Ticker

6/recent/ticker-posts

Hukuncin Tashi Tsaye Idan An Wuce Da Gawa

 𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum. Malam tambayana shin wai meyasa in an taho da gawa zakaga mutane a kan hanya suna tashi tsaye?

𝐀𝐌𝐒𝐀👇

وعليكم السلام ورحمة الله.

ﺍﻟﺤﻤﺪ ﻟﻠﻪ ﺭﺏ ﺍﻟﻌﺎﻟﻤﻴﻦ ، ﻭﺻﻠﻰ ﺍﻟﻠﻪ ﻋﻠﻰ ﺳﻴﺪﻧﺎ ﻣﺤﻤﺪ ﻭﻋﻠﻰ ﺁﻟﻪ ﻭﺻﺤﺒﻪ ﺃﺟﻤﻌﻴﻦ، ﻭﺑﺎﻟﻠﻪ ﺍﻟﺘﻮﻓﻴﻖ،

ﻋَﻦْ ﻋَﺎﻣِﺮِ ﺑْﻦِ ﺭَﺑِﻴﻌَﺔَ ﻗَﺎﻝَﻗَﺎﻝَ ﺭَﺳُﻮﻝُ ﺍﻟﻠَّﻪِ ﺻَﻠَّﻰ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﻋَﻠَﻴْﻪِ ﻭَﺳَﻠَّﻢَﺇِﺫَﺍ ﺭَﺃَﻳْﺘُﻢْ ﺍﻟْﺠَﻨَﺎﺯَﺓَ ﻓَﻘُﻮﻣُﻮﺍ ﻟَﻬَﺎ ﺣَﺘَّﻰ ﺗُﺨَﻠِّﻔَﻜُﻢْ ﺃَﻭْ ﺗُﻮﺿَﻊَ.

(ﺭﻭﺍﻩ ﻣﺴﻠﻢ، 958)

An karɓo daga Aamir Ibn Rabee'ah ya ce: Manzon Allah (sallallahu alaihi wa sallam) ya ce; Idan kun ga Janaza (Gawa ana Wucewa da ita) Ku tashi tsaye gareta har sai ta shige gabanku ko an sanyata (a kabari).

(Muslim, 958)

ﻋَﻦْ ﺍﺑْﻦِ ﺃَﺑِﻲ ﻟَﻴْﻠَﻰﺃَﻥَّ ﻗَﻴْﺲَ ﺑْﻦَ ﺳَﻌْﺪٍ ﻭَﺳَﻬْﻞَ ﺑْﻦَ ﺣُﻨَﻴْﻒٍ ﻛَﺎﻧَﺎ ﺑِﺎﻟْﻘَﺎﺩِﺳِﻴَّﺔِ، ﻓَﻤَﺮَّﺕْ ﺑِﻬِﻤَﺎ ﺟَﻨَﺎﺯَﺓٌ ﻓَﻘَﺎﻣَﺎ، ﻓَﻘِﻴﻞَ ﻟَﻬُﻤَﺎﺇِﻧَّﻬَﺎ ﻣِﻦْ ﺃَﻫْﻞِ ﺍﻟْﺄَﺭْﺽِ، ﻓَﻘَﺎﻟَﺎ(ﺇِﻥَّ ﺭَﺳُﻮﻝَ ﺍﻟﻠَّﻪِ ﺻَﻠَّﻰ ﺍﻟﻠَّﻪُ ﻋَﻠَﻴْﻪِ ﻭَﺳَﻠَّﻢَ ﻣَﺮَّﺕْ ﺑِﻪِ ﺟَﻨَﺎﺯَﺓٌ ﻓَﻘَﺎﻡَ، ﻓَﻘِﻴﻞَﺇِﻧَّﻪُ ﻳَﻬُﻮﺩِﻱٌّ؟ ﻓَﻘَﺎﻝَﺃَﻟَﻴْﺴَﺖْ ﻧَﻔْﺴًﺎ)

ﺭﻭﺍﻩ ﻣﺴﻠﻢ (960)

An karɓo Daga Inn Abi Lailah cewa: Lalle Ƙais ibn Sa'd da Sahla ibn Hunaifi sun kasance (suna Zaune) a Ƙaadisiyyah, sai aka wuce da gawa a gabansu, sai suka miƙe tsaye, sai wasu suka ce musu: "Cewa ita (wannan gawar) ta mutanen kasa ne (kafuran garin)" sai suka ce "(Lalle Manzon Allah sallallahu alaihi Wa sallam, an wuce da gawa sai ya tashi tsaye, wasu sukace: Shin shi (gawar) ba bayahude ba ne??? Sai (Manzon Allah) ya ce: Toh shi ba rai ba ne??).

(Muslim, 960)

An so ga mutum idan aka wuce da gawa, ya tashi tsaye gareta, domin Manzon Allah (sallallahu alaihi Wa sallam) ya yi Umarni da haka, kuma ya aikata, sannan ya bari (ya daina tashi tsaye). Aikata tashin da kuma rashin tashi, rashin tashin domin ya bayyana cewa tsayuwar ba wajibi bace.

(Majmu'ul Fataawa Wa Rasaa'il na Ibn Uthaymeen, 17/112)

والله أعلم،

Ku Kasance Da mu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa Tare Da Faɗakarwa a Sunnah.

𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇

https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://chat.whatsapp.com/CFp8AF5lYJt7v6HZ3i6mjf

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments