Karin Harshen Zamfarci (Musamman A Garin Gusau) (3)

    Kundin Binciken Neman Digirin Farko (B.A Hausa) Wanda Aka Gabatar A Sashen Harsuna Da Al’adu Jami’ar Tarayya Gusau

    Karin Harshen Zamfarci (Musamman A Garin Gusau) (3)

    NA

    BASHIRU HARUNA

     

    Karin harshe

    BABI NA BIYU

    ƘASAR HAUSA

    2.0 SHIMFIÆŠA

    A babin da ya gabata an yi ƙoƙarin kawo bitar ayyukan da suka gabata, da gudummuwar aikin ga ilimi da dalilin yin bincike da tsarin gabatar da aikin. A wannan babi na biyu za mu yi bayanin tarihin ƙasar Hausa da taƙaitaccen tarihin Zamfara da tarihin garin Gusau daha ƙarshe naɗewa.

    2.1 TAƘAITACCEN TARIHIN ƘASAR HAUSA

                Ƙasar Hausa tana da girma Æ™warai da gaske ta miÆ™e daga Arewa zuwa Kudu, Æ™asar Hausa ta fara daga Azbin zuwa kusurwar arewa maso gabas ta tsaunukan Jos. Daga nan kuma sai a buga ta yi arewa maso yamma har  ta dangane da wani Æ™ato kwari na Gulbin Kebbi. Daga wannan wuri sai ta karakata ta nufi arewa maso gabas har Azbin”. Wannan zagaye shi ya nuna iyakokin Æ™asar Hausa a gabas da yamma da kudu da arewa. Sannan kuma Æ™asar Hausa da waÉ—annan iyakokin suka yi iyaka da ita har zuwa yau, wannan Æ™asar watau Æ™asar Hausa ita ce mazaunin Hausawa. Duk da haka waÉ—annan abubuwan sun faru waÉ—anda suka kawo Æ™asar Hausa. Ire – iren abubuwan sun haÉ—a da nashe waÉ—ansu al’umma waÉ—anda asalinsu ba Hausawa ba ne, kamar mutanen Songhai. Tarihin ya nuna cewa akwai wani yunÆ™uri da Hausawa suka yi na neman mallake maÆ™wabtansu waÉ—anda ba Hausawa ba a yunÆ™urin sun ci nasarar mallake Æ™abilu kamar Kambari da AciPawa da Dakarkari da kuma Anya da Gwari”.(Amfani, 1980).

                Hausa harshe ne na Hausawa, su kuwa Hausawa wasu al’umma ne da suke zaune a Æ™asar Hausa a cikin yankin Afrika ta yamma. Kuma su Hausawa mutane ne baÆ™aÆ™e, wato baÆ™ar fata ba farar fata ba, kodayake a kan samu ‘yan farare jefi – jefi a cikinsu musamman in aka samu auratayya da wata Æ™abila tsakaninsu. Hausawa mutane ne masu tsananin riÆ™on al’adunsu na gargajiya musamman wajen tufafi da abinci, al’amurran sana’a ko kasuwanci ko neman ilimi dasauransu.

                Hausawa mutane ne waÉ—anda suka É—auki noma babbar sana’a, haka kuma suna da waÉ—ansu sana’o’i na al’adu kamar su Æ™ira da jima da fawa da dukancida wanzanci da sauransu. A yanzu yawancin Hausawa musulmai ne, saboda haka mafi yawancin al’adunsu waÉ—anda suka shafi aure da haihuwa da mutuwa duk sun dogara ne ga yadda addini ya shar’anta. Sai dai É—an abinda baka rasa ba na al’adun gargajiya musamman a wajen Maguzawa.

    2.2 TAƘAITACCEN TARIHIN ƘASAR ZAMFARA

                Tarihi ya nuna cewa masarautar Zamfara tana da babban matsayi tun kafuwar daular Usmaniyya. Masarautar Zamfara ta fara daga Æ™arni na goma sha biyar. Masarautar Zamfara na É—aya daga cikin tsofaffin masarautun Ƙasar Hausa. Daga Æ™arni na goma sha shida masarautar Zamfara ta fara tsarin irin na sarakuna. Daga nan aka fara kiran sarakunanta da sunan “Sarkin Zamfara”. Wurin da aka fara kafawa a matsayin babban birinin Zamfara, shi ne Dutsi. Sarakuna maza da mata sun yi zamani a Dutsi. Ganin irin hare – haren da ake kawo masu a wannan wuri na Dutsi, sai aka É—auke babban birnin daga Dutsi aka mayar da shi Kuyanbana. Dalilin wannan sauyi shi ne Kuyanbana wuri ne mai duhun itatuwa. Kodayake yanzu ba kowa a Kuyanbana sai kufai, wurin yana nan kusa da garin ÆŠansadau a Æ™aramar hukumar mulkin Maru.

                Daga lokacin da aka dawo kuyanbana, sai zaman lafiya da ci gaba suka wanzu a masarautar Zamfara. Daga bisani, hare – hare a kan wannan birni na Kuyanbana sun sa Zamfarawa sun sake babban birni wato Birnin Zamfara wanda yanzu yake a Æ™aramar hukumar Isa ta jihar Sakkwato. Bugu da Æ™ari, an zauna zaman wuccin gadi a wurare da dama, kamar su Kiyawa da Morai da Sabon Gari. A Æ™arshe an yi mazauni na din – din – dim a Anka a cikin Æ™arni na goma sha tara, (1815).

    Asalin kalmar ‘Zamfara’ta samo asali ne daga É—iyar Sarkin Gobir mai suna ‘Fara’. Yadda labarin ya zo mana shi ne, wannan É—iyar sarkin, an tilasta mata ta auri wanda ba ta so. Ganin haka sai ta gudu, ta bar gida, ta shiga dokar daji. A wannan dajin ta É“ata, daga baya ne wasu mafarauta suka tsince ta suka je da ita gidansu a unguwar maza da ke  kusa da Æ™auyen Dutsi.

                Sakamakon jin daÉ—in zaman da ‘Fara’ ta yi da waÉ—annan mutane, ya sanya ta yanke shawarar ta auri Æ™araminsu. A cikin wannan halin ne ta samu juna biyu da wannan mijin nata mafarauci. Ganin haka ya sa mafarautan suka yanke shawarar kai ta don ta yi goyon ciki wajen mahaifinta Sarkin Gobir a gida.

                Bayan watanni kaÉ—an sai ta haifu, wannan al’amari  ya farantawa mahaifinta (wato Sarkin Gobir). Sai ya yi masu godiya, sannan ya yi masu kyautar yankin unguwar ‘maza’.

                Daga nan ne aka fara kiran yankin da suna ‘Æ™asar mazanfara’. Daga Æ™arshe aka maida shi ‘Birnin Zamfara’. Da tafiya tayi nisasai aka yarda kalmar birni daga sunan, don haka sai kawai aka ce ‘Zamfara’. Wannan shi ne asalin kalmar Zamfara.

                A lokacin mulkin sarkin Zamfara Abarshi ne, mujaddadi Shehu Usmanu ÆŠanfodiyo ya shigo Æ™asar Zamfara domin yaÉ—a addinin Musulunci, ana cikin daula sai Nasara (Bature)ya zo, ya kafa mulkin mallaka a Nijeriya ta Arewa, ya kasa arewa lardi – lardi.

                Zamfara ta yi iyaka da jihar Sakkwato ta Arewa, jihar Katsina kuwa, ta yi iyaka ne ta gabas, sannan ta yi iyaka da jihar Kaduna ta É“angaren kudu, daga Æ™arshe, ta yi iyaka da jihar Neja da jihar Kebbi a É“angaren yamma.

                A É“angaren faÉ—in Æ™asa kuwa, jihar Zamfara ta mamaye marabba’in kilomita dubu talatin da takwas da É—ari huÉ—u da arba’in da takwas (38,448). Kamar yadda sauran jihohin arewacin Nijeriya suke, itama jihar Zamfara tana da yanayi huÉ—u a shekara. Akwai yanayin ‘rani’ dana ‘hunturu’ wanda ke farawa a watan Nuwamba zuwa watan Mayu. Sai kuma yanayin ‘kaka’ da na ‘damuna’ da kan fara daga watan Yuli zuwa watan Oktoba.

                Jihar Zamfara tana da manyan gulabe guda huÉ—u. Gulaben su ne, gulbin Bunsuru da gulbin Ka, da gulbin Zamfara da gulbin Gagare. Haka kuma akwai manyan tafkuna guda biyu. Tafkunan su ne, tafkin gulbin Kakate da tafkin Bakura Natu. Baya ga waÉ—annan manyan tafkuna, akwai Æ™ananan tafkuna irin su tafkin Saru, a cikin Æ™aramar hukumar Gummi, da tafkin Jena a Æ™aramar hukumar Zurmi. A Æ™aramar hukuma ta Maradun akwai babban dam da ake kira dam É—in Bakalori.

     


     

    TASWIRAR JIHAT ZAMFARA


     

    2.3 TAƘAITACCEN TARIHIN GUSAU

                Kamar yadda bayani ya gabata an kafa garin Gusau ne shekara ta (1811) bayan tasowa daga ‘Yandoto a shekara ta (1806) (Gusau, S. M 1984). Garin Gusau na É—aya daga cikin manyan garuruwan jahar Sakkwato, kafin daga bisani ya zama baban birnin jihar Zamfara a shekara ta (1996), kamar yadda kundin bayanin tarihin Æ™asa na (1920) ya nuna.Garin yana bisa kan titin Sakkwato zuwa Zariya  ne, kilomita 179 tsakaninsa da Zariya, kilomita 210 tsakaninsa da Sakkwato. Daga arewa kuma ya yi iyaka da Æ™asar Ƙaura. A yayin da ya yi wata iyakar daga yamma da BunguÉ—u, ta É“angaren kudu kuma ya yi iyaka da  garin ÆŠansadau da Tsafe (Gusau, 1984:7).

                Kasancewar almajirin Shehu Usmanu ÆŠanfodiyo wato malan Sambo ÆŠan’ashafa ya kafa Gusau, wanda yake shi da jama’arsa ba ruwansu da duk harkokin da suka shafi bautar iskoki da tsafi, irin wanda Hausawa ke yi kafin zuwan addinin Musulunci,ma’ana garin Gusau ba ya  da tarihin jahiliyya.

                Haka ta sa duk al’adun Gusawa,  al’adu ne irin na Musulunci. Kuma shigowar wasu mutane, wato baÆ™i a Gusau, ba ta gurÉ“ata waÉ—annan kyawawan al’adu ba, don kuwa mafi yawan baÆ™in da ke tasowa, malamai ne na Musulunci da almajirai.

                Ta É“angaren fada kuwa, duk umurnin da zai fito daga can zai kasance ne dai dai da abinda Musulunci ya yarda da shi na kyawawan É—abi’u da al’adu. Musamman kuma da yake, kusan duk sarakunan da aka yi a garin malamai ne na addinin Musulunci masu taÆ™awa da  tawali’u.  Da wannan shimfiÉ—a ce al’adun Gusawa ke gudana daidai da koyarwar addinin Musulunci da kyawawan al’adu irin na Fulbe da na Hausawa, waÉ—anda ba suci karo da shari’a ba.

                Irin wancan yanayi na kwararowar baÆ™i da Æ™ungiyoyin mutane daban – daban musamman a zamanin Sarkin Katsinan Gusau Malan Muhammadu Modibbo (1876M/1282H – 1877M/1291H) ya sa garin ya sami bunÆ™asa a cikin É—an Æ™anÆ™anin lokaci.

                A bisa Æ™ididdiga da taÆ™aitawa garin Gusau a dai – dai lokacin da ake gudanar da wannan bincike yana da masarauta É—aya  (1), babban sarki É—aya (1), ‘yan majalisa goma sha takwas (18), uwayen Æ™asa goma sha uku (13). Sarautun fada kuma akwai kimanin É—ari da huÉ—u (104). A yayin da ake da manyan malaman addinin Musulunci guda sittin da biyar (65).

                Daga kuma lokacin da aka kafa wannan gari na Gusau, an yi sarakuna kamar haka:

    i.                    Malam Muhammadu Sambo               (1806 – 1827)

    ii.                  Malam AbdulÆ™adir                                            (1827 – 1867)

    iii.               Malam Muhammadu Modibbo                       (1867 – 1876)

    iv.               Malam Muhammadu Tuburi               (1876 – 1877)

    v.                  Malam Muhammadu GiÉ—e                               (1887 – 1900)

    vi.               Malam Muhammadu Murtala                         (1900 –1916)

    vii.             Malam Muhammadu ÆŠangida                        (1916 – 1917)

    WaÉ—anda suka yi sarautar Gusau ba daga gidan malam Sambo ba, kamar haka:

    i.                    Malam Ummaru Malam                                   (1917 – 1929)

    ii.                  Malam Muhammad Mai Akawai                    (1929 – 1943)

    iii.               Malam Usman ÆŠan Sama’ila                (1943 – 1945)

    iv.               Ibrahim Marafa                                      (1945 – 1948)

    v.                  Muhammad Sarki Kudu                                   (1948 – 1951)

    vi.               Alhaji Sulaiman Isah                                         (1951 – 1984)

    Dawowar sarauta gida

    i.                    Alhaji Muhammad Kabir ÆŠanbaba     (1984 – 2016)

    ii.                  Alhaji Ibrahim Bello                                          (2016 zuwa yanzu)

    2.4 NAÆŠEWA

                Wannan babi kuwa an yi magana ne akan taÆ™aitaccen tarihin Æ™asar Hausa da tarihin Æ™asar Zamfara da kuma taÆ™aitaccen tarihin garin Gusau da kuma naÉ—ewa. Babin da zai biyo baya shi ne kare – karen harsuna.

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.