Jagora: Namiji kamam maza yakai
Jagora /Y/Amshi: Jikan
Shehu na tsaye,
Namiji kamam maza yakai,
Jikan Shehu na tsaye
Jagora: Mai riƙon ɗakin duniyag ga
Jagora /Y/amshi: Baya
sakewa da hwama,
Namiji kamam maza yakai,
Jikan Shehu na tsaye
Jagora: Namiji kamam maza
yakai
Jagora /Y/amshi: Jikan
Shehu na tsaye,
Namiji kamam maza yakai,
Jikan Shehu na tsaye
Jagora: Yai magana mun
amsa,
Bana ga babbas sallah
Jagora /Y/amshi: Za mu
layya da Sarkin makangara,
Namiji kamam maza yakai,
Jikan Shehu na tsaye
Jagora: Bajinin Bello yaci
birnin Gwari,
Yaci birnin Kogo,
Yaci birnin Gwari,
Yaci birnin Kogo
Jagora /Y/amshi: Barbare
duka bawan gidanku na,
Namiji kamam maza yakai,
Jikan Shehu na tsaye.
Haka dai ☝️☝️☝️☝️
Makaɗa Salihu Alasan ɗan Giye ɗan Tigari mai abin kiɗi na Rawayya ya ce suka faɗawa Sarkin Sudan na
Kwantagora na 3, Malam Ibrahim Umaru Nagwamatse lokacin da shi Jankiɗi da mahaifinsa Alasan ke
'yan amshi a ƙungiyar Kiɗa
ta kakansa wato Makaɗa
Giye ɗan Tigari mai
abin kiɗa.
Sarkin Sudan na Kwantagora Ibrahim ɗan Sarkin Sudan na Kwantagora na farko wato Malam Umaru Nagwamatse yayi sarauta har sau biyu. Lokaci na farko shi ne daga shekarar 1880 zuwa 1901 karo na biyu kuma daga 1903 zuwa rasuwarsa a shekarar 1929. Allah ya kyauta makwanci, amin.
To ya wannan lamari ya faru?
Turawan mulkin mallaka na Ingila a ƙarƙashin jagorancin Frederick Lugard sun
mamaye Kwantagora da yaƙi a ƙarshen watan Janairu na shekarar 1901 saboda abin da suka kira
rashin amincewa da mulkinsu da shi Sarkin Sudan Ibrahim ɗan Umaru Nagwamatse da jama'arsa suka yi. Su
kore su daga Kwantagora shi da jama'ar tasa ciki kuwa har da su Makaɗa Salihu Alasan Jankidi
Rawayya.
Suka zo har ƙasar Ƙaya ta
masarautar Zazzau domin kaucewa wannan iftila'i inda daga bisani Turawan su ka
kama Sarki Ibrahim suka kai shi Lokoja sai a shekarar 1903 suka sake dawowa
dashi a Kwantagora ya ci gaba da mulkinsa har zuwa 1929 da Allah SWT ya karɓi abinsa.
Daga Ƙaya su Makaɗa Salihu Alasan Jankidi
Rawayya suka koma ƙasarsu ta asali inda ya ci gaba da rayuwa har zuwa rasuwarsa a
shekarar 1973. Allah ya jaddada masa rahama, amin.
Ɗiyan wannan waƙa da muka yanko a sama
suna tattare da tarihi matuƙa. Wanzuwar wannan tun a mulkin Sarki Ibrahim (1880-1901 da
kuma 1903-1929) ya bayyana muna dogon zamani da Makaɗa Salihu Alasan Jankidi Rawayya ya ja a
rayuwarsa. A gabansa aka gwabza yaƙi da Kwantagorawa da Turawan Ingila ga
kuma irin gwagwarmayar da suka yi ta rayuwa bayan wannan mamaya ta Turawa.
Sun kira Sarkin Sudan Ibrahim da
"Namiji kamam maza yakai" domin su tunatar dashi irin famar
kakanninsa ( su Mujaddadi Shehu Usman Ɗanfodiyo da Malam Abdullahi Ɗanfodiyo
da Muhammadu Bello da Abubakar Atiku) da kuma mahaifinsa Malam Umaru Nagwamatse
suka yi wajen jaddada addinin musulunci wanda ya haifar da Daular Usmaniyya.
Domin a ciki ya na cewa "Jikan Shehu na tsaye".
"Yai magana na Garba mun
amsa" anan suna danganta Sarkin Sudan Ibrahim da yayansa/wansa Sarkin
Sudan na Kwantagora na 2 wato Abubakar ɗan
Modibbo.
Sai suka ci gaba da cewa
"Bana ga babbas sallah, zamu layya da Sarkin makangara". Kenan duka
Sarkin da ke da ƙasa musamman kusa da masarautar Kwantagora amma baya biyayya
ga Sarki Ibrahim to ya kwana da kari.
Domin ƙara fitowa da ƙarfin
mulki na Sarki Ibrahim sai suka ce masa "Bajinin Bello yaci birnin Gwari,
yaci birnin Kogo" domin su nuna yadda Sarkin Sudan na farko , mahaifin
Sarki Ibrahim wato Malam Umaru Nagwamatse ya yi fama tare dasu ya'yansa wajen
kafa masarautar Kwantagora. Suka kuma ambace shi da "Bajinin Bello... Wane
Bello kenan? Amirul muminina Muhammadu Bello ɗan
Mujaddadi Shehu Usman Ɗanfodiyo tunda yayan/wan kakansa Sarkin Musulmi Abubakar I
/Atiku mai Katuru ne.
