𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Alaikum, Malam. Wallahi, ni ne ranan muna tare da iyalina, sai ta ce min na sha maganin da zai ƙara min girman azzakari na da kuma tsayinta. Hakan ya sa ni na washe ta, kuma har na ce mata wannan zai iya saka na zarge ta, amma ta yaya ta san wannan maganar? Sai ta ce wai taji ana fada akwai maganin ne a radio. Gaskiya yanzu Malam na rasa yaya zan yi shiyasa na ce don Allah indai akwai yadda za'ayi azzakarina ta kara tsayi da girma ka taimaka min, domin ni bani da matsalan rashin karfin azzakari sai dai gaskiya azzakari na bai wuce 9 centimeter ko kuma ince tsayin ruler karami na cikin math-set. Saboda haka, don Allah, Malam akwai hanyan da zan yi azzakarina ta karu? Malam kuma wanne shawara zaka bani akan wannan maganan da ta gaya min domin har yanzu bana jin sha'awanta kaman da, thank you very much for your contribution. Malam don Allah ina bukatan amsar ka, domin nafi jin aminci tattare da maganganunka da hujjoji da kake bujirowa da su. Na gode. Allah ya ƙara maka imani.
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Wa alaikumussalam
warahmatullahi wabarakatuh.
Gaskiya ɗan'uwa Ya kamata ka
godewa Allah tunda ya baka cikakkiyar lafiya da ikon yin aure, sannan ya baka
matar da ka aura, harma kuka samu daman biyan bukatunku na sha'awa. Idan ka
duba zaka ga wasu da dama suna da lafiyar jiki, amma kuma mazakutarsu batta da
cikakkiyar lafiya.
Wasu kuma suna da cikakkiyar lafiyar amma Allah bai basu ikon yin auren ba, har
ranar mutuwarsu. Bai kamata ka ji haushin matarka saboda ta baka wannan
shawarar ba. Watakila akwai dalilin da yasa ta baka shawarar. Watakila kana da
wuƙa
mai kaifi ne, amma baka san yadda zaka yi aiki da ita ba. Don haka ya kamata
kayi tunani akan wasu halattattun hanyoyin da zaka bi domin gamsar da ita
ayayin da kuke Jima'i.
Ka fara gabatar da
wasanni, da kalamai na soyayya, da chanja position alokacin Jima'i. Duk waɗannan suna sanya
ma'aurata su samu gamsuwa da junansu. Kodayake, Allah Ya halicci maza
gwargwadon nau'in mazakutarsa kuma da hakan ne kowa zai iya biyan bukatar
jima'i ga matarsa. Allahu Ya bambamta maza wajen halittar mazakuta haka kuma Ya
bambamta mata wajen halittarsu. Saboda haka ne, bukatarsu ta bambamta ta fuskar
jima'i, inda wasu matan ke son namiji mai girman azzakari ko kuma mai tsawo da
zai cika su, ko kuma ya kai makurar farjinsu kafin su samu biyan bukata.
Masana sun ce, wasu
matan Ubangiji Ya halicce su da zurfi ko fadin farji ta yadda idan azzakarin
mutum gajere ne ko kuma ba shi da kauri to da wahala ya iya biya wa irin waɗannan mata bukata ta
fuskar jima'i. Irin waɗannan mata kan samu
gamsuwa ne kawai idan sun yi arangama da mai girman azzakari. Wannan dalili ya
sa matarka ke son ka kara girman azzakari.
Masana a wannan fanni
sun gudanar da bincike mai zurfi kuma sun samar da hanyoyi da yawan gaske da za
a iya kara kauri da tsawon azzakari, amma mun zaɓi wasu hanyoyi guda biyu dangane da
wannan makala. Mun zaɓi wadannan hanyoyi
biyu ne saboda suna da saukin haɗawa, kuma kayan haɗin na samuwa a
kowannne lokaci kuma ga su da araha. Sabosa haka kowa zai iya haɗawa a gida ba tare da
wahala ba, kuma ya kara girman azzakarinsa. Maza da yawa sun jarraba su kuma
sun samu biyan bukata.
1. Hanya Ta Farko:
Ana haɗa wannan maganin
karin kauri da tsawon azzakari ne da abubuwa biyu kacal: Su ne NAMA da kuma
ZUMA.
Yadda zaka haɗa wannan magani shi
ne; ka samu nama marar kitse ko kuma mu ce jan nama. Sannan ka tanadi zuma mai
kyau marar haɗi. Bayan ka kammala
takidar waɗannan kayan haɗin na ka, sai ka
yanka naman nan yanka-yanka gwargwadon yadda mahauta ke yanka wa masu abinci
naman sayarwa, amma zai yi kyau kar yankan ya kasance kanana sosai, sai ka soya
naman, amma ka lura da kyau kar ya kone, don gudun kar a rasa wasu sanadarai
masu muhimmanci.
Bayan ka kammala soya
naman nan sai ka zuba shi cikin ruwan zumarka da ka tanada tun da farko, sai ka
adana a mazubi mai kyau. Kullum da dare sai ka dinga cin naman nan yanka ɗaya. Da ikon Allah za
ka sha mamaki. Wannan hadi an jarraba shi kuma an samu biyan bukata, don haka
ka gwada zaka yi mana addu'ar alkhairi daga bisani, in sha Allahu. Wannan shi
ne hanya ta farko yadda ake ƙara girman azzakari a saukake.
2. Hanya Ta Biyu. Ita
ma wannan hanya ce mai sauki kwarai da gaske kuma kamar ta farkon ba ta da
wahalar haɗawa. Hanya ce da
mutum zai bi ya kara girman azzakarinsa, wato kara kauri da tsawon azzakarinsa.
Abubuwan da mutum zai tanada sun haɗa da, ALBASA da ZUMA da GARIN HABBATUS SAUDAH
da kuma GARIN FIJIL.
Yadda zaka haɗa shi ne, da farko
zaka markada ALBASAR bayan ka gyara ta, sai ka zuba ta cikin ruwan ZUMA ka
gauraya su, sannan sai ka ɗora a wuta ya dafasu, amma sama-sama, sai ka sauke.
Bayan ka sauke sai ka
zuba GARIN HABBATUS SAUDA da na FIJIL cikin haɗin can na ALBASA da ZUMA ka gauraya su
sosai, ka tabbatar sun gaurayu. Wannan haɗin za ka dinga sha babban cokali kullum da
safe kafin ka karya kumullo. In sha Allahu zaka bamu labari, idan hakan bai
samu ba, mu na fatan ka yi mana addu'a.
Mu na kira ga
ma'aurata kan kar suyi sake wajen kula da lafiyarsu musamman ta fuskar jima'i
saboda yadda ake samun korafe-korafe wajen mata game da matsalar rashin biyan
bukata daga wajen maza. Kuma masana da yawa na danganta hakan ta fuskar raunin
mazakuta. Don haka a yau mun kawo ma hanyoyi biyu, yadda za ka kara girman
azzakarinka a saukake. Allah Ya sa mu dace, Ameen.
A karshe mu na kara
kira ga mai karatu kan ya rarraba wannan makala a kafofin sada zumunta na
zamani (social media) don wasu jama'ar su amfana. Amma Kuji tsoron ALLAH, kada
ku kwafa (copy) ku goge wani abu daga ciki, koda Links ne. Ga wanda ya jarraba
kuma ya dace, mu na barar addu'a ga iyayenmu da malamanmu. Mun gode. Allah
ta'ala yasa mudace.
WALLAHU A'ALAM
Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah. Za ku iya samun shafinmu ta wannan hanyar...
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.