Akwai wata ka’ida da ya kamata mabiya Salaf Ahlus Sunnati wal Jama’a su sani; a lamarin Addini, babu wata kungiya ta Bidi’a da za ta kadaita da wata gaskiyan da babu ita a wajen Ahlus Sunna. Duk wani alheri a Addini da yake wajen wata kungiya ta Bidi’a, to akwai shi a wajen Ahlus Sunna.
Kamar yadda babu wata gaskiya ko alheri da yake
wajen Yahudawa da Nasara face akwai shi a wajen Musulmai, to haka babu wata
gaskiya ko alherin da yake wajen wata kungiyar Bidi’a face akwai shi a wajen
Ahlus Sunna. Don haka duk abin da wata kungiyar Bidi’a ta kadaita da shi a
Addini to ba gaskiya ba ne.
Wannar Ka’ida Ibnu Taimiyya ya karrara ta a wurare
daban daban. Daga ciki ya ce:
((وكل من سوى أهل السنة والحديث من الفرق فلا ينفرد عن أئمة الحديث
بقول صحيح)).
منهاج السنة النبوية (5/ 167)
((Duk wata kungiya wacce ba Ahlus Sunna da Hadisi
ba, ba sa kadaituwa da wani ingantaccen ra’ayi, a ce babu shi a wajen Malaman
Hadisi)).
A wani wajen kuma ya ce:
((إن كل طائفة سوى أهل السنة والحديث المتبعين آثار رسول الله
- صلى الله عليه وسلم - فلا ينفردون عن سائر طوائف الأمة إلا بقول فاسد، لا ينفردون
قط بقول صحيح)).
منهاج السنة النبوية (5/ 172 - 173)
((Lallai kowace kungiya wacce ba Ahlus Sunna da
Hadisi masu bin Hadisan Annabi (saw) ba, ba za su taba kadaita daga sauran al’umma
da wani ra’ayi ba face bataccen ra’ayi ne, kwata-kwata ba za su kadaita da
ingantaccen ra’ayi ba)).
A gaba ma ya ce:
((إن كل طائفة سوى أهل السنة والحديث المتبعين لآثار النبي - صلى
الله عليه وسلم - لا ينفردون عن سائر الطوائف بحق)).
منهاج السنة النبوية (5/ 177)
((Lallai kowace kungiya wacce ba Ahlus Sunna da
Hadisi masu bin Hadisan Annabi (saw) ba, ba za su taba kadaita da gaskiya daga
sauran kungiyoyi ba)).
Ma’ana: Ahlus Sunna ne kadai za su iya kadaita da
gaskiya daga sauran kungiyoyi, ba dai a samu wata kungiyar Bidi’a tana da
gaskiyar da babu ita a cikin Ahlus Sunna ba.
Saboda haka babu yadda za a yi a ce akwai wata
gaskiya ko wani alheri a Addini a wajen wata kungiya ta Bidi’a alhali a ce babu
shi a wajen Ahlus Sunna.
Irin
Rayuwar da Muke yi a Wannan Zamani
Muna wani zamani da aka rikita abubuwa a cikinsa.
An mai da Shirka ta zama Tauhidi.
An mai da Bidi'a ta zama Sunna.
An mai da wulakanta Annabi (saw) ya zama nuna son
Annabi (saw).
An mai da sabon Allah ya zama kayan ado.
An mai da riko da Addini da da'a ma Allah ya zama
kyauyanci.
An mai da haram ya zama halal.
Fasikan mutane fajirai azzalumai an mai da su
manyan mutane masu daraja.
An mai da karya ta zama gaskiya.
An mai da zalunci ya zama adalci.
An mai da jahilci ya zama ilimi.
An mai da barna ta zama gyara.
A wannan halin muke rayuwa a yau. Duka an juya
lamura saboda jahilci da son zuciya.
Mutum da sunan malumta zai fito ya fadi jahilci
amma a fito ana kambama shi, wai magana ta ilimi ya fadi.
Mutum zai yi zalunci amma a daure masa gindi.
Mutum zai yi barna a bayan kasa, ya haifar da
fitina a cikin al'umma amma a fito ana masa jinjina. In hukuma ta kama shi a
fito ana kare shi.
Mutum zai gama barna a Gomnati, ya kwashe dukiyar
kasa, amma sai ka ji ana kiraye - kirayen ya fito takaran shugaban kasa.
Kamar yadda zalunci yake cikin shugabanni haka
yake cikin talakawa. Azzalumin shugaba jarabawa ne da azabar Allah ga talakawa,
ko za su hankalta su koma ga Allah.
Saboda haka gaba daya rayuwar karya muke yi.
Dr. Aliyu Muh’d Sani (H)
Daga zauren Dr. Aliyu Muhammad Sani
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.