𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀❓
Mutum ne yake so ya saki Matarsa,
har ma ya rubuta takarda dauke da saki uku a ciki, amma dagaba ya sai ya fasa
ba ta takardar, Shin yanzu ta saku kenan ko ba ta saku ba??
𝐀𝐌𝐒𝐀❗️
Abin da Ma'abota Ilimi sukace
dangane da wannan Mas'ala shi ne: idan Miji ya rubutawa Matarsa takardar saki,
to hukunci yana komawa ne zuwa ga niyyar sa a lokacin da yake yin rubutun, idan
dama a lokacin ya yi haka ne da niyyar saki to ko shakka babu cewa Matarsa ta
saku ko ya ba ta takardar ko bai ba ta ba, amma idan a lokacin da yake rubutun
ba niyyarsa ya saketa ba, sai dai ya yi ne kawai saboda da nufin idan nan gaba
zai sake ta basai ya sake rubutawa ba, ko kuma ya rubuta ne da nufin ya baƙanta
mata rai ko dan ya tsoratar da ita saboda ta dena aikata wani abu da take yi
maras kyau, amma bawai ya yi ne da kudurin nufin ya saketa ba, dadai wasu
abubuwa makamancin hakan, Malamai suka ce a irin wannan yana yi Matarsa tana
nan ba ta saku ba, domin Manzon Allah(ﷺ) Ya ce:
"إنما الأعمال بالنيات......"
MA'ANA:
Haƙiƙa Dukkan ayyuka (na ibada) ana
yinsu ne da niyya..........
Kuma wannan ita ce fatawar waɗannan
Malamai kamar haka: ①-Imamu
Malik ②-Imamu
Abu-Hanifa ③-Imamush-Sha'abiy
④-Imamun-Nakh'iy
⑤-Imamuz-Zuhriy
⑥-Imamush-Shafi'iy.
Da Sauran Mafi yawa daga cikin Ma'abota Ilimi, sukace shi dai rubutu hukuncinsa
kamar kinaya ce, ita kuma kinaya ba a tabbatar da saki da ita sai in da niyya,
abisa ga zancen da yafi inganci, amma inda zai fito fili ƙarara ya furta da
bakinsa ya ce na sakeki to ko shakka babu anan Matarsa tasaku.
Danhaka kenan idan Miji ya rubutawa
Matarsa takardar saki mai ɗauke da lafazin da ya ɗauki Ma'anar saki a fili,
kuma ya rubuta hakan da niyyar ya saketa ɗin shikenan Matarsa ta saku, amma
idan saki biyu ne ya rubuta ko kuma saki uku magana mafi inganci za a ɗauke shi
ne amatsayin saki ɗaya kawai, duk da cewa Mazhabin MALIKIYYA sun tafi ne a kan
cewa idan mutum ya saki mace saki uku a lokaci ɗaya to kawai ta saku, amma
magana mafi inganci za a ɗauke shi ne amatsayin saki ɗaya kamar yadda Malamai
da yawa suka yi bayani a kan haka.
шαʟʟαнυ-тα'αʟα α'αʟαмυ
Mυѕтαρнα Uѕмαи
08032531505
Ga Masu Buƙatar Shiga Wannan Group
Zaku iya bi ta Links ɗin mu...
ƘARIN BAYANI
HUKUNCIN RUBUTA TAKARDAR SAKI BA TARE
DA BAYAR DA ITA BA
Tambaya
Assalamu Alaikum. Malam, mene ne hukuncin mijin da ya zauna
ya rubuta wa matarsa takardar saki (har saki uku), amma bayan ya gama rubutun
sai ya fasa ba ta takardar, ya adana ta ko ya yaga. Shin aurensu ya rushe ko
yana nan daram tunda bai ba ta takardar ba?
Amsa
Wa'alaikumus Salám wa Rahmatullāh. Wannan mas'ala tana komawa
ne ga Niyya, domin rubutu a wurin mafi yawan malamai (kamar yadda aka ambata
daga Mazhabar Malikiya, Shafi'iyya, da Hanafiyya) ana ɗaukarsa ne a matsayin
Kinaya (nuni). Shi kuma saki na nuni ba ya aukuwa sai da niyya.
