa ba.”
Annabi ﷺ
ma bai taba hannun wata mace ba a lokacin da yake karɓar mubaya’a (rantsuwa) daga mata. Nana Aisha
(RA) ta ce:
"Wallahi, hannun Manzon Allah ﷺ bai taba hannun wata
mace ba. Sai dai da magana kawai yake karɓar
mubaya’a."
(Sahih Muslim, 1866)
🧕 2. Hukuncin Taba Saboda
Larura (Darura)
Idan larura ce kamar:
• likita yana duba mara lafiya mace,
• ko yana yi mata allura,
• ko yana duba zafin jiki (temperature),
to wannan ya halatta idan:
1. Babu mace likita a wancan lokacin,
2. Kuma babu sha’awa ko jin daɗi
a zuciya,
3. Kuma ya tsaya kan iyakar abin da ake bukata, ba ya ƙetarewa.
Wannan yana ƙarƙashin ƙa’idar
shari’a:
الضَّرُورَاتُ تُبِيحُ الْمَحْظُورَاتِ
“Lalura tana halatta abin da aka hana.”
Sai dai kuma ka’idar ta cigaba da cewa:
وَتُقَدَّرُ بِقَدَرِهَا
“Amma sai a tsaya gwargwadon abin da ake
buƙata
kawai.”
Wato: idan likita zai iya yin abin ba tare da taɓa fata kai tsaye ba
(misali, ta hanyar safar hannu ko zani), to ya wajaba ya kiyaye hakan.
💧 3. Matsayin Alwala
Idan likita ya taɓa
mace saboda aikin likita, ba da niyyar sha’awa ba, to:
• Alwalarsa ba ta lalace ba,
• Domin wannan taɓawa ta cikin darura ce, ba ta jima’i ko jin daɗi ba,
• Kuma niyya (niyyah) ce ke bambanta
al’amura, kamar yadda hadisin Annabi ﷺ ya tabbatar da cewa:
"Innamal a‘mālu bin-niyyāt..."
(A Bukhari da Muslim)
“Ayyuka suna bin niyya.”
Amma idan ya taɓa
da sha’awa ko niyyar jin daɗi,
to wannan haramun ne, kuma idan ya fita wani abu daga jikinsa saboda sha’awa,
alwalarsa ta lalace.
📚 4. Matsayin Mazhabai
• Hanafiyya, Malikiyya, da Hanbaliyya:
duk sun yarda cewa haramun ne taɓa
mace da ba muharrama ba.
• Shafi’iyya: sun ƙara
cewa duk wani taɓawa,
ko da ba da sha’awa ba, ya sabawa alwala.
Amma duk mazhabobin sun yarda cewa larura ta magani tana ba
da izini cikin ƙa’ida.
🌿 Kammalawa:
1. Haramun ne a taɓa
mace da ba halalinka ba — sai saboda darura.
2. Likita ko mai taimako idan ya taɓa mace saboda aikin lafiya, kuma babu sha’awa,
to babu laifi.
3. Amma dole ya tsaya kan abin da ake buƙata,
ya kuma nisanci kallon ko taɓa
al’aura.
4. Alwalarsa tana nan matuƙar ba taɓawar
sha’awa ce ba.
اللهم طهر قلوبنا وأبصارنا من الفتن، واحفظنا
بما تحفظ به عبادك الصالحين.
“Ya Allah Ka tsarkake zukatanmu da idanunmu daga fitina, Ka kare mu kamar yadda Ka kare bayinka salihai.”

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.