Ticker

6/recent/ticker-posts

Mijina Ba Ya Sanar Da Ni Idan Zai Fita, Idan Kuma Ya Dawo Ba Ya Yin Sallama

𝐓𝐀𝐌𝐁𝐀𝐘𝐀

Assalamu alaikum malam, ya ƙoƙari? To, Allah ya taimaka. Malam, tambayata ita ce: Wai mene ne hukuncin namijin da idan zai fita ba ya wa matarsa sallama ko gaya mata ya fita, amma yana so ta yi masa addu'ar Allah ya tsare? Haka kuma idan ya dawo, ba ya yi mata sallama, amma yana so ta yi masa sannu da zuwa. Sai ita kuma tace haramun ne, ba za ta yi ba; idan bai gaya mata ya fita ba, ba za ta ce masa Allah ya tsare ba, idan kuma ya dawo bai yi mata sallama ba, ita ma ba za ta yi masa sannu da zuwa ba. To malam, yaya wannan abin yake? Ya halatta a gare ta ta ƙwale shi?

𝐀𝐌𝐒𝐀❗️

Wa alaikumussalam warahmatullahi wabarakatuh.

A shari'ar Musulunci, wajibi ne miji ya yi wa matarsa sallama idan ya shiga gida, kuma yana da kyau ya sanar da ita idan zai fita. Amma rashin yin hakan ba ya halasta wa matar ta ki yi masa addu'a "Allah ya tsare" ko ta ki tarbar sa da sannu da zuwa ba, domin biyayya da mutunta miji suna da nata matsayi.

Ba wajibi ba ne a shari'ar Musulunci miji ya fada wa matarsa duk lokacin da zai fita daga gida, amma hakan yana da kyau domin kwanciyar hankali da kuma sanin halin da ake ciki. Kuma yana kawo wa matarsa nutsuwa kuma yana hana fargaba, yana kara nuna girmamawa da kuma kyautata zama a tsakaninsu.

Allah ya wajabta yin sallama lokacin shiga kowane gida, har da gidan mutum na kansa. A cikin Suratus-Nur aya ta 61:

... ؕ فَاِذَا دَخَلۡتُمۡ بُيُوۡتًا فَسَلِّمُوۡا عَلٰٓى اَنۡفُسِكُمۡ تَحِيَّةً مِّنۡ عِنۡدِ اللّٰهِ مُبٰرَكَةً طَيِّبَةً ؕ كَذٰلِكَ يُبَيِّنُ اللّٰهُ لَـكُمُ الۡاٰيٰتِ لَعَلَّكُمۡ تَعۡقِلُوۡنَ

...To, idan kun shiga wasu gidaje, ku yi sallama a kan kawunanku, gaisuwa ta daga wurin Allah mai albarka, mai daɗi. Kamar wancan ne Allah Yake bayyana muku ayoyinSa, tsammaninku ku yi hankali. (Surah: An-Noor, Ayat: 61).

Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya ce wa Anas ɗan Malik: "Ya kai ɗana! Idan za ka shiga gurin iyalinka ka yi sallama, zai zama albarka a gare ka da kuma mutanen gidanka." (Tirmidhi).

Idan kina fuskantar wannan matsalar, yana da kyau ki zaunar da mijinki cikin lallashi da nuna ƙauna, ki tunatar da shi wannan sunnah ta Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) domin gidanku ya ci gaba da samun albarka da zaman lafiya.

A cikin hadisin da ke cikin Sahih Muslim, Manzon Allah (Sallallahu Alaihi Wasallam) ya bayyana cewa idan mutum ya shiga gidansa bai ambaci sunan Allah ba (wato bai yi sallama ba), Shaidan yana cewa da sauran shaidanu: “Kun sami wurin kwana a daren nan.” Wannan yana janyo yawan fada, rashin fahimta, da ɓacin rai a tsakanin miji da mata. Idan mutum ya shiga gida ya ambaci sunan Allah (ya yi sallama), shaiɗan yakan ce wa sauran shaiɗanu: "Ba ku da masauki a wannan gidan yau." Idan miji ya shiga gida da sallama da ambaton Allah, shaidan yana fita daga gidan, kuma zaman lafiya da albarka suna tabbata tsakaninsa da matarsa.

Mijin da yake shiga gida ba tare da ya yi wa matarsa ko iyalinsa sallama ba ya bar babban alheri, ya kuma saɓa wa koyarwar Alƙur'ani da Sunnah, domin yin sallama lokacin shiga gida Sunna ce mai ƙarfi (wasu malamai sun ce wajibi ne) da ke kawo albarka da kariya ga gida. Shiga gida babu sallama dabi'a ce ta rashin kulawa da rashin kyautata wa iyali. Ya kamata miji ya lazimci yin sallama domin samun rahamar Allah a gidansa.

Yin sallama yana sanar da mace cewa mijinta ne ya shigo, hakan yana hana ta tsorata ko firgita. Amma tana iya firgita idan ta ji mutum ya bayyana a kanta farat ɗaya ba tare da ta ji motsi ko sallama ba. Idan miji ya shigo bai yi sallama ba, mace za ta iya riga shi yin sallamar domin tunatar da shi cikin ruwan sanyi da hikima.

Malaman Musulunci sun bayyana cewa, koda mutum ya shiga gidan da babu kowa a ciki, Sunna ne ya yi sallama ta hanyar cewa: "ASSALAMU ALAINA WA 'ALA 'IBADILLAHIS-SALIHIN." Ko kuma Ya ce: ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAHI WABARAKATUH. Ko da babu kowa a gidan, shari'a ta nuna mutum ya yi sallama domin akwai mala'iku da aljanu musulmai masu zama a wurin.

Saboda haka wajibi ne miji ya yi wa matarsa sallama idan ya shiga gida, kuma yana da kyau ya sanar da ita idan zai fita. Amma rashin yin hakan ba ya halasta wa matar ta ki yi masa addu'a "Allah ya tsare" ko ta ki tarbar sa da sannu da zuwa ba, Rashin yi masa addu'a "Allah ya tsare" ko "sannu da zuwa" saboda zafin rai ko ramuwar gayya kuskure ne kuma rashin biyayya ne. Idan ta ki saboda ta ce sai ya gyara nashi laifin, tana kara rura wutar saɓani tsakaninsu ne. Ya kamata ta yi hakuri ta yi masa addu'a da maraba, sannan ta yi masa sallama domin tunatar da shi cikin ruwan sanyi da hikima.

WALLAHU A'ALAM

Zauren Fatawoyi Bisa Alkur'ani Da Sunnah.

ﺳُﺒﺤَﺎﻧَﻚَ ﺍﻟﻠَّﻬُﻢَّ ﻭَﺑِﺤَﻤْﺪِﻙَ ﺃﺷْﻬَﺪُ ﺃﻥ ﻟَﺎ ﺇِﻟَﻪَ ﺇِﻻَّ ﺃﻧْﺖَ ﺃﺳْﺘَﻐْﻔِﺮُﻙَ ﻭﺃَﺗُﻮﺏُ ﺇِﻟَﻴْﻚ

WALLAHU A'ALAM.

https://t.me/TambayaDaAnsa

𝐖𝐇𝐀𝐓𝐒𝐀𝐏𝐏👇

https://whatsapp.com/channel/0029VaA8YpB42DcZdoRuCj3G

𝐅𝐀𝐂𝐄𝐁𝐎𝐎𝐊👇

Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

**************************

Wannan ɗaya ne daga cikin fatahowin Musulunci da aka gina su kan Ƙur’ani da Hadisan Manzon Allah (SAW) waɗanda ake samu a shafukan Tambayoyi da Amsoshi na Sheik Malam Khamis Yusuf a Facebook, Telegram, da WhatsApp. Za ku iya bibiyar shafukansa domin karanta ƙarin fatawowi.

Question and Answers in Islam

Post a Comment

0 Comments