Kundin Binciken Neman Digirin Farko (B.A Hausa) Wanda Aka Gabatar A Sashen Harsuna Da Al’adu, Jami’ar Tarayya Gusau.
Ingausar
Yarbawa Da Hausawa A Garin
Gusau, Jihar Zamfara (4)
NA
ADAMU SANI
BABI NA UKU
GUSAU TA
SAMBO
3.0 SHIMFIƊA
Wannan babi
zai yi magana ne a kan garin Gusau, dangane da tarihin kafuwar garin, yanayin
garin, mazaunan farko na garin, da tattalin arzikin mutanen garin, addininsu da
kuma zuwan Yarbawa garin da yadda mu’amularsu ta kasance, da kuma yadda harshen
Hausa da al’adunsa suka yi naso ga rayuwar Yarbawan garin Gusau.
3.1 TAƘAITACCEN
TARIHIN GUSAU
A can da, ɓangaren da
Gusau take yanzu ya zauna ne a ƙarƙashin
mulkin daular Katsina ta Gabas wanda ubandawakin Katsina yake zaune a birnin
‘Yandoto yana kula da garuruwan da ke Katsina ta yamma. A wajen ƙarni
na goma sha bakwai (17) zuwa na sha takwas garin ‘Yandoton ya zama birni babba
wanda mutane daga wurare daban-daban suke zuwa ɗaukan karatu
da kuma harkokin kasuwanci a cikinsa. Don haka, garin ya ƙunshi manyan
malamai da ɗalibai da
sauran mutane masu zuwa ɗaukan karatu ko kuma bayar da shi. Sai
‘Yandoto ta zama jami’a inda mutane suke haɗuwa don ƙarawa
juna ilimi.
Alhaji
Mustapha (Mahaifin Alhaji Umaru) da malam Abdulrahaman (Mahaifin mal. Ashafa)
Fulani ne waɗanda suka zo
‘Yandoton suka zauna tare da dukkan iyalansu da nufin jiran bayyanar Shehu
Usman da suka sami labarinsa tun da daɗewa. Waɗannan Fulani
sun sanya hulɗar auratayya
tsakanin junansu bayan kasancewarsu ‘yan’uwa makusanta. Ta hanyar aure ce aka
haɗa Aminatu
‘Yar Alhaji Umaru aure da mal. Ashafa, sai suka sami haihuwar malam Muhammad
Sambo.
A wajen
shekara ta (1774 – 5) Shaihu Usmanu ya fara karantarwa da wa’azi a Degal inda
aka samu mutane da yawa suka ɗinga zuwa ɗaukar karatu
a wajensa. Daga cikinsu akwai Alhaji Umaru da jikansa Malam Muhammad Sambo ɗan Ashafa.
Tun lokacin da Alhaji Umaru da Malam Muhammad Sambo da Sauran jama’arsu suka
nuna goyon baya da yarda ga wa’azin Shaihu Usmanu, sai mutanen ‘Yandoto,
musamman haɓe suka hana
su zaman garin.
Saboda
tsanantawa sai Malam Muhammad Sambo ya yi hijira daga garin na ‘Yandoto zuwa
wani wuri gab da gulbin Sakkwato ya kafa birnin. Wannan ita ce hijira ta farko
da malam Muhammad Sambo ɗan Ashafa ya yi da jama’arsa a wajen
(1799). Amma a wancan lokacin ba a samu zama sosai ba saboda yawan hare-hare
wanda yake ba su da ƙarfin karewa, amma
sai da suka shekara bakwai a wajen watau daga (1799- 1806).
A shekara ta
(1806) M. Shahu Usmanu, ya tura ɗansa Shaihu Muhammad Bello don ya yi
munazara (tattaunawa ta ilimi) da mutanen ‘Yandoto domin a tabbatar da mai
gaskiya. Amma sai mutanen na ‘Yandoto suka ƙi karɓar shawarar,
wanda ya kawo daidaituwar ra’ayi a yaƙi ‘Yandoto,
inda aka cinye ta shekara ta (1806).
