Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Aslm Alkm, Dan Allah malam akwai wani addua Kuma
inason sanin ingancinsa,
اللهم اني اسالك وأتوجه إليك بنبينا محمد نبي الرحمة يا محمد إني أتوجه إليك إلى ربيا فيقضي حاجتي.
Wai mutum zai iya yin wannan addu'a yaroƙi Allah bukatarsa, Dan Allah malam ya inganta?
𝐀𝐌𝐒𝐀👇
Wa Alaikumus salam Warahmatullahi Wabarakatuhu,
Godiya ta tabbata ga Allah.
Imam Ahmad da wasunsu sun ruwaito da isnadi sahihi
daga Usman bn Haneef cewa: wani makaho ya zo wajen Annabi (Sallallahu Alaihi
Wasallam) ya ce: “Ka roƙa min Allah Ya ba ni lafiya.
Manzon Allah
(tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi) ya ce: “Idan ka so, zan yi maka addu’a;
Kuma idan ka
so, zan jinkirta maka wancan, kuma shi ne mafi alheri a gare ka (jinkirtawa).
[A wani hadisin kuma ya ce: “… Ko kuma idan ka so, ka
yi haƙuri, kuma shi ne mafi alheri a gare ka.” Ya ce: Ka yi
mini addu’a (yanzu). Sai Manzon Allah ﷺ ya umarce shi da ya yi
alwala ya kyautata, sannan ya sallaci raka’a biyu, sai ya yi wannan addu’ar:
اللهم إني أسألك ، وأتوجه إليك بنبيك محمد نبي الرحمة ، يا محمد إني توجهتُ بك إلى ربي في حاجتي هذه ، فتقضى لي ، اللهم فشفّعه فيَّ وشفّعني فيه.
Ma'ana: “Ya Allah ina rokonka, kuma ina tuba zuwa gare
ka bisa ga Annabinka Muhammadu, Annabin rahama. Ya Muhammad, ina juyowa da
yardarka zuwa ga Ubangijina game da wannan bukata tawa, domin ta biya mini. Ya
Allah ka kar6i cetonsa a kaina, kuma ka kar6i cetona a kansa”. Sai mutumin ya
karanta wannan kuma ya warke.
Wasu mutanen su kan sami ruɗani game da wannan hadisin,
suna ganin kamar ya zama hujja ga wasu nau'ikan tawassuli na bidi'a (neman
kusanci ga Allah), amma ba haka lamarin yake ba kamar yadda malamai suka yi
bayani, wanda malamai da yawa sun yi martani game da haka, daya daga cikin mafi
ingancin martani na ilimi dangane da wannan mas’ala shi ne wanda babban malamin
nan Shaikh Muhammad Nasir ad-Deen al-Albaani ya rubuta a cikin littafinsa
at-Tawassul Anwaa’uhu wa Ahkaamuhu (akwai shi da turanci mai suna Tawassul:
Its). Nau'o'insa da Hukuncensa). Duk da ba a kan wannan kike tambaya ba.
Amma dai dangane da tambayar ki wannan hadisin malamai
sun kawo shi a matsayin daya daga cikin mu'ujizar Annabi (Sallallahu Alaihi
Wasallam) kuma daya daga cikin addu'o'insa da aka amsa, kuma misalin abin da
Allah ya bayyana ta albarkar addu'arsa ta ban mamaki. Abubuwan da suka faru da
kuma waraka daga rashin lafiya nan ta ke. Bisa ga addu'ar Annabi ga wannan
makaho, Allah ya dawo masa da ganinsa. Don haka malaman hadisi irin su al-Bayhaƙi da sauransu suka ruwaito shi daga cikin alamomin Annabta
(dalaa’il an-nubuwwah). Wannan yana nuni da cewa dalilin warkar da makaho shi
ne addu'ar Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam).
Saboda haka ma iya cewa idan mutum ya roki Allah da
wannan addu'ar yana mai imani, to Allah zai amsa. Kuma addu'a da hadisi sun
inganta.
Kuma Allah Ne Mafi Sani.
✍️Shashen Fatawowi Bisa Ƙur'ani Da Sunnar Annabi
Sallallahu Alaihi Wasallama A Fahimtar Magabata Na Kwarai
Ku Kasance Damu Cikin Wannan Group Domin Ilimantarwa
Tare Da Faɗakarwa a Sunnah.
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/EPG7wVPlgxRFR4R9CdR8xY
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.