𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
As-Salaam Alaikum Wa Rahmatul Laah. Mene ne hukuncin masu aljanun da suke bayar da magani?
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa Alaikumus Salaam Wa
Rahmatul Laah Wa Barakaatuh.
Mu’amala a tsakanin mutane
da aljanu abu ne da ya daɗe a tarihi, kuma yawanci ba
ya haifar wa mutanen da suka shiga cikinsa wani alheri. Domin abu ne mawuyaci
wani aljani ya yarda ya haɗa-kai ko baki ko gwiwa da
wani ɗan
Adam a kan wata buƙatarsa,
in ba shi ɗan Adam ɗin
ya bayar da wani taimako ko hanun-jari mai tsoka ga wannan aljanin ba. Wanda
kuma a ƙarshe zai janyo cutuwa ko asara ko
lalacewa ga shi kansa wannan mutumin ko danginsa ko kuma wasu daga cikin ’yan uwansa mutane. Shiyasa
malaman Sunnah suka yi tsawa a kan a nisanci irin wannan ƙullin zumuncin, domin neman a tsira da
imani.
Magani iri biyu ne: Akwai
wanda ake samun sa ta hanyar jarrabawa ko gwadawa daga wurin masana harkar
lafiya, ko dai a gargajiyance a wurin masana harkar ko kuma a zamanance a
asibitoci. Akwai kuma wanda ake samun sa ta hanyar karanta wasu Ayoyin Alƙur’ani ko wasu Addu’o’i Ingantattu, tare
da amfani da wasu saiwoyi ko ganyayyaki ko yin ƙaho,
irin yadda suka tabbata daga Annabin Rahama (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa
Sallam). Wannan irin maganin kasidin ne, kuma shi ake samu ta wurin malamai
masana addini, kuma masu Imani da tsarkin zuci da kyautata ayyuka a cikin al’umma.
Neman magani daga waɗannan
wuraren biyu ya halatta, matuƙar
dai ana tare da aƙidar
cewa: Waraka dukkanta a hanun Allaah Maɗaukakin
Sarki ta ke. Kuma matuƙar
ana yin maganin ne tare da ƙanƙan-da-kai da neman waraka daga Allaah
Mahaliccin dukkan komai. Sannan kuma matuƙar
ba a tabbatar da cewa akwai wata matsala mai cutarwa da aka cusa ko aka gauraya
a cikin wannan maganin da aka karɓo
daga wurinsu (malaman) ba.
Amfani da ganye ko itatuwa
masu tsarki da kuma turare mai daɗi
(kamar miski ko ūd) domin yin ruƙya
ko turarena muhalli halal ne, muddin an dogara ga Allah kuma an yi da
Alkur'ani. Idan an haɗa da surkukuwa, buƙatar miyagun abu, ko ambaton sunayen
aljanu, to amfani da su ya bace kuma ya haramta.
Akwai kuma waɗansu
malaman da ba irin waɗannan malaman na Allaah ba.
Su ne kamar bokaye ko masu duba ko malaman istikhaara ko yin addu’a, waɗanda
su ma ake kiran su da suna malamai. Amma kuma ayyukansu ba kyawawa abin yabo ba
ne, sakamakon abin da suke yi na yin ta’ammali da rauhanai ko aljanu mutane ɓoye.
Yawancin waɗannan suna samun maganin da suke bayarwa
ga masu zuwa wurinsu ne ta hanyoyin yardar da shaiɗanun
aljanu, kamar ta biya musu buƙatun
da suka nema daga wurinsu na ayyukan saɓo da
shirka da kafirci.
Hanya ta gari wajen maganin
aljanu ita ce Ruƙya
ta shari'a ta hanyar Alkur'ani da ingantattun addu'o'i, ba ta hanyar masu duba
da bokan da ke ikirarin amfani da aljanu ba.
A karantarwar Sahihin
Addininmu na Musulunci dai ba a yarda a tafi wurin irin waɗannan
mutanen don neman magani ko wata buƙata
irin wannan ba. Manzon Allaah (Sallal Laahu ’Alaihi
Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:
مَنْ
أَتَي عَرَّافًا فَسَأَلَهُ عَنْ شَيْءٍ لَمْ تُقْبَلْ لَهُ صَلَاةُ أَرْبَعِينَ
لَيْلَة
Duk wanda ya tafi wurin mai
duba kuma ya tambaye shi a kan wani abu, to kuwa ba za a karɓi
Sallolinsa na kwana arba’in ba!
(Muslim (5714) da Ahmad
(16638) suka fitar da shi).
Watau kenan duk wanda ya
tafi domin tambaya kawai, to ya yi asarar ladan sallolinsa guda ɗari
biyu, watau: (5x40=200)!!
Wannan kuwa ba ƙaramar asara ba ce, in da mutane suna
fahimta. Allaah ya ƙara
mana fahimta.
Sannan kuma Manzon Allaah
(Sallal Laahu ’Alaihi wa Aalihi wa Sallam) ya ce:
مَنْ
أَتَى عَرَّافًا أَوْ كَاهِنًا فَصَدَّقَهُ بِمَا يَقُولُ فَقَدْ كَفَرَ بِمَا
أُنْزِلَ عَلَى مُحَمَّدٍ
Duk wanda ya tafi wurin mai
duba ko boka kuma ya gaskata shi a kan abin da yake faɗi,
to haƙiƙa!
Ya kafirce wa abin da aka saukar wa Annabi Muhammad (Sallallahu Alaihi
Wasallam) (Ahmad da Al-Haakim ya riwaito shi, kuma As-Shaikh Al-Albaaniy ya
inganta shi a cikin Sahih Al-Jaami’:
5939).
A ƙa’idar
shari’ar musulunci kuwa duk wanda ‘ya kafirce wa abin da aka
saukar wa Annabi Muhammad (Sallal Laahu ’Alaihi
wa Aalihi wa Sallam)’
bayan kuwa yana musulmi, to ya yi ridda kenan.
Idan wannan ne hukuncin
wanda ya je wurin irin waɗannan mutanen, to ina kuma
ga su kansu mutanen?!!
Allaah ya kiyashe mu, ya
tsare mu daga hanyoyin hallaka.
Don haka, wajibi ne musulmi
a duk inda yake ya nisanci duk abin da zai janyo masa naƙasa ko tawaya a cikin addininsa da
imaninsa, balle kuma abin da zai iya lalata shi, ya ruguza shi. Allaah ya
taimake mu.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.