Bayan cinye
‘Yandoto, sai Shaihu Muhammad Bello da Umurnin Shaihu Usmanu ya raba Daular
Katsina zuwa ɓangaren yamma
da na gabas. Aka ba malam Muhammad Sambo izinin jihadin garuruwan da ke Katsina
ta yamma watau Katsina Al-Gharbi ko Katsinan kaka. Malam Umaru Dallaje kuwa
Katsina ta gabas. Daga nan sai Malam Muhamamd Sambo ɗan Ashafa ya
kafa daula ƙarama ta jihadin Musulunci wanda take kula da
wasu garuruwan da suke nahiyar Katsina ta yamma wadda a ƙarshe Gusau
ta zama matattara.
Da aka cinye
‘Yandoto sai malam Muhammad Sambo ya mayar da ceɗiya ta ƙasar
Tsafe sansanin yaƙinsa daga (1806 – 1811). A shekara ta (1811)
ya sake komawa Birnin Gusau har zuwa shekara 1818 lokacin da suka ji labarin
zuwan yaƙin Banaga ɗan Bature
Sarkin Zamfaran Morai, sai suka tashi zuwa Bunguɗu suka
shekara biyu daga (1818 – 1820). Sai kuma suka koma kamani a shekara ta (1820 –
1822). Daga nan M. Muhammad Sambo da Jama’arsa suka kafa garin Wonaka a shekara
ta 1822. Allah ya yi wa Malam Muhammadu Sambo Ɗan Ashafa
rasuwa a nan Wonaka a shekara ta (1827). Sai Sarkin Musulmi Muhammad Bello ya
naɗa babban ɗanshi Mal.
Sambo Sarkin Katsinan Yamma watau M. Abdulƙadiri, ya
shekara talatin da uku a Wonaka (1827 -1860). Sai Sarkin Katsina na Maraɗi da Sarkin
Gobir na Tsibiri suka yi niyyar su kawo yaƙi a nan
Wonaka, don haka suka fita zuwa Birnin Rawayya. A Rawayya saboda wasu matsaloli
Sarkin Katsinan Yamma Abdulƙadir tare da
jama’arsa suka yi shawarar su koma tsohon wurinsu na Gusau. Da sannu- sannu
suka dawo Gusau a zama na biyu. A shekara ta (1862) a zamanin Sarkin Musulmi
Amadu ɗan Atiku.
A lokacin
Sarkin Katsinan Gusau M. Abdulƙadir ta sami
ganuwa da kuma samun cikakken tsarin zama irin na garuruwa. A zamaninsa ne ma
Sarkin Maraɗi Ɗan
Baskore (1953 – 73) da Sarkin yaƙinsa Kaura
Hasau suka kawo yaƙi Gusau, amma Allah
ya ba Gusau nasara kansu, suka kashe wasu, wasu kuma suka gudu sannan aka kama
bayi har 300.
Gusau ta sami
bunƙasa ne da shahara lokacin da ta kai tana iya
kare kanta daga dukkan hare-hare da yaƙe-yaƙe,
da miyagun namun daji da sauransu, sun sami wannan ƙarfi ne
saboda samun isassun kayan yaƙi da mayaƙa,
da dakaru, sai kuma amincewar wasu mutane baƙi waɗanda suka
taimaka wa Mal. Muhammad Sambo wajen jihadin Musulunci tun kafin cinye ‘Yandoto
da kuma waɗanda aka taso
da su daga Rawayya. Sannan ta samu bunƙasa ta
shigowar wasu mutane daga garuruwa daban-daban, tun can da har kuwa yanzu, daga
cikin baƙin ƙabilun da ke
zaune a garin Gusau. Sun haɗa da: Yarbawa, Igbo, Nufawa, Tibi
Dakkarawa da sauransu.
A taƙaice
garin Gusau gari ne da aka kafa shi tun a shekarar 1811, kimanin shekara 208,
da suka gabata bayan tasowar garin daga ‘yandoto a shekarar 1806. Garin Gusau
yana ɗaya daga
cikin manyan garuruwan tsohuwar jihar Sakkwato kafin daga bisani ya zama babban
birnin Jahar Zamfara a shekarar 1996.
Garin Gusau
yana da masarauta ɗaya mai babban Sarki, akwai kuma iyayen ƙasa
goma sha huɗu (14), ‘yan
majalisar Sarki goma sha takwas, sarautun fada kuma akwai kimanin ɗari da huɗu (104).