Sai suka ƙara da wasan barkwanci
dake a tsakanin Fulani( jinsin zuriyar su Sarki Ibrahim) da Barebari/Kanuri
mutanen daular Borno.
Mahaifin Sarki Ibrahim wato Malam
Umaru Nagwamatse ne ya samar da masarautar Kwantagora.
Malam Umaru ɗan Sarkin Musulmi Abubakar
I /Abubakar Atiku mai Katuru ne da ya yi sarautar Sarkin Musulmi daga shekarar
1837- 1842.
An haifi Malam Umaru a wani ƙauye
da ake kira Gwamatse dake cikin Ƙaramar Hukumar Mulkin Wamakko ta Jihar
Sakkwato ta yau a dai dai lokacin da kakani da iyayensa ke gudanar da jihadi na
jaddada addinin musulunci a farko farkon ƙarni na 19 (1800s miladiya).
Wasu masana kuma suka ce a'a
haihuwar Malam Umaru ta faru ne a wani wuri da aka kira "Gwamatse"
dake cikin masarautar Bakura a Jihar Zamfara ta yau a lokacin da masu jihadi ke
zaman Ribaɗi (a halin
yanzu babu wannan wuri sai dai ayi kirdado/hasashe). To ko ma dai ya batun yake
Malam Umaru ɗan Sarkin
Musulmi Abubakar I /Abubakar Atiku mai Katuru ɗan
Mujaddadi Shehu Usman Ɗanfodiyo Tagammadahullah Birahamatihi ya samu alkunyarsa ta
"Nagwamatse" daga wajen /wurin da aka haife shi.
Ya fito ya doshi kudu maso
yammacin Sakkwato har sai da ya samar da masarautar Kwantagora da hedikwata a
Kwantagora ta hanyar yaƙe - yaƙe. A shekarar 1859 yayansa /wansa Sarkin Musulmi Malam Ahmadu ɗan Sarkin Musulmi Abubakar
I / Atiku mai Katuru ɗan
Mujaddadi Shehu Usman Ɗanfodiyo (yayi sarauta daga shekarar 1859 - 1866 ya umurci
Sarkin Gwandu Malam Haliru mai Kara - Kara (yayi sarauta daga shekarar
1850-1860) da yaje ya naɗa
Malam Umaru Nagwamatse sarautar Kwantagora da laƙabin "Sarkin Sudan".
Malam Umaru Nagwamatse ya kasance
Sarki har zuwa wafatinsa a shekarar 1876. Daga nan ne zuriyarsa suka ci gaba da
mulki a wannan masarauta ya zuwa yau da mai martaba Sarki Muhammadu Bara'u
Mu'azu ya kasance Sarki na 7.
Mai martaba Sarki Muhammadu ɗan Malam Bara'u ne, Malam
Bara'u ɗan Sarkin
Sudan na Kwantagora Mu'azu ne wato Sarki na 5 da yayi sarauta daga shekarar
1961-1974, shi kuma ɗan
Sarki na 3 Ibrahim ne wanda yayi mulki har sau biyu 1880 - 1901 da kuma
1903-1929, shi kuma ɗan
Sarkin Sudan na Kwantagora na farko ne wato Malam Umaru Nagwamatse da yayi
sarauta daga shekarar 1859-1876, shi kuma ɗan
Sarkin Musulmi Abubakar I /Atiku mai Katuru ne wanda yayi sarautar Sarkin
Musulmi daga 1837-1842, shi kuma ɗan
Mujaddadi Shehu Usman Ɗanfodiyo ne.
A hoton dake tare da wannan
sharhi mai alfarma Sarkin Musulmi Alh. (Dr.) Muhammad Sa'ad Abubakar CFR Mni ne
a gefen dama tare da mai martaba Sarkin Sudan na Kwantagora, Alh. Muhammad
Bara'u Mu'azu. A ɗiyan
waƙar
da aka yi amfani dasu wajen gabatar da sharhinmu ana ambatar "Shehu da
Bello" a ciki saboda bayyana alaƙar waɗannan
gidaje guda biyu wato Sakkwato da Kwantagora.
Mai alfarma Sarkin Musulmi Alh.
(Dr.) Muhammad Sa'ad Abubakar CFR Mni ɗan
Sarkin Musulmi Abubakar III, shi kuma Sarki Abubakar III(yayi sarauta daga
1938-1988) ɗan Modibbo
Usman ne, Modibbo Usman ɗan
Sarkin Musulmi Mu'azu ne wanda ya yi sarauta daga shekarar 1877-1881, shi kuma ɗan Sarkin Musulmi Muhammadu
Bello ne wanda yayi mulki daga shekarar 1817-1837, shi kuma ɗan Mujaddadi Shehu Usman Ɗanfodiyo
ne.
Kenan yaya /wa ne da ƙane
daga kaka guda ɗaya,
Mujaddadi Shehu Usman Ɗanfodiyo.
Allah SWT ya jaddada rahamarsa
zuwa ga dukkan magabatanmu ya sa mu wanye lafiya mu cika da kyau da imani
Alfarmar Sahibul Qiblataini Rasulallahi Sallallahu Alaihim Wasallam, amin ya
rabbal alamin.
Daga Taskar:
Hon. Ibrahim Muhammad (Ɗanmadamin
Birnin Magaji) Jihar Zamfara, Nijeriya.
11/08/2026

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.