Ingausar Yarbawa Da Hausawa A Garin Gusau, Jihar Zamfara (4)

    Kundin Binciken Neman Digirin Farko (B.A Hausa) Wanda Aka Gabatar A Sashen Harsuna Da Al’adu, Jami’ar Tarayya Gusau.

    Ingausar Yarbawa Da Hausawa A Garin Gusau, Jihar Zamfara (4)

    NA

    ADAMU SANI

    Zamfara Gusau

    BABI NA UKU

    GUSAU TA SAMBO

    3.0 SHIMFIÆŠA

    Wannan babi zai yi magana ne a kan garin Gusau, dangane da tarihin kafuwar garin, yanayin garin, mazaunan farko na garin, da tattalin arzikin mutanen garin, addininsu da kuma zuwan Yarbawa garin da yadda mu’amularsu ta kasance, da kuma yadda harshen Hausa da al’adunsa suka yi naso ga rayuwar Yarbawan garin Gusau.

     

    3.1 TAƘAITACCEN TARIHIN GUSAU

    A can da, É“angaren da Gusau take yanzu ya zauna ne a Æ™arÆ™ashin mulkin daular Katsina ta Gabas wanda ubandawakin Katsina yake zaune a birnin ‘Yandoto yana kula da garuruwan da ke Katsina ta yamma. A wajen Æ™arni na goma sha bakwai (17) zuwa na sha takwas garin ‘Yandoton ya zama birni babba wanda mutane daga wurare daban-daban suke zuwa É—aukan karatu da kuma harkokin kasuwanci a cikinsa. Don haka, garin ya Æ™unshi manyan malamai da É—alibai da sauran mutane masu zuwa É—aukan karatu ko kuma bayar da shi. Sai ‘Yandoto ta zama jami’a inda mutane suke haÉ—uwa don Æ™arawa juna ilimi.

     

    Alhaji Mustapha (Mahaifin Alhaji Umaru) da malam Abdulrahaman (Mahaifin mal. Ashafa) Fulani ne waÉ—anda suka zo ‘Yandoton suka zauna tare da dukkan iyalansu da nufin jiran bayyanar Shehu Usman da suka sami labarinsa tun da daÉ—ewa. WaÉ—annan Fulani sun sanya hulÉ—ar auratayya tsakanin junansu bayan kasancewarsu ‘yan’uwa makusanta. Ta hanyar aure ce aka haÉ—a Aminatu ‘Yar Alhaji Umaru aure da mal. Ashafa, sai suka sami haihuwar malam Muhammad Sambo.

     

    A wajen shekara ta (1774 – 5) Shaihu Usmanu ya fara karantarwa da wa’azi a Degal inda aka samu mutane da yawa suka É—inga zuwa É—aukar karatu a wajensa. Daga cikinsu akwai Alhaji Umaru da jikansa Malam Muhammad Sambo É—an Ashafa. Tun lokacin da Alhaji Umaru da Malam Muhammad Sambo da Sauran jama’arsu suka nuna goyon baya da yarda ga wa’azin Shaihu Usmanu, sai mutanen ‘Yandoto, musamman haÉ“e suka hana su zaman garin.

     

    Saboda tsanantawa sai Malam Muhammad Sambo ya yi hijira daga garin na ‘Yandoto zuwa wani wuri gab da gulbin Sakkwato ya kafa birnin. Wannan ita ce hijira ta farko da malam Muhammad Sambo É—an Ashafa ya yi da jama’arsa a wajen (1799). Amma a wancan lokacin ba a samu zama sosai ba saboda yawan hare-hare wanda yake ba su da Æ™arfin karewa, amma sai da suka shekara bakwai a wajen watau daga (1799- 1806).

     

    A shekara ta (1806) M. Shahu Usmanu, ya tura É—ansa Shaihu Muhammad Bello don ya yi munazara (tattaunawa ta ilimi) da mutanen ‘Yandoto domin a tabbatar da mai gaskiya. Amma sai mutanen na ‘Yandoto suka Æ™i karÉ“ar shawarar, wanda ya kawo daidaituwar ra’ayi a yaÆ™i ‘Yandoto, inda aka cinye ta shekara ta (1806).

     

    Bayan cinye ‘Yandoto, sai Shaihu Muhammad Bello da Umurnin Shaihu Usmanu ya raba Daular Katsina zuwa É“angaren yamma da na gabas. Aka ba malam Muhammad Sambo izinin jihadin garuruwan da ke Katsina ta yamma watau Katsina Al-Gharbi ko Katsinan kaka. Malam Umaru Dallaje kuwa Katsina ta gabas. Daga nan sai Malam Muhamamd Sambo É—an Ashafa ya kafa daula Æ™arama ta jihadin Musulunci wanda take kula da wasu garuruwan da suke nahiyar Katsina ta yamma wadda a Æ™arshe Gusau ta zama matattara.

     

    Da aka cinye ‘Yandoto sai malam Muhammad Sambo ya mayar da ceÉ—iya ta Æ™asar Tsafe sansanin yaÆ™insa daga (1806 – 1811). A shekara ta (1811) ya sake komawa Birnin Gusau har zuwa shekara 1818 lokacin da suka ji labarin zuwan yaÆ™in Banaga É—an Bature Sarkin Zamfaran Morai, sai suka tashi zuwa BunguÉ—u suka shekara biyu daga (1818 – 1820). Sai kuma suka koma kamani a shekara ta (1820 – 1822). Daga nan M. Muhammad Sambo da Jama’arsa suka kafa garin Wonaka a shekara ta 1822. Allah ya yi wa Malam Muhammadu Sambo ÆŠan Ashafa rasuwa a nan Wonaka a shekara ta (1827). Sai Sarkin Musulmi Muhammad Bello ya naÉ—a babban É—anshi Mal. Sambo Sarkin Katsinan Yamma watau M. AbdulÆ™adiri, ya shekara talatin da uku a Wonaka (1827 -1860). Sai Sarkin Katsina na MaraÉ—i da Sarkin Gobir na Tsibiri suka yi niyyar su kawo yaÆ™i a nan Wonaka, don haka suka fita zuwa Birnin Rawayya. A Rawayya saboda wasu matsaloli Sarkin Katsinan Yamma AbdulÆ™adir tare da jama’arsa suka yi shawarar su koma tsohon wurinsu na Gusau. Da sannu- sannu suka dawo Gusau a zama na biyu. A shekara ta (1862) a zamanin Sarkin Musulmi Amadu É—an Atiku.

     

    A lokacin Sarkin Katsinan Gusau M. AbdulÆ™adir ta sami ganuwa da kuma samun cikakken tsarin zama irin na garuruwa. A zamaninsa ne ma Sarkin MaraÉ—i ÆŠan Baskore (1953 – 73) da Sarkin yaÆ™insa Kaura Hasau suka kawo yaÆ™i Gusau, amma Allah ya ba Gusau nasara kansu, suka kashe wasu, wasu kuma suka gudu sannan aka kama bayi har 300.

     

    Gusau ta sami bunÆ™asa ne da shahara lokacin da ta kai tana iya kare kanta daga dukkan hare-hare da yaÆ™e-yaÆ™e, da miyagun namun daji da sauransu, sun sami wannan Æ™arfi ne saboda samun isassun kayan yaÆ™i da mayaÆ™a, da dakaru, sai kuma amincewar wasu mutane baÆ™i waÉ—anda suka taimaka wa Mal. Muhammad Sambo wajen jihadin Musulunci tun kafin cinye ‘Yandoto da kuma waÉ—anda aka taso da su daga Rawayya. Sannan ta samu bunÆ™asa ta shigowar wasu mutane daga garuruwa daban-daban, tun can da har kuwa yanzu, daga cikin baÆ™in Æ™abilun da ke zaune a garin Gusau. Sun haÉ—a da: Yarbawa, Igbo, Nufawa, Tibi Dakkarawa da sauransu.

    A taÆ™aice garin Gusau gari ne da aka kafa shi tun a shekarar 1811, kimanin shekara 208, da suka gabata bayan tasowar garin daga ‘yandoto a shekarar 1806. Garin Gusau yana É—aya daga cikin manyan garuruwan tsohuwar jihar Sakkwato kafin daga bisani ya zama babban birnin Jahar Zamfara a shekarar 1996.

     

    Garin Gusau yana da masarauta É—aya mai babban Sarki, akwai kuma iyayen Æ™asa goma sha huÉ—u (14), ‘yan majalisar Sarki goma sha takwas, sarautun fada kuma akwai kimanin É—ari da huÉ—u (104).

     

    Masarautar Gusau ta yi Sarakuna mabambanta zamuna daban-daban waÉ—anda suka haÉ—a da:

    ·         Sambo ÆŠan Ashafa                          1806 – 1827

    ·         Malam AbdulÆ™adir                          1827 – 1867

    ·         Malam Muhammad Modibbo                   1867 – 1876

    ·         Malam Muhammad Tuburi                       1876 – 1887

    ·         Malam Muhammadu Gida                         1887 – 1900

    ·         Malam Muhammad Murtala                     1900 – 1916

    ·         Malam Muhamamd Dangida                    1916 – 1917

    ·         Umaru Malam                                              1917 – 1929

    ·         Muhammad Mai Akwai                             1929 – 1945

    ·         Usman S/Kudun ÆŠansadau                      1943 – 1945

    ·         Malam Ibrahim                                            1945 – 1948

    ·         Malam Muhammad                                     1948 – 1951

    ·         Alhaji Sulaiman S/Kudun Gusau             1951 – 1984

    ·         Alhaji Muhammad Kabir ÆŠanbaba           1984 – 2015

    ·         Alhaji Ibrahim Bello                        2015 – zuwa yanzu

     

    3.2 YANAYIN GARIN GUSAU

    Yanayin ƙasar Gusau, ƙasa ce shinfiɗaɗɗiya wadda take kan tudu, ba ta da yawan kwararra da duwarwatsu, sannan tana da yanayin ƙasa mai laka da fadama da kuma mai danba, akwai kuma inda take da jar ƙasa da wadda ba a rasa ba mai jigawa. Manyan gulabe guda biyu sune suka ratsa cikin ƙasar Gusau, akwai gulbin Sakkwato wanda ya ratso ta Ɗandume ya biyo kwaren Ganuwa da Rijiya da Gidan Fakkan da Gidan Malamai ya faɗo Gusau ya wuce zuwa Bunguɗu da Maru har ya isa Sakkwato, sai kuma gulbin Gagare watau na Wonaka wanda ya koma har ƙaura Namoda.

     

    Gusau A.R, (2014), ya nuna cewa garin Gusau yana bisa kan titin Sakkwato zuwa Zariya, Kilomita 179 tsakaninsa da Zariya, 210, kuma tsakaninsa da Sakkwato. Daga gabas ta yi iyaka da Æ™asar Katsina, da Tsafe, daga yamma kuma ta yi iyaka da Æ™asar BunguÉ—u. Ta yi iyaka da Æ™asar Ƙaura – Namoda ta wajen arewa, daga kudu kuwa ta yi iyaka da Æ™asar ÆŠansadau da kuma Tsafe.

    Haka kuma garin Gusau yana da yanayin shekara guda biyu watau yanayin rani, wanda hunturu da bazara kan kutso da kuma yanayin damina da kan zo da ruwan sama.

     

    3.3 MAZAUNAN FARKO NA GARIN GUSAU

    Gusau S.M, da Gusau B.M (1984) sun bayyana cewa asalin mahaifin malam Muhamamd Sambo ÆŠan’ashafa da Kakansa duka Fulani ne, waÉ—anda kuma su ne suka kafa garin Gusau, bayan yawace-yawacen da birnin ya yi sanadiyar hare-hare da ya addabe su. A shekarar (1862) zamanin Sarkin Katsinan Gusau AbdulÆ™adir Gusau ta sami cikakken tsaro kuma ta ci gaba da zama inda take a yau ba su yi wata Æ™aura ba har ila yau.

     

    Duk da cewa Fulani ne suka assasa ta, amma kuma saboda shigowar baÆ™i daga maÆ™wabtansa sai ya zamana ya rikiÉ—a ya koma garin Hausawa, Hausa ta zama ita ce babban harshen sadarwa tsakanin mazauna garin. Domin duk da’awar da Malam Sambo ÆŠan’ashafa ya yi a farfajiyar Katsina ta yamma da harshen Hausa ya yi ta domin shi ne harshen da mutanen wurin ke amfani da shi.

     

    3.4 TATTALIN ARZIKIN MUTANEN GARIN GUSAU

    Tattalin arziki shi ne hanyar da mutane kan bi domin samu sauƙin gudanar da rayuwarsu dangane da abin da ya shafi saye da sayarwa da sauransu.

    Gusau ta sami shahara sosai ta wajen tattalin arzikin Æ™asa tun kafin zuwan Turawan mulkin mallaka noma da wasu ‘yan Æ™ananan sana’o’i ne abin yi, amma saboda yawan matafiya a wancan lokaci aka samu ci gaban sana’o’i kamar É—inki, da saÆ™a, da jima, da Æ™ira da sauransu. Daga cikin waÉ—annan sana’o’i ne aka sami masana’antu da masu gudanar da wasu sana’o’i na gargajiya kamar maÆ™era, da marina da mahauta, da sauransu.

     

    Akwai manyan hanyoyin kasuwanci guda huÉ—u da suke É“ullowa ta kowace kusurwa waÉ—anda ‘yan kasuwa da fatake da sauran matafiya suke shigowa Gusau da kayayyakin kasuwanci iri-iri ko fita da su daga Gusau, kamar shanu, hatsi, gero, tufafi da takin zamani da sauransu.

     

    A yanzu Gusau ta bunÆ™asa Æ™warai da gaske ta fannin tattalin arziki domin ta sami manyan ‘yan kasuwa waÉ—anda suka duÆ™ufa ainun wajen kafa kamfanonin kasuwanci da masana’antu na zamani da suka haÉ—a da: Gidajen ruwan leda, gidajen biredi, da kamfanonin casar shinkafa, da kamfanin gyaran audugu (kaÉ—a), bugu da Æ™ari akwai makarantun zamani na kuÉ—i ko masu zaman kansu, haka kuma akwai bankuna (wajen ajiya da aika saÆ™onnin kuÉ—i) da kuma gidajen kiwon kaji da samar da Æ™wai da sauransu.

     

    3.5 ADDININ MUTANEN GARIN GUSAU

    Idan aka ce addini shi ne hanyar bauta wadda mutum ya yi imani da ita, ta hanyar bin umurni da hani na wani abin bauta, (Gobir 2017).

    Addinin musulunci shi ne addinin da asalin mutanen Gusau ke bi, domin wanda ya kafa garin malam Muhammad Sambo ÆŠan’ashafa a shekarar (1811) musulmi ne, haka mahaifinsa da kakansa duk suna cikin almajiran Shaihu Usman ÆŠanfodiyo. Sun karantar da addinin musulunci kuma sun yi jihadi domin yaÉ—uwar addinin.

     

    A zamanin Sambo Gusau ta zama babbar cibiya ta koyar da addinin musulunci da kuma wasu dokoki nasa. Mutane suna zuwa daga kusa da ma wurare masu nisa domin É—aukar karatu. An gina makarantu da masallatai domin ci gaban addinin a garin Gusau.

     

    Bayan wannan a shekara (1903) lokacin da Turawan mishan da na mulkin mallaka suka shigo ƙasar Hausa, an sami wata hanyar bauta ta addinin masihiyya (Kirstanci) a garin Gusau wanda a kan samu mabiya wannan addinin har ila yau.

    Bugu da Æ™ari sanadiyar Æ™aurace-Æ™aurace daga maÆ™wabtan garin Gusau an samu mabiya addinin gargajiya a garin Gusau kamar ‘yan bori da sauransu.

    Garin Gusau ya yi suna game da addinin musulunci, idan kuma aka É—auki mazaunansa masu riÆ™o da addinin, domin a nan ne tsohon gwamnan farar hula na Zamfara Alhaji Ahamd Sani Yariman Bakura ya Æ™addamar da shari’ar musulunci a Jihar ta Zamfara inda Najeriya da Æ™asashen duniya sunan garin da jihar ya yi fice.

    3.6 ZUWAN YARBAWA GARIN GUSAU

    Hijira daga wani wuri zuwa wani wuri ba baƙon abu ba ne a tarihin duniya baki ɗayanta. Kafin zuwan Yarbawa a garin Gusau an samu kwararowar baƙi daga maƙwabtan garin Gusau kamar; Kwatarkwashi, Bunguɗu, Wonaka, da sauransu.

     

    A farkon Æ™arni na ashirin ne aka samu kwararowar baÆ™i a garin Gusau, waÉ—anda suka bambanta ta fuskar harshe da kuma al’adun mutanen garin Gusau daga cikin Æ™abilun akwai; Nufawa, Yarbawa, da Igbo, da Tibi da Igala da sauransu.

     

    A shekarar (1920) ne Yarabawa suka fara zuwa Gusau a matsayin ‘yan Kasuwa, inda daga bisani suka zama mazauna garin. BaÆ™in sun zo ne daga Æ™asashen Yarbawa mabambanta da suka haÉ—a da; Ilorin, Abeokuta, Ibadan, da sauransu. BaÆ™in sukan kawo kayan Sayarwa a Gusau kamar goro, da gishiri da Kanwa da ayaba, da sauransu. Haka kuma idan za su koma su kan sayi kaya daga nan zuwa Æ™asarsu kamar fatar dabbobi, albasa, tumatur, tattasai da sauransu.

     

    A shekarar (1927) an ƙara samun kwararrowar baƙin Yarbawa zuwa garin Gusau ta Sanadiyar aikin layin dogo (Hanyar Jirgin ƙasa) wanda ya ƙara haɓaka tattalin arzikin garin domin samun sauƙin sufurin mutane da kaya.

    Baya ga wannan a shekarar (1960) an samu ƙarin kwararowar baƙin Yarbawa garin Gusau sanadiyar buɗe kamfanin masaƙa da aka yi wanda ya bai wa Yarbawa da dama gurabun ayuka, kuma suka cakuɗu da Hausawan da ke aiki a kamfanin da ma wajen kamfanin a unguwannin Gusau daban-daban.

     

    Haka kuma akwai Yarbawan da suka zo Gusau ta sanadiyar ziyarar ‘yan uwansu da abokai da suke nan Gusau, daga nan suma suka maÆ™ale suka zama mazauna Gusau (Tosin 2019).

     

    Baya ga wannan akwai Yarbawan da ke zaune a garin Gusau waɗanda, suka zo ta sanadiyar aikin yi wa ƙasa hidima (NYSC), sai suka kasa komawa ƙasashensu domin rayuwa da yanayin garin Gusau ya yi musu.

     

    Sai kuma É—aiÉ—aiku waÉ—anda aiki ya kawo su kama tun daga aikin kamfanoni lokacin turawan mulkin mallaka kamar kamfanin (Royar Niger Company) da aiki irin na Gwamnatin tarayya wanda yakan kai ma’aikata sassan Najeriya daban-daban. A taÆ™aice waÉ—annan su ne dalilan da suka kawo zuwan Yarbawa a garin Gusau.

    3.7 MU’AMULAR YARBAWA DA HAUSAWAN GUSAU 

    An samu mu’amula ta cuÉ—eni-in- cuÉ—e-ka tsakanin al’ummar Yarbawa da kuma Hausawa mazauna garin Gusau ta É“angarrori da dama, wanda kuma wannan hulÉ—a ta taimaki dukkan É“angarorin biyu, domin ci gaban rayuwarsu, daga cikin É“angarorin da mu’amular ta taka rawa akwai;

    Babban abin da ya kawo mu’amula ta kusa tsakanin Yarbawa da Hausawan Gusau ita ce, ta harshe wato koyon harshen Hausa da su baÆ™in Yarbawan ke Æ™oÆ™arin yi tsakaninsu da Hausawa, kuma suka iya inda wasu daga cikinsu suka zama kamar Hausawa ta fuskar amfani da harshen Hausa.

     

    Bayan wannan kuma, ‘ya’ya Yarbawa suna Æ™ulla alaÆ™a ta abokantaka da ‘ya’yan Hausawan da suke zaune da su. Wanda yanayin wurin zama kan haddasa dangantaka tsakanin Hausawa da Yarbawan da ke zaune sabon Gari, Birnin Ruwa, Bakin Kasuwa, da Sauransu.

     

    Haka kuma an samu mu’amula ta Æ™ut-da-Æ™ut tsakanin Yarbawan Gusau da Hausawa. Wannan mu’amula ta shafi lamarin mulki wanda Yarbawa suna da nasu tsarin mulki, amma duk da haka, suna Æ™arÆ™ashin Sarkin Katsinan Gusau domin su Æ™ungiya ce ta wani yare wadda ke zaune a Gusau, dole sai an samu tattaunawa tsakaninsu da masarautar Gusau.

     

    HulÉ—ar cinikayya kamar yadda aka faÉ—a a baya, Yarbawan Farko da suka zo Gusau sun zo ne ta sanadiyar kasuwanci, wanda yake mataki na musaya tsakanin Hausawa da Yarbawa. Daga cikin abubuwan da Yarbawa kan sayarwa Hausawan Gusau akwai; Kanwa, gishiri, goro da sauransu, Yarbawa kan sayi albasa, tattasai, dabbobi, fatar dabbobi da sauransu. Saboda haka kasuwanci ya zama wata muhimmiyar mu’amular Hausawa da Yarbawan garin Gusau.

     

    Neman ilimi ya kawo cuÉ—anya tsakanin Hausawa da Yarbawan garin Gusau, domin makarantun garin Gusau na ilimin zamani da na addini duk a cakuÉ—e ake tsakanin ‘ya’yan Hausawa da na Yarbawa. Misali Makarnatar Ansaruddini, sabon Garin Gusau, makarnatar Yarbawa ce, amma É—aliban da ke karatu a sashen Islamiyya a iya yin raba daidai ko kuma Hausawa su fi yawa. Da wannan za mu iya cewa neman ilimi ya kawo cuÉ—anya tsakanin Hausawa da Yarbawan garin Gusau.

     

    Bugu da Æ™ari aikin gwamnati ya taka muhimmiyar rawa wajen mu’amular Hausawan Gusau da Yarbawan garin waje É—aya domin gudanar da ayukan ci gaban Æ™asa. Yarbawa sun taka muhimmiyar rawa a fagen ilimin garin Gusau domin akan same su a makarantu daban-daban na garin Gusau, sai kuma É—aiÉ—aiku a wasu ma’aikatun waÉ—anda ba makarantu ba kuma har yanzu ana samunsu kuma ana mu’amula da su.

     

    Sana’o’i sun taimaka wajen hulÉ—ar Hausawa da Yarbawan Gusau, kama daga sana’o’in hannu kamar kanikanci (gyran mota da mashin), sana’ar kafinta, É—inkin tela da sauransu. WaÉ—annan sana’o’in hannu sun taimaka wajen hulÉ—ar Æ™abilun biyu a garin Gusau. Haka kuma ana kai ‘ya’yan Hausawa wajen Yarbawa koyon sana’a kafin ‘yan gida su yawaita ga sana’o’in. WaÉ—annan da makarantansu ne suka kawo mu’amuloli mabanbanta tsakanin Hausawan Gusau da abokan zama Yarbawan garin Gusau.

     

    3.8 TASIRIN HARSHEN HAUSA DA AL’ADUNSA GA YARBAWAN GUSAU

    Harshen Hausa da al’adun Hausawa sun yi naso ga Yarbawan garin Gusau ta sanadiyar abubuwa daban-daban da suka haÉ—a da:

     

    Harshen Hausa ya yi matuÆ™ar tasiri ga al’ummar Yarbawan garin Gusau inda wasun su da dama sun kusa komawa Hausawa ta fuskar harshe domin Hausa ta yi tasirin da tana so ta rinjayi harsunan uwa, domin a kan iya samun wasu kalmomi waÉ—anda ba ya iya amfani da su cikin magana ko da, da Yarbanci yake magana sai dai ya yi amfani da na Hausa.

     

    Ta fuskar sutura, kuwa Yarbawan Gusau sun gauraya da Hausawan Gusau domin yanzu suna saka tufafi irin na Hausawa da suka Æ™unshi babbar riga da hula Æ™ube, ko mu- haÉ—u-banki. Haka kuma sukan sanya dogayen kaftanai irin na al’adar mutanen garin Gusau. Ta fuskar zamananci kuwa, matasan Yarbawa ba kasafai suke saka tufafin al’adarsu ba, sai dai can ba a rasa ba.

     

    Babbar al’adar da ta nashe Yarbawan Gusau ita ce auratayya wadda kan faru tsakanin Æ™abilun biyu, an samu auratayya da dama wanda Bahaushe kan auri Bayaraba, idan sun sami ‘ya’ya sai ka ga harshen Hausa ya rinjaya ga yaran da aka haifa.

     

    Haka kuma ta fuskar al’adun da suka shafi abinci Yarbawan Gusau sun tasirantu da abincin gargajiya na Hausawa suna amfani da su domin buÆ™atun yau da kullum, abinci irin su; Tuwon dawa, dambu, É—anwake, da fura da sauransu.

     

    3.9 NAÆŠEWA

    Daga Æ™arshe wannan babi ya yo tsokaci game da kafuwar garin Gusau a (1811), bayan cinye daular ‘Yandoto a (1806), da kuma irin sarakunan da suka muki garin har zuwa yau. Haka kuma an yi tsokaci a kan yanayin garin Gusau da tattalin arzikinsa. Da hanyar bautar mutanen garin, da kuma bayyanar baÆ™in haure a garin musmaman Yarbawa, da mu’amularsu da ‘yan gida da kuma irin tasirantuwa da harshe da al’adun mutanen Gusau da Yarbawan suka yi, sai kuma naÉ—ewa da ta zo daga Æ™arshe.

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.