𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu alaikum. Malam, barka da yau. Dan Allah ka taimaka min da shawara da addu’a cikin gaggawa. Tun jiya wani mugun tunani da waswasi yake yawo a zuciyata yana tura ni zuwa ga zagin Allah (Subhanallahi). Ina ta ƙoƙarin kawar da tunanin amma ya ƙi tafiya. Duk lokacin da abin ya zo min, nakan ji kamar na kashe kaina saboda tsananin ɓacin rai da tashin hankali. Ni ma yanzu ba ni da tsarki da zan yi sallah na roƙi Allah. Zuciyata na dab da fashewa saboda haushin kaina da nake ji. Me ya kamata na yi?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumus salam wa
rahmatullahi wa barakatuh.
Karamar damuwa da kike ciki
ta bayyana kwarai, amma ina roƙonki
da ki kwantar da hankalinki, ki cire kowane irin tsoro ko damuwa daga
zuciyarki. Wannan tunanin da kike ji sam ba naki ba ne, ba daga gare ki yake
fitowa ba, kuma ba zai taɓa fitar da ke daga Musulunci
ko ya ruguza imaninki ba. Wannan matsala ita ce abin da malamai suke ƙira da Waswasul Qahri (wato waswasin
Shaidan na tilastawa). Lokacin da Shaidan ya gaza jefa mumini a cikin manyan
zunubai na fili, yakan dawo ta hanyar jefa masa munanan tunani a cikin gida na
aƙida domin ya firgita shi, ya ɗora
masa tsananin ƙunci, har ya kai shi
ga yanke ƙauna daga rahamar
Allah Madaukakin Sarki.
Ainihin gaskiyar lamarin ita
ce: Jin ɓacin
rai, ƙunci, da kuma tsananin ƙyamar da kike yi wa wannan tunanin har
kike jin tamkar ki mutu da ki furta shi, ita kanta wannan natsuwa da kishin
addinin babbar shaida ce ta cewa imaninki yana da ƙarfi kwarai da gaske. Idan da har kina
so ko kina da niyyar aikata wannan sabo, da ba za ki ji wannan radadin da
takaicin a cikin zuciyarki ba. Barawo ba ya fasa gidan da babu komai a ciki;
Shaidan yana damunkar wannan zuciyar ne saboda ya san tana ɗauke
da kyawawan lu'u-lu'u na imani.
Wannan matsalar ta riga ta
faru a zamanin magabata na gari. Sahabbai (Raliyallahu Anhum) sun taɓa
zuwa wajen Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) cikin tashin hankali irin
naki, suka bayyana masa cewa suna samun wasu munanan tunani a cikin zukatansu
waɗanda
suke jin tsoron ko da furta su da harshe, kuma sun gwammace a jefo su daga sama
zuwa ƙasa da su furta wannan abun.
An ruwaito daga Abu Hurairah
(Raliyallahu Anhu) ya ce:
جَاءَ
نَاسٌ مِنْ أَصْحَابِ النَّبِيِّ صَلَّى اللَّهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ فَسَأَلُوهُ:
إِنَّا نَجِدُ فِي أَنْفُسِنَا مَا يَتَعَاظَمُ أَحَدُنَا أَنْ يَتَكَلَّمَ بِهِ،
قَالَ: «وَقَدْ وَجَدْتُمُوهُ؟» قَالُوا: نَعَمْ، قَالَ: «ذَاكَ صَرِيحُ
الْإِيمَانِ»
Waɗansu
mutane daga cikin sahabban Annabi (Sallallahu Alaihi Wasallam) sun zo masa suka
tambaye shi: "Lallai mu muna samun abubuwa a cikin zukatanmu waɗanda
kowannenmu yake jin girman laifin furta su da harshensa." Sai Annabi ya
ce: "Shin har kuka same shi (wato wannan radadin da ƙyamar)?" Suka ce: "E, kwarai
kuwa." Sai ya ce: "Wannan shi ne tsantsar imani (fili wanda babu
ha'inci a ciki)." (Sahih Muslim)
Wannan hadisi yana nuna miki
fili cewa Allah ba zai kama ki da laifin duk wani tunani da yake yawo a
zuciyarki ba, muddin ba ki furta shi da harshenki ko kika aikata shi da gaɓoɓinki
ba. Karancin tsarkin jiki na al'ada (ko janaba) da kike ciki shi ma ba zai hana
ki yin zikiri ko roƙon
Allah ba. Addinin Musulunci ya amince wa mace mai al'ada ta riƙa ambaton Allah, tana karanta addu'o'i
da yin zikiri domin samun kariya daga Shaidan.