Masarautar
Gusau ta yi Sarakuna mabambanta zamuna daban-daban waɗanda suka haɗa da:
·
Sambo Ɗan Ashafa 1806 – 1827
·
Malam Abdulƙadir 1827 – 1867
·
Malam Muhammad Modibbo 1867 – 1876
·
Malam Muhammad Tuburi 1876 – 1887
·
Malam Muhammadu Gida 1887 – 1900
·
Malam Muhammad Murtala 1900 – 1916
·
Malam Muhamamd Dangida 1916 – 1917
·
Umaru Malam 1917
– 1929
·
Muhammad Mai Akwai 1929 – 1945
·
Usman S/Kudun Ɗansadau 1943 – 1945
·
Malam Ibrahim 1945 – 1948
·
Malam Muhammad 1948 – 1951
·
Alhaji Sulaiman S/Kudun Gusau 1951 – 1984
·
Alhaji Muhammad Kabir Ɗanbaba 1984 – 2015
·
Alhaji Ibrahim Bello 2015 – zuwa yanzu
3.2 YANAYIN
GARIN GUSAU
Yanayin ƙasar
Gusau, ƙasa ce shinfiɗaɗɗiya wadda
take kan tudu, ba ta da yawan kwararra da duwarwatsu, sannan tana da yanayin ƙasa
mai laka da fadama da kuma mai danba, akwai kuma inda take da jar ƙasa
da wadda ba a rasa ba mai jigawa. Manyan gulabe guda biyu sune suka ratsa cikin
ƙasar Gusau, akwai gulbin Sakkwato wanda ya
ratso ta Ɗandume ya biyo kwaren Ganuwa da Rijiya da
Gidan Fakkan da Gidan Malamai ya faɗo Gusau ya wuce zuwa Bunguɗu da Maru har
ya isa Sakkwato, sai kuma gulbin Gagare watau na Wonaka wanda ya koma har ƙaura
Namoda.
Gusau A.R,
(2014), ya nuna cewa garin Gusau yana bisa kan titin Sakkwato zuwa Zariya,
Kilomita 179 tsakaninsa da Zariya, 210, kuma tsakaninsa da Sakkwato. Daga gabas
ta yi iyaka da ƙasar Katsina, da Tsafe, daga yamma kuma ta yi
iyaka da ƙasar Bunguɗu. Ta yi
iyaka da ƙasar Ƙaura – Namoda
ta wajen arewa, daga kudu kuwa ta yi iyaka da ƙasar Ɗansadau
da kuma Tsafe.
Haka kuma
garin Gusau yana da yanayin shekara guda biyu watau yanayin rani, wanda hunturu
da bazara kan kutso da kuma yanayin damina da kan zo da ruwan sama.
3.3 MAZAUNAN
FARKO NA GARIN GUSAU
Gusau S.M, da
Gusau B.M (1984) sun bayyana cewa asalin mahaifin malam Muhamamd Sambo Ɗan’ashafa
da Kakansa duka Fulani ne, waɗanda kuma su ne suka kafa garin Gusau,
bayan yawace-yawacen da birnin ya yi sanadiyar hare-hare da ya addabe su. A
shekarar (1862) zamanin Sarkin Katsinan Gusau Abdulƙadir Gusau ta
sami cikakken tsaro kuma ta ci gaba da zama inda take a yau ba su yi wata ƙaura
ba har ila yau.
Duk da cewa
Fulani ne suka assasa ta, amma kuma saboda shigowar baƙi daga maƙwabtansa
sai ya zamana ya rikiɗa ya koma garin Hausawa, Hausa ta zama ita ce
babban harshen sadarwa tsakanin mazauna garin. Domin duk da’awar da Malam Sambo
Ɗan’ashafa ya yi a farfajiyar Katsina ta yamma
da harshen Hausa ya yi ta domin shi ne harshen da mutanen wurin ke amfani da
shi.
3.4 TATTALIN
ARZIKIN MUTANEN GARIN GUSAU
Tattalin
arziki shi ne hanyar da mutane kan bi domin samu sauƙin gudanar da
rayuwarsu dangane da abin da ya shafi saye da sayarwa da sauransu.
Gusau ta sami
shahara sosai ta wajen tattalin arzikin ƙasa tun kafin
zuwan Turawan mulkin mallaka noma da wasu ‘yan ƙananan
sana’o’i ne abin yi, amma saboda yawan matafiya a wancan lokaci aka samu ci
gaban sana’o’i kamar ɗinki, da saƙa, da jima,
da ƙira da sauransu. Daga cikin waɗannan
sana’o’i ne aka sami masana’antu da masu gudanar da wasu sana’o’i na gargajiya
kamar maƙera, da marina da mahauta, da sauransu.
Akwai manyan
hanyoyin kasuwanci guda huɗu da suke ɓullowa ta
kowace kusurwa waɗanda ‘yan
kasuwa da fatake da sauran matafiya suke shigowa Gusau da kayayyakin kasuwanci
iri-iri ko fita da su daga Gusau, kamar shanu, hatsi, gero, tufafi da takin
zamani da sauransu.
A yanzu Gusau
ta bunƙasa ƙwarai da
gaske ta fannin tattalin arziki domin ta sami manyan ‘yan kasuwa waɗanda suka duƙufa
ainun wajen kafa kamfanonin kasuwanci da masana’antu na zamani da suka haɗa da: Gidajen
ruwan leda, gidajen biredi, da kamfanonin casar shinkafa, da kamfanin gyaran
audugu (kaɗa), bugu da ƙari
akwai makarantun zamani na kuɗi ko masu zaman kansu, haka kuma akwai
bankuna (wajen ajiya da aika saƙonnin kuɗi) da kuma
gidajen kiwon kaji da samar da ƙwai da
sauransu.
3.5 ADDININ
MUTANEN GARIN GUSAU
Idan aka ce
addini shi ne hanyar bauta wadda mutum ya yi imani da ita, ta hanyar bin umurni
da hani na wani abin bauta, (Gobir 2017).
Addinin musulunci
shi ne addinin da asalin mutanen Gusau ke bi, domin wanda ya kafa garin malam
Muhammad Sambo Ɗan’ashafa a shekarar (1811) musulmi ne, haka
mahaifinsa da kakansa duk suna cikin almajiran Shaihu Usman Ɗanfodiyo.
Sun karantar da addinin musulunci kuma sun yi jihadi domin yaɗuwar addinin.
A zamanin
Sambo Gusau ta zama babbar cibiya ta koyar da addinin musulunci da kuma wasu
dokoki nasa. Mutane suna zuwa daga kusa da ma wurare masu nisa domin ɗaukar karatu.
An gina makarantu da masallatai domin ci gaban addinin a garin Gusau.
Bayan wannan
a shekara (1903) lokacin da Turawan mishan da na mulkin mallaka suka shigo ƙasar
Hausa, an sami wata hanyar bauta ta addinin masihiyya (Kirstanci) a garin Gusau
wanda a kan samu mabiya wannan addinin har ila yau.
Bugu da ƙari
sanadiyar ƙaurace-ƙaurace daga
maƙwabtan garin Gusau an samu mabiya addinin
gargajiya a garin Gusau kamar ‘yan bori da sauransu.
Garin Gusau
ya yi suna game da addinin musulunci, idan kuma aka ɗauki
mazaunansa masu riƙo da addinin, domin a
nan ne tsohon gwamnan farar hula na Zamfara Alhaji Ahamd Sani Yariman Bakura ya
ƙaddamar da shari’ar musulunci a Jihar ta
Zamfara inda Najeriya da ƙasashen
duniya sunan garin da jihar ya yi fice.
3.6 ZUWAN
YARBAWA GARIN GUSAU
Hijira daga
wani wuri zuwa wani wuri ba baƙon abu ba ne
a tarihin duniya baki ɗayanta. Kafin zuwan Yarbawa a garin Gusau an
samu kwararowar baƙi daga maƙwabtan
garin Gusau kamar; Kwatarkwashi, Bunguɗu, Wonaka, da
sauransu.
A farkon ƙarni
na ashirin ne aka samu kwararowar baƙi a garin Gusau,
waɗanda suka
bambanta ta fuskar harshe da kuma al’adun mutanen garin Gusau daga cikin ƙabilun
akwai; Nufawa, Yarbawa, da Igbo, da Tibi da Igala da sauransu.
A shekarar
(1920) ne Yarabawa suka fara zuwa Gusau a matsayin ‘yan Kasuwa, inda daga
bisani suka zama mazauna garin. Baƙin sun zo ne
daga ƙasashen Yarbawa mabambanta da suka haɗa da; Ilorin,
Abeokuta, Ibadan, da sauransu. Baƙin sukan kawo
kayan Sayarwa a Gusau kamar goro, da gishiri da Kanwa da ayaba, da sauransu.
Haka kuma idan za su koma su kan sayi kaya daga nan zuwa ƙasarsu kamar
fatar dabbobi, albasa, tumatur, tattasai da sauransu.
A shekarar
(1927) an ƙara samun kwararrowar baƙin Yarbawa
zuwa garin Gusau ta Sanadiyar aikin layin dogo (Hanyar Jirgin ƙasa)
wanda ya ƙara haɓaka tattalin arzikin
garin domin samun sauƙin sufurin mutane da
kaya.
Baya ga
wannan a shekarar (1960) an samu ƙarin
kwararowar baƙin Yarbawa garin Gusau sanadiyar buɗe kamfanin
masaƙa da aka yi wanda ya bai wa Yarbawa da dama
gurabun ayuka, kuma suka cakuɗu da Hausawan da ke aiki a kamfanin da
ma wajen kamfanin a unguwannin Gusau daban-daban.
Haka kuma
akwai Yarbawan da suka zo Gusau ta sanadiyar ziyarar ‘yan uwansu da abokai da
suke nan Gusau, daga nan suma suka maƙale suka zama
mazauna Gusau (Tosin 2019).
Baya ga
wannan akwai Yarbawan da ke zaune a garin Gusau waɗanda, suka zo
ta sanadiyar aikin yi wa ƙasa hidima
(NYSC), sai suka kasa komawa ƙasashensu
domin rayuwa da yanayin garin Gusau ya yi musu.
Sai kuma ɗaiɗaiku waɗanda aiki ya
kawo su kama tun daga aikin kamfanoni lokacin turawan mulkin mallaka kamar
kamfanin (Royar Niger Company) da aiki irin na Gwamnatin tarayya wanda yakan
kai ma’aikata sassan Najeriya daban-daban. A taƙaice waɗannan su ne
dalilan da suka kawo zuwan Yarbawa a garin Gusau.
3.7 MU’AMULAR
YARBAWA DA HAUSAWAN GUSAU
An samu
mu’amula ta cuɗeni-in- cuɗe-ka tsakanin
al’ummar Yarbawa da kuma Hausawa mazauna garin Gusau ta ɓangarrori da dama,
wanda kuma wannan hulɗa ta taimaki dukkan ɓangarorin
biyu, domin ci gaban rayuwarsu, daga cikin ɓangarorin da
mu’amular ta taka rawa akwai;
Babban abin
da ya kawo mu’amula ta kusa tsakanin Yarbawa da Hausawan Gusau ita ce, ta
harshe wato koyon harshen Hausa da su baƙin Yarbawan
ke ƙoƙarin yi
tsakaninsu da Hausawa, kuma suka iya inda wasu daga cikinsu suka zama kamar
Hausawa ta fuskar amfani da harshen Hausa.
Bayan wannan
kuma, ‘ya’ya Yarbawa suna ƙulla alaƙa
ta abokantaka da ‘ya’yan Hausawan da suke zaune da su. Wanda yanayin wurin zama
kan haddasa dangantaka tsakanin Hausawa da Yarbawan da ke zaune sabon Gari,
Birnin Ruwa, Bakin Kasuwa, da Sauransu.
Haka kuma an
samu mu’amula ta ƙut-da-ƙut tsakanin
Yarbawan Gusau da Hausawa. Wannan mu’amula ta shafi lamarin mulki wanda Yarbawa
suna da nasu tsarin mulki, amma duk da haka, suna ƙarƙashin
Sarkin Katsinan Gusau domin su ƙungiya ce ta
wani yare wadda ke zaune a Gusau, dole sai an samu tattaunawa tsakaninsu da
masarautar Gusau.
Hulɗar cinikayya
kamar yadda aka faɗa a baya, Yarbawan Farko da suka zo Gusau sun
zo ne ta sanadiyar kasuwanci, wanda yake mataki na musaya tsakanin Hausawa da
Yarbawa. Daga cikin abubuwan da Yarbawa kan sayarwa Hausawan Gusau akwai;
Kanwa, gishiri, goro da sauransu, Yarbawa kan sayi albasa, tattasai, dabbobi,
fatar dabbobi da sauransu. Saboda haka kasuwanci ya zama wata muhimmiyar
mu’amular Hausawa da Yarbawan garin Gusau.
Neman ilimi
ya kawo cuɗanya tsakanin
Hausawa da Yarbawan garin Gusau, domin makarantun garin Gusau na ilimin zamani
da na addini duk a cakuɗe ake tsakanin ‘ya’yan Hausawa da na Yarbawa.
