Ticker

6/recent/ticker-posts

Ɓacewar Kuɗi A Gida

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalaamu Alaikum Wa Rahmatul Laah. Malam, wata matsala ce ta sha min kai: Ko yana yiwuwa kuɗaɗe su riƙa ɓacewa a cikin gida ba tare da wani mutum ya ɗauke su ba?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laahi Wa Barakaatuh.

Masana sun ce zai iya yiwuwa kaya ko kuɗi su riƙa ɓacewa a inda mutane suka ajiye su, ko da wani daga cikinsu bai ɗauka ba. Domin ai ba mutane ne kaɗai suke rayuwa a duniyar nan ba. Akwai aljanu mutanen ɓoye waɗanda suke ganinmu ta inda mu ba mu ganin su.

Idan dai har sheɗanin aljani zai iya shiga masallacin Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) a cikin surar wani tsoho kuma har ya riƙa ƙoƙarin sace kayan abincin da Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya bai wa Abu-Hurairah (Radiyal Laahu Anhu) a matsayin gadi, to a wane wuri ne a cikin gida za a ce sauran danginsa ba za su iya shiga, su ɗebo kaya ko kuɗaɗe ba.

Maganin irin wannan dai in shã Allahu shi ne a riƙa ajiye kaya da kuɗaɗe a ɓoyayyen wuri tare da faɗin Bismillaah a lokacin ajiyewa da kullewa. Domin Annanbi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya tabbatar da cewa sheɗanu ba sa buɗe ƙofar da aka rufe da Bismillaah.

Sannan kafin a fara tunanin jingina batun satar ga ɓoyayyun aljanu, a tabbatar an tsananta bincike a cikin mutane tukun.

A dogara ga Allaah a yi istirjaa’i, a nemi sakayya da samun musanye daga Allaah Ubangijin Halittu a lokacin da aka gano aukuwar satar. Kar a tsananta wurin zargin wani mahaluki ba da cikakkiyar hujja ba, mai kai wa ga aukuwar fitina. Galibi abin da sheɗanun aljanun suke neman aukuwarsa kenan a tsakanin musulmi.

Allaah ya ƙara mana kariya.

WALLAHU A'ALAM

Sheikh Muhammad Abdullaah Assalafiy

Zauren Fatawowi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/BSA30hdZD7V3WSJF8WVwUj

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments