Ticker

6/recent/ticker-posts

Wacce Take Burge ni

Tsokaci: Wai “kowa da abin da ya dame shi!” inji maƙwabcin mai akuya yayin da ya sayi kura. ‘Yan’adam na abota/ƙawance ko soyayya. Yawanci ana gina wulɗayyar da wasu tubalai na musamman. Daga cikinsu akwai sha’awa da dukiya da ilimi da mutunci da fice ko ɗaukaka da hali ko ɗabi’a. Waɗannan kuwa su ke zaman ginshiƙan da ke tallafe da shigifar hulɗayyar. Yayin da aka samu gazawar ginshiƙan, sai dai a ce “Allah ya kiyaye!” Zuciyata ma na da irin nata muradi. Tana da wani abu na musamman da ke burge ta. Yayin da mace ta mallaki wannan abu, lallai ta zama “macen da take burge ni!”
WACCE TAKE BURGE NI

             Ta

Ba wacce taf fi kowa a dandali na kyau ba,
Ba sai tana da siffa na burge ‘yan maza ba,
Ban damu ‘yar firat ce koko duma-duma ba,
Ba sai tsawonta daidai abin ake yabo ba,
            Ban damu ko fara ce koko baƙa wulik ba.

Ban damu ko da siffa na kanta ya yake ba,
Ban damu sai da gashi ko da ko talkobo ba,
Ban damu ko goshinta ya shigga off site ba,
Ban damu ko ƙeyarta ta wucce boundry ba,
            Ban damu ko fuska tana da kyan gani ba.

Ban duba kunnuwanta in sun kyawun gani ba,
Ban duba ko idonta fari koko da ja ba,
Ba wai tsawo na hanci koko in ya daɓe ba,
Ba wai siffa ta baki da anka yo mata ba,
            Ba ko tsarin haƙora da ac cikin baki ba.

Ban damu in a miƙe ko danƙare wuya ba,
Ban damu kafaɗunta salonsu ya yake ba,
Ban damu hannuwanta nau’insu ko siffa ba,
Ban damu ko da cindo ƙida na yatsukan ba,
            Ban damu in faratanta na da kyan gani ba.

Ban damu ko kamannun cikinta ya yake ba,
Ban damu kunkuminta ko yai zubin diri ba,
Ban damu in ƙafafunta sun yi kyan gani ba,
Ban ce ko babu kyawu ko ba ni so na kyau ba,
            Amma a zuciyata ba shi yake mulki ba.

Ba sai tana da nera tuli a bankuna ba,
Ba sai tana albashi abin a zo gani ba,
Bai sai tana sana’a na burge al’uma ba,
Ba sai a kasuwanci jarinta ya ɗaga ba,
            Kuɗi da arzikinta ba su nake gani ba.

Ba wacce kaddarori a nan ta yo fice ba,
Ba sai tana da mota koko gidan shiga ba,
Ba sai tana da fili da ko dabbobin kiyo ba,
Ban musa kyansa sam-sam biɗa da yin na kai ba,
            Sai dai a zuciyata ba shi nake gani ba.

Ba sai gidan sarauta da ke da ɗaukaka ba,
Ba sai gidan tajirci da sunka yo fice ba,
Ba ‘yar gidan siyasa da ke a gwamnati ba,
Ba wai gidan malunta tushe na illimi ba,
            Ban damu da giddansun ba itta zan yi duba.

Duk waɗanda ba su ko ni nake hari ba,        
Macen da ni nake so ba zan ƙi ambata ba,
MAI HALIN ƘWARAI wacee ba ta zamba,
Ba wacce gaskiyarta sai dai a yo sha’an ba,
            Ba wadda ke da halin gani na duniya ba.

Ba wacce ba ta kunyar ta yo abin faɗi ba,
Ba wacce ba kawaici gare ta ko kaɗan ba,
Ba wacce ba ta tsoron ta yo abin gayi ba,
Ba macce mai gadara mai nuna tutiya ba,
            Ba wacce ke ganin ta fi ai mata hani ba.

Ba wacce ke da ƙyashi ko nuna hassada ba,
Ba wacce ke da gulma ko son a yo mata ba,
Ba wacce ke da ƙeta ga ɗan da ba nata ba,
Ba wacce ba ta buri na taimakon umma ba,
            Ba wacce rayuwarta bai zam abin gwadi ba.

Ba wacce tarbiyarta bai wucce fafaki ba,
Ba wacce ko iyaye ke yin Allah wadai ba,
Ba wacce sai an ce yi, koko a ce bari ba,
Ba wacce in an yi hani take maiman kure ba,
            Ban son macen da ba ta san shiru da maggana ba.

Ba mai yawan surutun da babu kan gado ba,
Ba wacce bat ta san lokacin a yo kaza ba,
Ba wacce ke da ganda ba koko son jiki ba,
Ba wacce bat ta damu ta yo ƙwazon fice ba,
            Ba mai yawan ƙawaye na ɓata lokaci ba.

Ba mai biye ƙawaye wajen sharholiya ba,
Ba mai ɗaukar zuga gun waɗansu ‘yan’adam ba,
Ba mai ganin waɗai ba da so na kwaikwayo ba,
Ba wacce ke da son wai a san tana da shi ba,
            Ba wacce ke gani don ta zo ta kwaikwaya ba.

Ba wacce ba ta nazari da yin tuntuntuni ba,
Ba wacce ba ta tsarin salo na rayuwa ba,
Ba wacce duk tunaninta bai wuce na yau ba,
Ba wacce ba azanci a kanta ko kaɗan ba.
Ba bogaza ba sannan ba mubazzara ba.

Ba wacce ke da son kai da so na zuciya ba,
Ba wacce ke da son rai da so na rayuwa ba,
Ba wacce ke da buri na hole duniya ba,
Ba wacce ke da cacar kuɗi da dukiya ba,
            Ba wacce tattali bai gane ta ko hanya ba.

Ba wacce ke faɗa kan ƙarya da so na rai ba,
Ba wacce ke biris da shure gaskiya ba,
Abin da duk daidai ne bai saɓa ƙa’ida ba,
Idan yawa gare shi yawan bai yo yawa ba,
Idan kaɗan ake so, bai zamto ɗan ɗiris ba.

Ba wai ina zuba ne kawai a don waƙa ba,
Ban yo zancen daɗai don in tara baituka ba,
Tabbas ar ra’ayina ban ƙara gisshiri ba,
Ban so abin wuya ba da ke wuyar samu,
            Hali kaɗai nake so, ba zan ƙi ai daɗi ba.

Ina ta kan batu af! Ban sanya basmala ba,
Astagfirullah Allah ka sa ban sau hanya ba,
Ka gyara zuciyata ka sa ba zan taɓe ba,
Da ni da duk salihhai ba mu so so na kai ba,
            Shigar da mu aljanna Ilahu, Jalla, Rabba!

Daɗo dubban salati da bai wu aƙ ƙida ba,
Ga Manzo Al-aminu da bak ka yo ya shi ba,
Da alaye sahabu dukansu ban rabe ba,
Ka sa a ran ƙiyama da su ba ma rabe ba,
            Tamat! Abu-Ubaida ban girmi kuskure ba.

Post a Comment

0 Comments