𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Assalamu Malam dan Allah wani abu ne yake damu na nake neman mafuta mijina matafiyi ne yana tafiya neman abinci yakan yi wata uku sannan ya zo amman kamin wata ukun nakan ji kewarsa tana damu na idan na kira sa na gaya masa sai ya ce min na yi hakuri daga wannan ba wata magana mai dadi da za ta samarmin nutsuwa nanuna masa cewa ni fa maca ce ina da bukatar kulawarsa babu wani wanda Allah ya halattamin na nemi kulawa a gurinsa in bashi ba amman har yanzu ya ki ganewa na ce ya tafi da ni ya ki kuma in ya zo ba ya dadewa dadewarsa kwana biyu wallahi malam na rasa yanda zan yi bana san fadawa cikin wani yana yi na saɓon Allah Dan Allah malam kabani shawara na gode 😭😭😭😭
HUKUNCIN MIJI YA YI TAFIYA SAMA DA WATA HUƊU (4) BA TARE DA YA DAWO ZUWA GA IYALINSA BA
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
wa'alaikumussalam. To
yar'uwa kamar yadda malamai sukace; Baya halatta miji yayi tafiya sama da wata
huɗu ba tare da ya dawo
zuwa ga iyalinsa ba, hakanan koda wani dalili na Shari'a yasa mijin yana gari
sai ya kaurace mata da nufin yi mata horo na ladabtarwa to bai halatta ya
kaurace mata sama da wata huɗu ba kamar yadda aya ta 226 ta cikin suratul Baƙara ta yi bayani:
لِّـلَّذِيۡنَ
يُؤۡلُوۡنَ مِنۡ نِّسَآٮِٕهِمۡ تَرَبُّصُ اَرۡبَعَةِ اَشۡهُرٍۚ فَاِنۡ فَآءُوۡ
فَاِنَّ اللّٰهَ غَفُوۡرٌ رَّحِيۡمٌ
Ga waɗanda suke yin
rantsuwa daga matansu akwai jinkirin wata huɗu. To, idan sun kõma, to, lalle ne Allah Mai
gafara ne, Mai jin ƙai.
Sabida haka ýar'uwa
mafi yawan malamai sun tafi akan fahimtar cewa: mata na iya hakuri da jima'i
tsawon watanni huɗu. Wannan yasa idan
miji matafiyi ne matukar baya haura wata huɗu ba tare da ya dawo ga iyalinsa ba, To
Shari'a ba ta zarginsa da danne mata hakki na ɓangaren jima'i, illah iyaka idan yana
barinsu da yunwa baya wadatar dasu da abinci ruwan sha da sauran abubuwan
rayuwa da suke bukata baya nuna kulawarsa garesu to wannan ya wuce iyakar
Shari'a.
Sabida haka baiwar
Allah tunda dai Allah ya ƙaddara miki miji mai tafiye-tafiye ne akwai bukatar ki
sanya hakuri tunda har baya haura watanni huɗu matukar dai yana ciyar daku da kula da
lafiyarku har zuwa lokacinda yake dawowa to kina iya hakuri da hakan.
Sannan ki koma zuwa
ga Allah kiyi ta rokonsa ta hanyar ambatonsa kiyi ta kai kukanki ga Allah maɗaukakin sarki Sannan
ki dinga yiwa mijin Addu'a Allah ya kawo masa wata kofar samu wacce zai dawo
mazaunin gida ya dinga harkokinsa a gida maimakon tafiye-tafiyen.
Sannan babu laifi
kina iya sanar da manyanku cewa kina bukatarsa a kusa dake in sha Allahu zasu
ja hankalinsa akan ya tafi dake kuma wannan shi ne abinda yafi alkhairi matukar
dai yana da halinda zai mallaki muhalli ko ya kama hayar muhalli a can garinda
yake neman, ko kuma ya dinga kara kwanaki idan ya dawo maimakon kwanaki biyu,
idan nan ma ba'a samu matsaya ba kuma ke kina da karfin sha'awar da bazaki iya
jure wata uku ko huɗu ba tare da miji ya
kusanceki ba, hakanan kwana biyun da yake yi idan ya dawo baya wadatar dake
kuwa akwai yiwuwar ki auka halaka to kuna iya zuwa ga alkalin muslunci in sha
Allahu zai samar muku da daidaito a tsakaninku domin yana daga manufofin aure shi
ne kaucewa aukawa zina.
Sannan a karshe ina
kira ga mazaje musamman matafiya lallai yana dakyau su dinga lura da bukatun
iyalinsu ba kuma iya abinci da sauran kayan more rayuwa ba Har da abinda ya
shafi jima'i domin suma suna da bukatar jima'in akai-akai kuma banda ku
mazajensu Babu wanda aka halattawa ya kusancesu. Idan kai kana ganin kana da
mace fiye da ɗaya to ka sani ita
miji ɗaya tal take dashi
Kuma rashin kiyaye hakkokin mata na jima'i yana kawo barazana ga rayuwarsu da
imaninsu, Sannan ku dinga nuna damuwarku akansu maimakon koda yaushe su zasu
kiraku kuma ku dinga kiransu kuna debe musu kewa kuna kwantar musu da hankali
kai babu laifi ma ku dinga yin SEX CHAT dasu domin debe musu kewa maimakon ku
dinga nuna halin ko in kula da bukatarsu gareku Amma SEX CHAT ɗin ya zama da
sharadin kai da matar ku keɓance babu wani kusa daku Sannan da sharadin chat din
bazai watsu ga wasu wadanda baku ba.
WALLAHU A'ALAM
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
WALLAHU A'ALAM.
https://t.me/TambayaDaAnsa
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.