Ticker

6/recent/ticker-posts

Matata Tana Wulakanta Ni Saboda Ina Cikin Mawuyacin Hali Na Rashin Kudi

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

As-Salaam Alaikum Wa Rahmatul Laah. Matata tana aiki kuma tana samun albashi, amma kullum wulaƙanci nake sha a hannunta domin karayar tattali da ya same ni. In dai ban kawo cefane ba, to ba ni da abinci ko wurin kwana. Ko dai kawai in sake ta ne?

MATATA TANA WULAƘANTA NI SABODA INA CIKIN MAWUYACIN HALI NA RASHIN KUƊI

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa Alaikumus Salaam Wa Rahmatul Laah Wa Barakaatuh.

Abin da kake ciki yana da matukar ciwo da tashin hankali. Ba daidai ba ne mace ta riƙa wulaƙanta mijinta saboda yana cikin mawuyacin hali na rashin kuɗi. Aure jarrabawa ce da ake buƙatar haƙuri da taimakon juna daga ɓangarorin biyu. Duk da cewa halin da kake ciki yana da zafi sosai, saki ba shine mafita ta farko ba. Dukiyar matarka nata ce, amma kuma hakkin ta ne ka ciyar da ita.

A ƙaida ko da mace tana da arziƙi, haƙƙin ciyarwa da tufatarwa da samar da mazauni da bayar da magani a lokacin rashin lafiya da sauransu makamantansu a kan mijinta ne su ke, ba a kan ta ba. Wannan shi ya bai wa namiji matsayinsa na mai kulawa da iya yin saiti ga iyalinsa har da matarsa. Allaah Ta’aala ya ce:

الرِّجَالُ قَوَّامُونَ عَلَى النِّسَاءِ بِمَا فَضَّلَ اللَّهُ بَعْضَهُمْ عَلَى بَعْضٍ وَبِمَا أَنْفَقُوا مِنْ أَمْوَالِهِمْ

Mazaje ne masu tsayuwa a kan mata domin abin da Allah ya fifita sashensu a kan sashe da shi, da kuma abin da mazan suke kashewa na dukiyoyinsu. (Surah An-Nisaa’: 34).

Don haka, idan miji ba zai iya ɗaukar nauyin iyalinsa ba, bai halatta tun farko ma ya yi aure ba. Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya ce:

«يَا مَعْشَرَ الشَّبَابِ مَنِ اسْتَطَاعَ مِنْكُمُ البَاءَةَ فَلْيَتَزَوَّجْ، وَمَنْ لَمْ يَسْتَطِعْ فَعَلَيْهِ بِالصَّوْمِ فَإِنَّهُ لَهُ وِجَاءٌ»

Ya ku taron matasa! A cikinku duk wanda yake da ikon ‘BAA’AH’ to ya yi aure, kuma duk wanda ba shi da iko sai ya kama yin azumi, domin shi kariya ne a gare shi. (Sahih Al-Bukhaariy: 5065; Sahih Muslim: 1400).

Ma’anar ‘AL-BAA’AH’ kamar yadda malamai suka nuna ita ce: Ƙarfi ko ikon saduwa da mace, ko kuma ƙarfin ɗaukar nauyin ɗawainiyar auren.

Don haka shari’a ba ta bai wa namiji daman kwanciya ya jira wai matarsa ce za ta riƙa ciyar da shi ba.

Ita kuma mace da ta samu arziƙi sama da mijinta, ya zama haƙƙi a kanta ta kula da yin sadaka da alheri ga jamaa musamman talakawa daga cikin makusantanta. Saboda maganar Allaah (Subhaanahu Wa Taaala) da ya ce:

وَفِي أَمْوَالِهِمْ حَقٌّ لِلسَّائِلِ وَالْمَحْرُوم

Kuma a cikin dukiyoyinsu akwai haƙƙi ga mai tambaya da wanda ya kame. (Surah Az-Zaariyaat: 19).

Kuma mafi girma daga cikin waɗanda suke da wannan haƙƙin samun sadakar mace akwai mijinta, saboda maganar da Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) ya gaya wa Zainab matar Abdullaah Bn Masud (Radiyal Laahu Anhumaa) cewa:

«صَدَقَ ابْنُ مَسْعُودٍ، زَوْجُكِ وَوَلَدُكِ أَحَقُّ مَنْ تَصَدَّقْتِ بِهِ عَلَيْهِمْ»

Gaskiya Ibn Mas’ud ya gaya miki: Mijinki da ’ya’yanki suka fi cancantar samun sadakar dukiyarki. (Sahih Al-Bukhaariy: 1462).

Wannan ɗin kuma shi ya fi mata lada, saboda abin da ya zo a cikin wata riwaya na hadisin da ya gabata, lokacin da su Zainab ɗin suka tambayi Annabi (Sallal Laahu Alaihi Wa Alihi Wa Sallam) a kan bayar da sadaka ga mazajen aurensu, sai ya ce:

«نَعَمْ، لَهُمَا أَجْرَانِ: أَجْرُ الْقَرَابَةِ، وَأَجْرُ الصَّدَقَةِ »

Na’am, suna da lada biyu: Ladan zumunci da ladan sadaka. (Sunan An-Nasaa’iy: 2583, kuma Al-Albaaniy ya sahhaha shi).

Don haka dai maganar ba ta kai na saki ba a tsakaninku, in sha Allahu. Kawar da kai za ka yi daga dukiyarta, ka tashi ka jajirce wurin nema daga falalar Allah. Ita kuma ta taimaka maka, ko da da sadaka ne. Allaah ya ƙara mana fahimta.

WALLAHU A'ALAM

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.

   ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam 

Post a Comment

0 Comments