Ticker

6/recent/ticker-posts

Ta Yi Sallar Tarawihi Da Earpiece

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu Alaikum Warahmatallahi Wabarkatahu. Wata ce naga zatayi sallar tarawih sai ta kunna karatun Qur'ani tasa earpiece, wai sai ta rinka bin karatun sabida ta tsawaita sallar. shin yin hakan ba laifi?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa'alaikumus Salam Warahmatullahi Wabarkatuhu.

Qwarai kuwa akwai laifi domin kuwa hakan da tayi bidi'a tayi, babu wanda yasata yin hakan.

Alqur'ani yakamata ta ɗauka ta riqe tana kallo tana karantawa, inkuma bata iya karatunba, saita samu wata sura wacce ta haddace koda qulhuwallahu ne, sai takama qulhuwallahu tayita maimaitawa taita maimaitawa, kai koda aya ɗaya rak ta haddace to ya halasta kiyita maimaita wannan ayar harki gama tsayuwar kamar ilahinnas misali wannan ayar ace ita kawai ka iya acikin alqur'ani toh babu laifi kayita maimaitata har kagama tsayuwan darenda zakayi, domin hadisi ya tabbata manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam yayi tsayuwar dare guda babu ayarda yake karantawa face wani yankin wata aya can suratul ma'ida

إِن تُعَذِّبْهُمْ فَإِنَّهُمْ عِبَادُكَ وَإِن تَغْفِرْ لَهُمْ فَإِنَّكَ أَنتَ الْعَزِيزُ الْحَكِيمُ  

''Idan Ka azabta su, to lalle ne su, bãyinKa ne, kuma idan Ka gãfarta musu, to, lalle ne Kai ne Mabuwayi Mai hikima.'' (suratul Mâ'ida Aya ta 118)

Wannan yankin ayar itace yayita maimaitawa har yagama tsayuwar dare, kuma kasan dai tsayuwar Annabi ba irin taka bace.

Allah yasa mudace.

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

 https://t.me/TambayaDaAnsa

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments