Ticker

6/recent/ticker-posts

Shanu Suna Biyo Shi A Mafarki

TAMBAYA (14)

Assalamualaikum. Barka da shan ruwa. Pls ina da tambaya ne pls. Wani bawan Allah ne yake min complain sosai akan yana mafarki mara dadi sosai. Wai yana gida sai shanu su biyo shi Su yi ta dukan kofar gidan da kahon su, wai sai sun shigo shikuma yai ta kuka yana addu'ah, Sai ya shiga dakinsa ya rufe. Shikuma macijin a kan window yake sai ya shige Wani rami. Pls we need your response ASAP. It's getting out of control

AMSA

USMANNOOR: Wa alaikumus salam wa rahmatullahi wa barakatuh. Alhamdu lillahi rabbil alamin wassalatu wassalamu ala rasulillah wa ala alihi wa sahbihi ajma'in. Da farko dai ya kamata mu san mafarki kala nawa ne ? Domin kuwan sanin rabe raben fassarar mafarkan zai bude kofar sanin maganin mummunan mafarkin da yakeyi.

Annabi SAW ya ce: "Mafarki mai kyau (ru'ya) daga Allah SWT ne, mummunan mafarki kuma (hulm) daga shaidan ne, don haka duk wanda ya ga abin da baya so a mafarki, sai yayi tofa sau 3 a bangaren hagunsa ya nemi tsarin Allah, ba abin da zai sameshi" (Sahih al-Bukhari, 3118)

A musulunci mafarki kala 3 ne, na farko shine mafarki wanda yake na al'ada, misali: idan mutum ya ci abinci saiya kwanta bai sha ruwa ba, to zai iyi mafarki gashinan a kusada teku kokuma korama yanata shan ruwa kokuma ya tsinci kansa yana shan pure water ko wani abu makamancin wannan. Wannan irin mafarkan babu wata illa ga mutum dukda dai kowanne irin mafarki yanada irin ma'anarsa

Saikuma mafarki na 2 shine na alkhairi akan wani albishir da akewa mutum ana kiran wannan mafarkin "ru'ya", misali: mafarkin Aljannah kokuma wata korama, mafarkin ganin Manzon Allah SAW (Kitabu Al-ru'ya littafi na 29 hadisi mai lambata 5639 wanda Jabir bin Abdullahi ya karbo hadisin cewar Manzon Allah SAW ya ce: "Duk wanda ya ganni a mafarki to hakika ni ya gani, saboda shaidan baya irin shigata a mafarki"), haka kuma zaka iya yiwa wani mafarki kamar ka ga abokinka a mafarki yana dawafi a Kaaba bayan wani lokaci kuma sai Allah cikin ikonSa kuma kaga ya kirasa Hajji ko Umra.

Watannin baya da tsakar rana na taba mafarkin matar abokinmu ta haihu, inata nemansa nayi masa albishir nace masa kuma yayi kyauta, bamu hadu ba sai bayan kwana 3, muna haduwa na fada masa yayi matukar farin cikin sannan ya cemin amman yayi mamaki saboda yau kwana 3 kenan da zuwansu asibiti aka gano tana dauke da juna biyu. Kuma nima kwana 3 din da ya wuce dinne dai nayi wannan mafarkin. Idan ba ikon Allah ba, ta yaya haka zata faru ? (Allah ya sauke ta lafiya)

Irin wadannan mafarkai na bushara ne daga Allah SWT

Na karshe kuma na 3 shine mafarki mummuna kokuma na sharri, shikuma ana kiransa da "hulm" misali: zai iya mafarkin ana masa azaba da wuta, kokuma, dannau ya danne mutum, kokuma dabba ta biyoka (misali mafarkin shanu suna tunkushinka kokuma micizai suna saranka), wadannan duk daga shaidan ne. Kuma anayiwa mutum mafarki, akwai sanda na taba mafarki wani abokin karatuna an biyoshi anata dukansa har saida ya karye, lokacinda na farka na fada masa nace yayi sadaka saboda neman kariya, kullum da safe sai ya bada sadakar kosai

A satin sai wannan iftila'in ya faru amman ba akanshi ba, cikin ikon Allah sai karayar ta sauka akan wani abokin karatunnamu daban, mashin ya bugeshi ya karye, so kaga anan fassarar mafarkin da nayi ta fito kuma sadakar kosan nan da yake itace ta zame masa garkuwa

Abin da yake kawo mafarki mummuna "hulm" yanada alaqa da mantawa dakuma sakaci na rashin azkar din kwanciya bacci kamar yanda Manzon Allah SAW ya koyardamu

Imam Muslim ya rawaito hadisi wanda aka karbo daga Samura bin Jundab ya ce duk lokacin da Annabi SAW ya idar da sallar asuba yakan juyo da fuskarsa mai albarka garemu sannan ya ce: "Shin akwai wani a cikinku wanda yayi mafarki a jiya da daddare" ? (Kitabu Al-ru'ya littafi na 29 hadisi na 5652)

Ana son mutum ya saba da aikata wadannan sunnonin guda 7 kamar haka:

1) Ka fadawa abokinnaka ya dinga alwala cikakkiya kafin ya kwanta saboda hadisin da yake a cikin sahih Muslim mai lambata 2710 cewar wani sahabi ya ce: Annabi SAW ya ce "Duk sanda zaku bacci to kuyi alwala kamar dai ta sallah, sannan ku kwanta da tsagin dama

2) Ya dinga karanta Amanar Rasulu kafin ya kwanta. An karbo daga Abu Mas'ud ya ce Annabi SAW ya ce: "Duk wanda ya karanta ayoyin karshe na Suratul Baqara to sun isar masa" (Sahih Al-Bukhari 5009)

3) Ya dinga kakkabe shimfidarsa, saboda Hadisin Abu Hurairata RTA wanda Manzon Allah SAW ya bada umarnin a dinga kakkabe abin kwanciya kafin ayi bacci saboda mutum baisan menene abin da ya sauka akan shimfidarsa ba lokacin da bayanan (Bukhari 6320 da Muslim 6714a)

4) Ya dinga karanta azkar. An karbo Hadisi daga ya ce Nana Fatima RA tazo wajen Annabi SAW ya bata baiwa wadda zata tayata aiki, sai Ma'aiki SAW ya ce: "Bana baki abin da yafi baiwa ba ?" Saiyace: "Kafin ki kwanta bacci ki dinga karanta Subhanallah 33, Alhamdulillah 33 saikuma Allahu Akbar 34" Sayyadina Ali RTA ya ce: "Tun da naji wannan (garabasa) ban taba fashin kwanciya ba face saina karantasu" Sai wani sahabi ya ce ko a daren yakin Siffin saida ka karantasu sai Sayyadina Ali RTA ya ce ko a daren yakin Siffin (Bukhari 5362 da Muslim 2727a)

5) Ya dinga kwanciya da tsagin dama. Saboda hadisin da Hudaifatul Yamani RTA ya karbo cewar duk sanda Annabi SAW zai kwanta bacci yakan saka hannunsa na dama a kuncinsa sannan ya ce: "Allahumma bismika amutu wa'ahya" Sannan kuma idan ya tashi sai ya ce: "Alhamdulillahil lazi ahyana ba'ada ma'amatana wa'ilaihinnushur" (Hadisin yana cikin Sahihul Bukhari mai lambata 6314)

6) Maybe abokin naka yana kwanciyar ruf da ciki ne. Akwai hadisi wanda Abu Dharr Al-Gifari RTA ya karbo ya ce: "Akwai lokacinda Ma'aiki SAW yazo wucewa sai ya ganni nayi kwanciyar ruf da ciki sai yasa kafarsa mai albarka ya zungureni ya ce: "Ya Junaidib ! Wannan itace irin kwanciyar yan wuta" Sahih (Darussalam) Ibn Majah 3724

7) Ya dinga karanta Ayatul Kursiyyu kafin ya kwanta bacci. Saboda kissar abin da ya faru tsakani Abu Hurairah da Shaidan wanda a karshe dai Shaidan ya bawa Abu Hurairah ayoyin kariya (Ayatul Kursiyyu) cewar idan Abu Hurairah din ya karanta to Allah zai turo Mala'ika yayi gadinsa babu Shaidanin da zaizo kusa da shi har gari ya waye. Har Ma'aiki SAW ya ce: "Shaidan ya fadi gaskiya duk da dai makaryaci ne" (Bukhari 2311)

A karshe inason a sanar da shi cewar ya cire duk wani hoto da yake a jikin bangon dakin da yake kwana, hoto wanda yake a rataye na mutum ne ko zane haka, kamar irin zanen tsuntsaye/mage/shanu ko cartoon characters haka kokuma irin hotunan nan na enlargement saboda munsan dai hadisin da Sayyadina Ali RTA ya karbo cewar;

Watarana ya gayyaci Annabi SAW walima lokacin da yazo sai yaga hotuna a gidan Sayyadina Alin saiya juya baya zai koma, sai ya ce masa: "Ya Ma'aikin Allah ! Ran mahaifina da mahaifiyata fansa gareka, saboda me zaka koma ?" Sai Annabi SAW ya ce: "Lallai da akwai labule a gidan kuma a jikin labulen da akwai hoto, kuma mala'iku basa shiga gida wanda akwai hoto" (Na fito da wannan hadisi ne daga cikin littafin Zad Al-Ma'ad na Imam Ibn Al-Qayyim Aljauziyya Rahimahullah wanda ya kafa hujjar hadisin da riwayar Ibn Majah 2/323 da Abu Ya'ala a musnad dinsa sannan kuma hadisin sahihi ne wanda Ibn Majah ne marawaicinsa)

Akwai wata fira da na taba jin wani Aljani ya ce suna hawa kan hoto dukda dai yawancin Aljanu akwai su da zuqi ta malli amman idan kayi comparing hadisin can zakaga cewar indai har mala'iku bazasu shigo gida mai hoto ba to tabbas kam Aljanu sun samu wajen fakewa, maybe hakan yasa suyita tsoratarda abokinnaka a mafarki silar hotunan da suke a makwancin nasa kamar yanda suka taba tsoratarda wata dalibata bayan magariba taga wani Aljani ya fito daga jikin drawing dake bangon kitchen din gidansu ya biyota ta kwalla ihu ta shige dakin mamansu, sai da safiya tayi aka goge drawing din saboda kowa ya kasa gogeshi a daren jiya. Nace mata ta yawaita karanta azkar na safiya da maraice

Allah ya kiyayemu daga sharrin kawunanmu dakuma sharrin Aljanun dake rayuwa tare damu, Amin

Subhanakallahumma wabi hamdika ash'hadu anla ilaha illa anta, astaghfiruka, wa'atubi ilayk

WALLAHU TA'ALA A'ALAM

Aturawa yan uwa musulmi maza da mata domin mu amfana da ilimin baki daya musamman ma a wannan zamanin wanda gidaje dai dai ne da babu hoto a ciki

Amsawa:

 

✍️Usman Danliti Mato (Usmannoor_As-salafy)

Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/IerSx3AH0ZSJyHIuIYfqds

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments