𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum, yayana barka da
dare, don Allah tambayata ita ce: a koya min yadda bawa zai yi addu'a, nagode.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa'alaikumus Salamu, Allah maɗaukakin
Sarki yana son a roƙe shi, kuma yakan yi fushi da wanda ba ya roƙon shi, kuma
shi ya ce ku roƙe ni zan amsa maku, kamar yadda aya ta 60 ta suratu Gáfir ta yi
bayani. Addu'a tana da matsayi mai girma a addinin Musulunci, har ma ta kai ga
Annabi ﷺ ya ce: Addu'a ita ce ibada". Abu Dáwud 1479, Ibn Majah 3828.
Daga cikin ladubban da bawa ya
kamata ya kiyaye su domin addu'arsa ta sami saurin karɓuwa a wurin Allah sun haɗa
da:
1. Mai addu'a ya zama mai kaɗaita
Allah a bautarsa, ya kiyaye shirka da sauran saɓon Allah, ya zamo mai ɗa'a ga
Allah.
2. Ya zamo mai tsarkake niyyarsa
a addu'ar da yake yi, yana yi ne don Allah.
3. A wajen yin addu'ar ya roƙi
Allah ta hanyar yin tawassuli da sunayen Allah kyawawa.
4. Ya zamo mai yabo da jinjina ga
Allah da duk abin da Allah ya cancanci a yi masa hakan. Saboda ya tabbata wani
mutum ya zo ya yi sallah a lokacin Annabi ﷺ yana zaune, da wannan mutum ya idar
da sallah, sai ya roƙi Allah da cewa Allah ya yi masa gafara da rahama, sai
Manzon Allah ﷺ ya ce masa: "Kai mai sallah ka yi gaggawa, idan ka yi
sallah, to ka zauna ka yabi Allah da abin da ya cancance shi, ka yi mini
salati, sannan sai ka yi addu'a". Tirmizhiy 3476.
5. Yi wa Manzon Allah ﷺ salati
kafin fara addu'a kamar yadda ya gabata a hadisi na sama.
6. Fuskantar alƙibla yayin
addu'a, saboda ya tabbata Annabi ﷺ ya fuskanci alƙibla ya yi addu'a a lokacin
da ya fuskanci rundunar mushirikai su dubu ɗaya (1000) a ranar yaƙin Badar, shi
kuma da Sahabbansa su ɗari uku da sha tara (319), ya fuskanci alƙibla ya ɗaga
hannayensa ya roƙi Allah ya cika masa alƙawarin da ya yi masa, kamar yadda
Muslim ya ruwaito a hadisi mai lamba ta 1763.
7. Daga hannaye a lokacin addu'a.
Saboda sahabi Salmanu ya ruwaito cewa Annabi ﷺ ya ce: "Lallai Ubangijinku
SWT Mai kunya ne, kuma Mai girma ne, yana jin kunyar bawansa idan ya ɗaga
hannayensa zuwa gare shi ya kuma dawo da su ba komai". Abu Dáwud 1488.
8. Yin yaƙini a kan cewa Allah
zai amsa maka addu'arka, kamar yadda hadisi mai lamba 3479 a Tirmizhiy ya
tabbatar, wato ka riƙa jin tabbacin cewa lallai Allah zai karɓi addu'arka.
9. Naci da yawaita yin addu'ar a
kai a kai.
10. Yin ƙanƙan da kai a cikin
al'amura.
11. Cin abinci ta hanyar halal,
da sanya tufafi ta halal, da nisantar haram ta kowace hanya.
Saboda Abu Hurairata ya ruwaito
cewa Annabi ﷺ ya ce: "Ya ku mutane lallai Allah mai tsarki ne, ba ya karɓa
sai mai tsarki, lallai Allah ya umurci Muminai da abin da ya umurci Manzanni,
sai ya ce: "Ya ku Manzanni, ku ci daga tsarkaka, ku yi aiki na ƙwarai...),
sannan kuma ya ce: "Ya ku waɗanda suka yi imani ku ci daga tsarkaka na
abin da muka azurta ku)...".
Muslim 1015.
Wannan na nuni a kan cewa cin
halal da shan halal, da sanya tufafin halal, dalilai ne da suke sa a karɓi
addu'ar bawa.
Allah ya sa mu dace, amin. Kuma
duk bawan da yake kiyaye waɗannan abubuwa da iznin Allah Allah zai riƙa karɓar
addu'arsa.
Allah ne mafi sani.
Jamilu Ibrahim Sarki, Zaria.
Zauren Tambaya Da Amsa Abisa
Alkur'ani Da Sunnah. Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group Zaku iya bi ta Links ɗin
mu...
Ladubban Yin Addu’a
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum, yayana barka da dare, don Allah
tambayata ita ce: a koya min yadda bawa zai yi addu’a, nagode.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa’alaikumus Salamu, Allah maɗaukakin Sarki yana son a roƙe shi, kuma yakan yi fushi da wanda ba ya roƙon shi, kuma shi ya ce
ku roƙe ni zan amsa maku,
kamar yadda aya ta 60 ta Suratul Gáfir ta yi bayani:
وَقَالَ رَبُّكُمُ ادْعُونِي أَسْتَجِبْ لَكُمْ ۚ إِنَّ الَّذِينَ
يَسْتَكْبِرُونَ عَنْ عِبَادَتِي سَيَدْخُلُونَ جَهَنَّمَ دَاخِرِينَ
Kuma Ubangijinku ya ce: ‘‘Ku kira Ni in karɓa muku. Lalle waɗannan da ke
kangara daga barin bauta Mini, za su shiga Jahannama sunã ƙasƙantattu.’’ (Suratul Gáfir aya ta 60)
Addu’a tana da matsayi mai girma a addinin
Musulunci, har ma ta kai ga Annabi Sallallahu alaihi Wasallam ya ce: Addu’a ita
ce ibada". Abu Dáwud 1479, Ibn Majah 3828.
Daga cikin ladubban da bawa ya kamata ya kiyaye su
domin addu’arsa ta sami saurin karɓuwa a wurin
Allah sun haɗa da:
1. Mai addu’a ya zama mai kaɗaita Allah a bautarsa, ya kiyaye shirka da sauran saɓon Allah, ya zamo mai ɗa’a ga Allah.
2. Ya zamo mai tsarkake niyyarsa a addu’ar da yake
yi, yana yi ne don Allah.
3. A wajen yin addu’ar ya roƙi Allah ta hanyar yin tawassuli da sunayen Allah
kyawawa.
4. Ya zamo mai yabo da jinjina ga Allah da duk
abin da Allah ya cancanci a yi masa hakan. Saboda ya tabbata wani mutum ya zo
ya yi sallah a lokacin Annabi Sallallahu alaihi Wasallam yana zaune, da wannan
mutum ya idar da sallah, sai ya roƙi Allah da cewa Allah ya yi masa gafara da rahama, sai Manzon Allah
Sallallahu alaihi Wasallam ya ce masa: "Kai mai sallah ka yi gaggawa, idan
ka yi sallah, to ka zauna ka yabi Allah da abin da ya cancance shi, ka yi mini
salati, sannan sai ka yi addu’a". Tirmizhiy 3476.
5. Yi wa Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam
salati kafin fara addu’a kamar yadda ya gabata a hadisi na sama.
6. Fuskantar alƙibla yayin addu’a, saboda ya tabbata Annabi
Sallallahu alaihi Wasallam ya fuskanci alƙibla ya yi addu’a a lokacin da ya fuskanci rundunar mushirikai su dubu ɗaya (1000) a ranar yaƙin Badar, shi kuma da Sahabbansa su ɗari uku da sha tara (319), ya fuskanci alƙibla ya ɗaga hannayensa ya roƙi Allah ya cika masa alƙawarin da ya yi masa, kamar yadda Muslim ya
ruwaito a hadisi mai lamba ta 1763.
7. Daga hannaye a lokacin addu’a. Saboda sahabi
Salmanu ya ruwaito cewa Annabi Sallallahu alaihi Wasallam ya ce: "Lallai
Ubangijinku Subhanah wata’ála Mai kunya ne, kuma Mai girma ne, yana jin kunyar
bawansa idan ya ɗaga hannayensa
zuwa gare shi ya kuma dawo da su ba komai". Abu Dáwud 1488.
8. Yin yaƙini a kan cewa Allah zai amsa maka addu’arka, kamar yadda hadisi mai lamba
3479 a Tirmizhiy ya tabbatar, wato ka riƙa jin tabbacin cewa lallai Allah zai karɓi addu’arka.
9. Naci da yawaita yin addu’ar a kai a kai.
10. Yin ƙanƙan da kai a cikin al’amura.
11. Cin abinci ta hanyar halal, da sanya tufafi ta
halal, da nisantar haram ta kowace hanya. Saboda Abu Hurairata ya ruwaito cewa
Annabi Sallallahu alaihi Wasallam ya ce: "Ya ku mutane lallai Allah mai
tsarki ne, ba ya karɓa sai mai
tsarki, lallai Allah ya umurci Muminai da abin da ya umurci Manzanni, sai ya
ce: "Ya ku Manzanni, ku ci daga tsarkaka, ku yi aiki na ƙwarai...), sannan kuma
ya ce: "Ya ku waɗanda suka yi
imani ku ci daga tsarkaka na abin da muka azurta ku)...". Muslim 1015.
Wannan na nuni a kan cewa cin halal da shan halal,
da sanya tufafin halal, dalilai ne da suke sa a karɓi addu’ar bawa.
Allah ya sa mu dace, amin. Kuma duk bawan da yake
kiyaye waɗannan abubuwa da iznin
Allah Allah zai riƙa karɓar addu’arsa.
Allah ne mafi sani.
Jamilu Ibrahim Sarki, Zaria.
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur’ani Da Sunnah. Ku
kasance Damu...
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.
0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.