Misali Makarnatar Ansaruddini, sabon Garin Gusau, makarnatar Yarbawa ce, amma ɗaliban da ke
karatu a sashen Islamiyya a iya yin raba daidai ko kuma Hausawa su fi yawa. Da
wannan za mu iya cewa neman ilimi ya kawo cuɗanya tsakanin
Hausawa da Yarbawan garin Gusau.
Bugu da ƙari
aikin gwamnati ya taka muhimmiyar rawa wajen mu’amular Hausawan Gusau da
Yarbawan garin waje ɗaya domin gudanar da ayukan ci gaban ƙasa.
Yarbawa sun taka muhimmiyar rawa a fagen ilimin garin Gusau domin akan same su
a makarantu daban-daban na garin Gusau, sai kuma ɗaiɗaiku a wasu
ma’aikatun waɗanda ba
makarantu ba kuma har yanzu ana samunsu kuma ana mu’amula da su.
Sana’o’i sun
taimaka wajen hulɗar Hausawa da
Yarbawan Gusau, kama daga sana’o’in hannu kamar kanikanci (gyran mota da
mashin), sana’ar kafinta, ɗinkin tela da sauransu. Waɗannan
sana’o’in hannu sun taimaka wajen hulɗar ƙabilun
biyu a garin Gusau. Haka kuma ana kai ‘ya’yan Hausawa wajen Yarbawa koyon sana’a
kafin ‘yan gida su yawaita ga sana’o’in. Waɗannan da
makarantansu ne suka kawo mu’amuloli mabanbanta tsakanin Hausawan Gusau da
abokan zama Yarbawan garin Gusau.
3.8 TASIRIN
HARSHEN HAUSA DA AL’ADUNSA GA YARBAWAN GUSAU
Harshen Hausa
da al’adun Hausawa sun yi naso ga Yarbawan garin Gusau ta sanadiyar abubuwa
daban-daban da suka haɗa da:
Harshen Hausa
ya yi matuƙar tasiri ga al’ummar Yarbawan garin Gusau
inda wasun su da dama sun kusa komawa Hausawa ta fuskar harshe domin Hausa ta
yi tasirin da tana so ta rinjayi harsunan uwa, domin a kan iya samun wasu
kalmomi waɗanda ba ya
iya amfani da su cikin magana ko da, da Yarbanci yake magana sai dai ya yi
amfani da na Hausa.
Ta fuskar
sutura, kuwa Yarbawan Gusau sun gauraya da Hausawan Gusau domin yanzu suna saka
tufafi irin na Hausawa da suka ƙunshi babbar
riga da hula ƙube, ko mu- haɗu-banki. Haka
kuma sukan sanya dogayen kaftanai irin na al’adar mutanen garin Gusau. Ta fuskar
zamananci kuwa, matasan Yarbawa ba kasafai suke saka tufafin al’adarsu ba, sai
dai can ba a rasa ba.
Babbar
al’adar da ta nashe Yarbawan Gusau ita ce auratayya wadda kan faru tsakanin ƙabilun
biyu, an samu auratayya da dama wanda Bahaushe kan auri Bayaraba, idan sun sami
‘ya’ya sai ka ga harshen Hausa ya rinjaya ga yaran da aka haifa.
Haka kuma ta
fuskar al’adun da suka shafi abinci Yarbawan Gusau sun tasirantu da abincin
gargajiya na Hausawa suna amfani da su domin buƙatun yau da
kullum, abinci irin su; Tuwon dawa, dambu, ɗanwake, da
fura da sauransu.
3.9 NAƊEWA
Daga ƙarshe
wannan babi ya yo tsokaci game da kafuwar garin Gusau a (1811), bayan cinye
daular ‘Yandoto a (1806), da kuma irin sarakunan da suka muki garin har zuwa
yau. Haka kuma an yi tsokaci a kan yanayin garin Gusau da tattalin arzikinsa.
Da hanyar bautar mutanen garin, da kuma bayyanar baƙin haure a
garin musmaman Yarbawa, da mu’amularsu da ‘yan gida da kuma irin tasirantuwa da
harshe da al’adun mutanen Gusau da Yarbawan suka yi, sai kuma naɗewa da ta zo
daga ƙarshe.
0 Comments
Rubuta tsokaci.