𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum warahamatullahi. Malam mace za ta yi sallah toh sai aka ce ba lallai ba ne sai ta ta da iƙama kawai Allahu akbar zatace sai tafara karatun sallah? Wai shin wannan ya halatta ko dole sai ta ta da wannan iƙama?
𝐀𝐌𝐒𝐀👇
وعليكم السلام ورحمة الله.
ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ ﺭﺏ ﺍﻟﻌﺎﻟﻤﻴﻦ ، ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﺳﻴﺪﻧﺎ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﻋﻠﻰ ﺁﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﺃﺟﻤﻌﻴﻦ، ﻭﺑﺎﻟﻠﻪ ﺍﻟﺘﻮﻓﻴﻖ،
Anyi tambaya ga kwamitin ba da fatawa na kasar
Saudiyyah cewa shin an wajabta ma mace a shari'ah ta yi iƙaamah idan tana jagorantar wasu mata a sallah? Sai suka amsa
da cewa: ba a wajabtawa mata yin iƙaamah ba a sallah ko da mace
na sallah ita kaɗai ko mace daya tana jagorancin wasu mata a jam'i,
kamar yadda ba a shar'anta musu yin kiran sallah ba. (Fataawa al-Lajnah
al-Daa’imah, 6/84).
An tambayi Shaykh Ibn Baaz (rahimahullah) cewa
"Shin ya halatta ga mace ta yi Kiran sallah da Iƙaamah a sallah ko bai halatta ba??" Sai Shaykh ya amsa
cewa: ba a shar'anta Wa mata yin kiran sallah ko Iƙaamah ba, amma wannan ga maza ne. Da kiran sallah da Iƙaamah babu dayansu da aka shar'anta ga mata, Kawai za su yi
sallarsu ne babu kiran sallah babu iƙaamah. (Majmu'ul Fataawa wa
Maƙaalaat Mutanawwi’ah, 10/356)
والله أعلم،
SHIN ITAMA MACE ZA TA DINGA TADA IƘAMA NE KAMAR NAMIJI
TAMBAYA
(211)❓
Assalamu
alaikum.malamai barkan ku da warhaka dan Allah Ina da tambaya akan sallah.
tambayar itace kamar haka mlm yaya mafarin sallar farillah na mace shinzata
tada ikamane kokuma za ta yi niyane kamar sallar nafilah?
AMSA❗
Waalaikumus
Salam Warahmatullahi Wabarakatuhu
An tambayi
Committeen Fatawa na Saudiyya: shin ya halatta a shari'a mace ta tada iqama
yayin da take Jan Mata a sallah
Suka ce:
"Baa shar'anta mace ta yi iqama ba ko za ta ja Mata salla ko kuma ita
kadai zatayi sallah ba kamar yanda ba'a shar'anta musu suyi Kiran Sallah
ba"
(Fatawa
Al-Lajnah Ad-Da’imah, 6/84)?
An tambayi
Marigayi Shaikh Abdulaziz Bin Baaz (Rahimahullah), shin ya halatta mace ta yi Kiran
sallah da Kuma iqama a sallarta
Ya ce:
"Baa shar'anta Kiran sallah ga mata ba, wadannan maza aka shar'anta wa
(Majmu`
Fatawa wa Maqalat Mutanawwi`ah, 10/356)
Wallahu
ta'ala a'alam
Amsawa:
Usman
Danliti Mato (Usmannoor_Assalafy)
Zauren
Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Ku kasance Damu...
Ku Kasance Damu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa
Tare Da Faɗakarwa a Sunnah.
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/J1hm5Tw12uYBƙfaiPwf28l
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.