Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Auren Kirista

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Naji ance wai Namiji Musulmi zai iya auren mace Kirista, amma Mace Musulma ba zata auri Namiji Kirista ba, Shin aya ce ko hadisi ko kuma magana ce kawai?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Haƙiƙa Shari'ar Muslunci ta halattawa Musulmi ya auri Mace Kirista ko Bayahudiya, wannan itace Maganar mafi yawa daga cikin Malamai Ma'abota Ilimi, kuma halaccin hakan ya samo Asaline daga cikin Al-ƙur-ani faɗin Allah()

وَطَعَامُ الَّذِينَ أُوتُوا الْكِتَابَ حِلٌّ لَّكُمْ وَطَعَامُكُمْ حِلٌّ لَّهُمْ وَالْمُحْصَنَاتُ مِنَ الْمُؤْمِنَاتِ وَالْمُحْصَنَاتُ مِنَ الَّذِينَ أُوتُوا الْكِتَابَ مِن قَبْلِكُمْ

MA'ANA

Abincin waɗan da aka zo musu da Littafi (Yahudu da Nasara) halal ne a gare ku, haka kuma abincin ku (ku Musulmi) halal ne a gare su, Haka nan (halal ne ku auri) kamammun Mata (waɗanda basa zina) daga cikin Muminai, (Musulmai) da kuma kamammun Mata daga cikin waɗanda aka zo musu da Littafi kafinku, (Yahudu da Nasara) (suratul Má'ida aya 5)

Danhaka Malamai sukace idan Ahlul-kitabi (Kirista ko Bayahudiya) ta kasance ta kame kanta bata aikata zina, to ya halatta a aureta, duk da cewa suma Ahlul-Kitabi kafirai ne Mushrikai da Nassin Al-ƙur-ani Mai girma, to amma waccan aya ta keɓance su da wannan hukunci, danhaka su kaɗai ne Allah() ya halatta mana muci yankan su da abincin su kuma mu auri Matan su, shi yasa wannan halacci ya taƙaita ne kaɗai akan Ahlul-kitabi (Yahudu da Nasara), amma sauran Kafirai da suke bautar waɗansu abubuwa dabam-dabam kokuma waɗan dama basu da wani abin bauta (Majusawa) haramun ne a aure su, saboda faɗin Allah()

وَلَا تَنكِحُوا الْمُشْرِكَاتِ حَتَّىٰ يُؤْمِنَّ وَلَأَمَةٌ مُّؤْمِنَةٌ خَيْرٌ مِّن مُّشْرِكَةٍ وَلَوْ أَعْجَبَتْكُمْ ...

MA'ANA

Kada ku auri Mata Mushrikai (Kafirai), domin (ku auri) Baiwa Mumina shi yafi alkhairi akan ku auri Mushrika koda kuwa kyawunta ya ƙayatar daku…… (suratul Bakara aya 221)

Haka nan wannan Halacci ya taƙaita ne kaɗai akan Maza Musulmai, amma baya halatta ga Mace Musulma ta auri Kirista, ko kuma dukkan wani wanda ba Musulmiba

Saidai abin lura anan shine, halacci ne kawai akace Musulmi ya auri Ahlul-kitabi, amma ko Matsayin Mustahabbi hakan bai kaiba, danhaka Malamai sukace idan Musulmi ya aminta da cewa wannan Matar Kirista da zai aura ba zata iya rinjayarsa ba ya yi Ridda kokuma ta iya rinjayar 'ya'yansa zuwa ga addinin ta to shikenan ya halatta ya aureta, danhaka ana buƙatar Mutum ya kasance yana da Ƙarfin imani dakuma ilimin addini atare dashi, sannan ya kasance niyyarsa ta yin auren itace ya yi ta ƙoƙarin nuna mata addinin Musulnci har ta gane ta karɓa, to amma duk dahaka Malamai sukace barin auren su ɗin shine yafi alkhairi, Musamman ma a irin wannan zamanin da muke cikinsa wanda galibi idan anyi irin wannan auren to Kallabi ne yake jan Rawani a madadin Rawani yaja Kallabi, abin nufi da yawa mazan sukan yi ridda ne, kuma koda Mutum yana da ƙarfin imanin da ba zata iya rinjayar sa ba, to abu ne mai sauƙi awajenta ta iya rinjayar 'yaa'yan da suka haifa tare dashi, shi yasa Malamai sukace barinsa ɗin zaifi sa Mutum yatsira da imaninsa da kuma na 'ya'yansa, danhaka gara Mutum yaje ya nemi 'yar'uwar sa Musulma ya aura

шαʟʟαнυ-тα'αʟα α'αʟαмυ

           Mυѕтαρнα Uѕмαи

              08032531505

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/FmJ5Ojsns1KFolTP8qu9GT

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐓��𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

 https://t.me/TambayaDaAmsa

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments