Ticker

6/recent/ticker-posts

Ma'anar Sunan Ummu-Salma

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamualaikum warahamatullahi wabarakatu. Mene ne Ma'anar sunan ummusallama da asalin sunan da na mahaifinta?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikumussalam warahmatullahi wabarakatuhu

Sunan UMMU-SALMA ko UMMU-SALAMA suna ne na asalin Larabci wanda ke nufin "Mahaifiyar mai Aminci" ko kuma "Mahaifiyar wacce ke cikin kwanciyar hankali." Kalmar Ummu ko Umm (أُمّ) na nufin "Uwa" (mahaifiya), ya yin da Salma Ko Salama (سلمة) ke nufin "Zaman lafiya" ko "Aminci." A dunkule, ma'anar sunan ita ce "Mahaifiyar wanda ko wadda ke cikin aminci da zaman lafiya."

Wannan suna ya shahara matuka a tarihin Musulunci saboda shine sunan Ummu Salama (R.A), wadda ta kasance ɗaya daga cikin Matayen Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) kuma uwa ga muminai.

Asalin wannan lakabi na "Ummu Salma" ya fito ne daga sunan babban danta, wanda ta haifa daga aurenta na farko da mijinta Abu Salama (ABDULLAH BN ABD AL-ASAD).

Sunanta na asali Kafin ta auri Annabi Muhammad (Sallallahu Alaihi Wasallam), shi ne HIND BINT ABI UMAYYA ko HIND AL-MAKHZUMIYA. Kabilar ta ce Al-Makhzumiya (Banu Makhzum).

Mahaifiyarta: Sunanta 'ATIKAH BINT 'AMIR wasu suna kiran ta 'ATIKAH BINT ABDUL MUTTALIB.

Sunan mahaifinsa ABU UMAYYA IBN AL-MUGHIRA BN ABDULLAH, wanda aka fi sani da SUHAIL IBN AL-MUGHIRAH ko ZAD AR-RAKIB. Ya kasance babban mutum kuma shahararre a cikin kabilarsa ta Kuraishawa da kyauta musamman ga matafiya. An fi sanin sa da laƙabin "ZĀD AL-RĀKIB", wanda ke nufin Ma'ajin abinci na matafiya. Ana kiran sa da wannan sunan ne saboda tsananin karimcinsa, inda yake daukar nauyin duk wanda zai yi tafiya tare da shi ba tare da ya bari ya dauki wani guzuri ba. Ya kasance babban shugaba mai daraja da kima a cikin kabilar Ƙuraishawa ta garin Makkah.

Ummu Salma (R.A) ta kasance mace mai daraja, haƙuri, da cikakken hankali. Ita ce mace ta farko da ta yi hijira zuwa ƙasar Habasha tare da mijinta na farko. Bayan rasuwar Abu Salama, Annabi Muhammad (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya aure ta a shekara ta huɗu bayan Hijira.

Ummu Salma ta shahara da basira. A lokacin Yarjejeniyar Hudaibiyya, shawararta ta ceton musulmi daga rudani a lokacin da suka yi jinkirin yanka dabbobin layya bayan Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya umurce su. Ta kasance daya daga cikin matan da suka fi haddar Alqur'ani da kuma sanin hadisai, inda ta ruwaito hadisai da dama daga Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam).

Ta rayu bayan wafatin Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) na tsawon shekaru da yawa. Ta rasu a Madina tana da shekaru kusan tamanin, a shekara ta 680 (ko 683 Miladiyya), kuma an binne ta a makabartar Baqi'.

WALLAHU A'ALAM

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.

   ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam 

Post a Comment

0 Comments