An ruwaito daga Abu Hurairah
(Raliyallahu Anhu) cewa Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya bayyana
afuwar Allah a kan waswasin zuciya:
إِنَّ
اللَّهَ تَجَاوَزَ لأُمَّتِي مَا حَدَّثَتْ بِهِ أَنْفُسَهَا، مَا لَمْ
تَتَكَلَّمْ أَوْ تَعْمَلْ
Lallai Allah ya yafewa
al'ummata abin da zukatansu suke sa sa masu (na tunani ko waswasi), muddin ba
su yi magana da harshe ko sun aikata shi ba. (Sahih al-Bukhari)
Hanyoyin da Zaki Bi Domin
Yantar da Zuciyarki:
1. Ririta Wannan Ka'ida
(Watsi da Tunanin): Duk lokacin da wannan tunanin ya zo miki, kada ki tsaya
kina gardama da shi ko neman amsa masa a cikin zuciya. Ki yi saurin nisanta
kanki daga tunanin ta hanyar shagaltar da hankalinki da wani abin daban ko
tashi daga inda kike.
2. Yayin da Tunanin ya Zo:
Yi saurin cewa:
أَعُوذُ
بِاللَّهِ مِنَ الشَّيْطَانِ الرَّجِيمِ ، آمَنْتُ بِاللَّهِ وَرُسُلِهِ
A'uzu billahi
minash-shaitanir-rajim, amantu billahi wa rusulih.
(Ina neman tsarin Allah daga
shaidan jifaffe, na yi imani da Allah da manzanninsa).
3. Du'a da Ambaton Allah: Ki
yawaita fadar waɗannan addu'o'in a kowane
lokaci domin tabbatar da natsuwar zuciya:
يَا
مُقَلِّبَ الْقُلُوبِ ثَبِّتْ قَلْبِي عَلَى دِينِكَ
Ya Muqallibal-qulub, sabbit
qalbi 'ala dinik.
(Ya Mai juyar da zukata, ka
tabbatar da zuciyata a kan addininka).
اللَّهُمَّ
إِنِّي أَعُوذُ بِكَ مِنَ الْهَمِّ وَالْحَزَنِ
Allahumma inni a'uzu bika
minal-hammi wal-hazan.
(Ya Allah lallai ni ina
neman tsarinka daga damuwa da ɓacin rai).
Kada ki kuskura ki sake yin
tunanin cutar da kanki ko kashe kanki sakamakon wannan jarabawa. Rayuwarki tana
da matukar kima a wajen Ubangiji, kuma wannan waswasi wani gajeren hadari ne
kawai da zai wuce da yardar Allah. Tunda kin san abin da ke faruwa ba daidai ba
ne kuma kina ƙi da zuciyarki, to
kin riga kin taka mataki mafi muhimmanci na samun nasara a kan Shaidan.
Wallahu Ta'ala A'alam.
SHIN WAJIBI NE MAMU SU DINGA
FAƊIN DUK ABINDA LIMAN YA FAƊA ACIKIN SALLAH?
𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamualaikum malam barka
da safiya dafatan Kai da iyalanka Kuna cikin koshin lafiya. Malam tambaya ta ita
ce shin wajibine Suma Mamu su dinga fadin duk abinda liman yafada acikin Sallah
kamar kabbara, zaman Hutu da Kuma fadin Sami allahulimanhamidah.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumussalam
warahmatullahi wabarakatuh.
Malaman fiƙihu sun tafi a kan cewa faɗin
kabbarorin tashi daga wani rukunin zuwa wani (kamar daga sujada zuwa zama ko
tashi zuwa raka'a ta biyu) sunna ce ko wajibi ga liman da mai sallah shi kaɗai,
kuma ana son mamu ya yi su a ɓoye (cikin ransa ko da ƙaramin murya) don bin liman, amma ba a ɗora
wa mamu nauyin yin su da ƙarfi
ba.
A cewar mafi yawancin
malamai da kuma limamai da littattafan fiƙhu,
fadin SAMI-ALLAHU LIMAN HAMIDAHŪ, wajibi ne ko Sunnah mai ƙarfi ga Liman da wanda yake sallah shi
kaɗai,
yayin da mamu ma ake son ya faɗa a lokacin da yake tashi
daga ruku'u kafin ya daidaita a tsaye. ba wai sai ya gama tsayawa tsaf ba kafin
ya fara faɗin zikirin ba.
Idan liman ya ce:
"SAMI'ALLAHU LIMAN HAMIDAH" yayin tashi, Sai mamun ya ce:
"RABBANĀ WA LAKAL-ḤAMD
ko ALLAHUMMA RABBANA LAKAL-HAMDU" lokacin da ya daidaita a tsaye. Wasu
malaman sun ce mamu zai haɗa biyun duka
("SAMI'ALLAHU LIMAN HAMIDAH" da "RABBANĀ WA LAKAL-ḤAMD"
JALSATUL-ISTIRAHAH: Zaman
hutu kafin a tashi zuwa raka'a ta biyu ko ta huɗu
sunna ce a wasu mazhabobin amma ba wajibi ba ne, kuma mamu yana bin liman ne a
duk abin da ya aikata, idan liman ya yi shi ma zai iya yi.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.