1. Matsayin Rubutu Da Alaqarsa Da Niyya
Idan miji ya rubuta saki, aka tambaye shi "Me kake
nufi?" Idan ya ce: "Na rubuta ne da niyyar sakin ta," to saki ya
auku ko da takardar ba ta isa hannun matar ba. Amma idan ya ce: "Na rubuta
ne kawai don in gwada alkalami," ko "don in tsoratar da ita amma ba
na nufin saki," to aurensu yana nan.
Hujja daga Hadisi:
عَنْ عُمَرَ بْنِ الْخَطَّابِ رَضِيَ
اللهُ عَنْهُ قَالَ: سَمِعْتُ رَسُولَ اللهِ صَلَّى اللهُ عَلَيْهِ وَسَلَّمَ
يَقُولُ: «إِنَّمَا الْأَعْمَالُ بِالنِّيَّاتِ، وَإِنَّمَا لِكُلِّ امْرِئٍ مَا
نَوَى»
Fassarar Hausa: Daga Umar ɗan Khattab (R.A) ya ce: Na ji
Manzon Allah (S.A.W) yana cewa: "Haƙiƙa ayyuka suna kasancewa ne tare da
niyya, kuma kowane mutum yana da abin da ya yi niyya." (Sahihul Bukhari:
1).
Sakin da yake aukuwa ba tare da niyya ba shi ne wanda aka
furta shi Sarihi (a sarari) da baki, kamar mutum ya ce "Na sake ki."
Amma rubutu, tunda kalami ne na shiru, yana buƙatar ƙudiri na zuciya.
2. Matsayin Saki Uku A Lokaci Guda
Idan har niyyar sakin ta tabbata, to takardar da aka rubuta
saki uku a cikinta, mafi ingancin magana (wadda Ibn Taimiyyah da Ibnul Qayyim
suka rinjayar, kuma akwai hujjoji a kanta) ita ce: Saki ɗaya ne ya auku. Ko da
mutum zai ce "Na sake ki saki dubu" a kalma guda, saki ɗaya ne a
shari'ance.
Hujja daga Hadisi (Sahihu Muslim):
عَنِ ابْنِ عَبَّاسٍ رَضِيَ اللهُ
عَنْهُمَا قَالَ: «كَانَ الطَّلَاقُ عَلَى عَهْدِ رَسُولِ اللهِ صَلَّى اللهُ
عَلَيْهِ وَسَلَّمَ وَأَبِي بَكْرٍ، وَسَدْرًا مِنْ خِلَافَةِ عُمَرَ، طَلَاقُ
الثَّلَاثِ وَاحِدَةً»
Fassarar Hausa: Daga Ibn Abbas (R.A) ya ce: "Sakin uku
(da aka yi a lokaci guda) ya kasance ana ɗaukar sa a matsayin saki ɗaya a
zamanin Manzon Allah (S.A.W), da zamanin Abubakar, da kuma farkon khalifancin
Umar." (Sahihu Muslim: 1472).
3. Shawara Ga Ma'aurata
Yana da kyau miji ya kiyaye wasa da kalaman saki ko rubuta
su, domin saki babban al'amari ne da Allah Ya sanya shi a matsayin mafita ta
ƙarshe, ba abin wasa ko tsoratarwa ba. Idan mutum ya rubuta saki da niyyar
gaske, to ya zama dole ya sanar da matar kuma ta fara iddah, domin idan ya ɓoye
mata ya ci gaba da saduwa da ita, ya kusa faɗawa cikin zina ba tare da ya sani
ba.
Kammalawa
1. Idan ya rubuta ba tare da niyyar saki ba, aure yana nan.
2. Idan ya rubuta da niyyar saki, saki ya auku ko da bai ba
ta takardar ba.
3. Idan saki uku ya rubuta a lokaci guda, saki ɗaya ne a mafi
ingancin magana.
Allah ne mafi sani.
𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇
https://chat.whatsapp.com/BXjuXb1WxX99NV3OsXPnLV
𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
𝐓𝐄𝐋𝐄𝐆𝐑𝐀𝐌👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ
**************************
Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

0 Comments
ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.
HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.