Ticker

6/recent/ticker-posts

Tsattsafin Raha Cikin Waƙoƙin Alƙali Alhaji Haliru Wurno

Na rubuta wannan maƙala domin tunawa da Alƙali Alhaji Haliru Wurno, ɗan uwa kuma masoyi. Allah ya yi masa gafara ya sa shi cikin aljannarsa Firdausi cikin rahamarsa da jinƙansa, amin.” (Prof. A.B. Yahya)

Daga 

Abdullahi Bayero Yahya
Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya
Jami’ar Usmanu ƊanfodiyoSakkwato
Email: 
bagidadenlema2@gmail.com 
Phone: 
 07031961302

Tsakure

Raha haliyyar ɗan Adam ce. Ita kuwa haliyya takan yi tasiri a kan rayuwar ɗan Adam. Ana iya ganin tasirin wannan haliyya cikin waƙoƙin da Alƙali Alhaji Haliru Wurno ya rubuta. Waɗannan waƙoƙi kuwa sun ƙunshi jigogi mabambanta, kama daga waɗanda suke sakayau kuma maɗauka raha, zuwa ga masu nauyi waɗanda bisa ga al’ada, manisanta ne da raha. Saboda haka ne wannan maƙala take kallon wannan tsattsafi na raha a matsayin salon marubuci na gaba ɗaya cikin waƙoƙin Alƙali Alhaji Haliru Wurno. A taƙaice tsattsafin raha shi ne salon waƙoƙinsa na gaba ɗaya, da shi ne za a iya a ce wannan waƙar Haliru Wurno ce ko kuma ba ita ce ba.

ƙoƙarin tabbatar da haka maƙalar ta fara da gabatarwa wadda ta ƙunshi bayani a kan kalmomin fannu, da kalmomin ƙumshiyoyin tunani masu nasaba da haliyyar raha, da kuma taƙaitaccen tarihin Alƙali Alhaji Haliru Wurno. Daga nan sai maƙalar ta shiga yin nazari a kan wuraren da haliyyar raha ta samu tsattsafi cikin waƙoƙin mawaƙin. Ta kuwa haɗa wannan tare da misalai domin kafa hujja.

Gabatarwa

Babban ƙudurin wannan maƙala shi ne tabbatar da cewa tsattsafi, wato barbaɗi ko yayyafin haliyar raha shi ne salon waƙoƙin Alƙali Alhaji Haliru Wurno. Salo ne wanda ya zo a ƙarƙashin abin da Abdulƙadir Ɗangambo ya kira Salon marubuci na gaba ɗaya1

To amma kafin maƙalar ta nuna gaskiyar wannan hasashe zai dace ta fayyace wasu kalmomin fannu da ƙamshiyoyin tunani. Sanin haka ne madafa ga fahimtar gundarin saƙon da maƙalar take ɗauke da shi.

Kalmomin Fannu Da Ƙumshiyoyin Tunani

Muhimman kalmomin fannu a wannan nazari su ne tsattsafi da haliyya. Su kuwa ƙumshiyoyin tunani masu nasaba da raha su ne fara’a da nishaɗi da ban-dariya da shammata da ba’a da bananci da kuma barkwanci

Tsattsafi yana nufin salon kawo wata magana (wato, saƙo ko jigo) ko cusa wata haliyya ko kuma amfani da wani salo a kai a kai (wato, a yayyafa ko a barbaɗa) cikin waƙa ko kuma mafi yawan waƙoƙin marubuci. Idan muka ƙaddara waƙa a matsayin wani fili mai faɗi, sannan muka ɗauko wani abu kamar gari muka barbaɗa shi a wannan fili, garin zai kasance wanda ake iya gani a nan da can a cikin filin. Saboda haka an samu tsattsafin gari cikin wannan fili. Kiran wannan salo da sunan tsattsafi ba barbaɗi ko yayyafi ba, waɗanda duk masu dacewa ne, ya zo ne domin yin ishara da ‘daɗi’ ko ‘zaƙin’ da salon yake ba waƙa. Wato wannan salon, tsattsafa ce, tsattafa kuwa da zuma akan yi ta.

 Haliyya tana nufin yanayin ko ‘labarin’ zuciya wanda waƙa take tattare da shi. Yanayi ne da kalmomi da yadda suka zo cikin waƙa suke cusa wa mai karatu ko sauraren waƙa. Haliyya tana iya zama ita ce wadda zuciyar marubuci take ciki a lokacin da yake rubuta waƙarsa, ko kuma haliyyar da ya cusa wa kansa da gangan domin waƙar da yake a kan rubutawa ta ƙunshe ta.2 Ga alama haliyya za ta fi jigo ko salo jawo muhawara a tsakankanin manazarta waƙoƙi saboda nasabarta da zuciya.

Kalmomin raha da fara’a da nishaɗi dukansu haliyyoyi ne masu ma’anonin da suka yi kusa da juna. Dukansu nau’o’i ne na farin ciki. A yayin da farin ciki ya wanzu a matsayin kalmomi biyu na tsagwaron harshen Hausa, su kuwa kalmomin nan uku ga alama su ne suka maye gurabun takwarorinsu na harshen. Masana harshen Larabci su ne da ilmin fayyace yadda suke. A harshen Hausa dai raha tana nufin sakankancewar zuciya cikin walwala da rashin damuwa. Ita kuwa fara’a tana nufin jin daɗin rai(zuciya) mai haskaka fuska. Nishaɗi yanayin zuciya ne makamancin raha kuma mai saurin ingiza mai shi ne ga yin abubuwa na walwala. Abin da wuya ( ba da kamar wuya ba), har dai ga wanda ba masanin Ilmin Mutuntaka ba.

Ban dariya shi ne abu ko aikin da yake sa a yi dariya ko murmushi. Su kuwa waɗannan ayyuka dukansu masu bayyana haliyar raha da dangoginta ne. Shammata cikin magana tana nufin a faɗi wani abu game da mutum, na jikinsa ko halinsa, domin muzantawa wadda za ta kawo a dare shi. Ba’a tana kusa ga shammata wajen ma’ana fiye da bananci. Wato faɗar magana ga wani domin ta ba shi haushi a yi dariya, ga ta nan dai kamar wani ƙaramin zambo. Shi kuwa barkwanci magana ce mai kawo dariya gaya ko da kuwa ga lamarin da ya riga ya ɓaci ne.

To duk waɗannan abubuwa, tun daga ban-dariya har zuwa barkwanci, ayyuka ne waɗanda suke bayyana samuwar raha tattare da mai aiwatar da su. A. wannan maƙala abubuwa ne da ke bayyana raha cikin waƙa musamman a baitoci ko ɗangogin da suke. Abubuwa ne da watakila suke yin ishara ga halin marubucin waƙa na kasancewa mutum wanda raha ta rinjayi fushi da damuwa da baƙin ciki, da dai dangogin waɗannan, a cikin rayuwarsa gaba ɗaya. Abin nufi a nan shi ne marubucin da ake iya siffanta salon waƙoƙinsa na gaba ɗaya da cewa salon raha ne, to ana kyautata zaton cewa mutum ne mai fara’a, mai dariya kuma wanda ba ya barin damuwa ko baƙin ciki ko ɓacin rai, ɗayansu ko dukansu, su nauyaya rayuwarsa. Mutum ne mai tarbon abin da ya zo masa a yadda ya zo masa. Idan na ɓacin rai ne, ya nuna ɓacin ransa, amma kuma ba zai bari ya faifaye ba, domin rayuwa ba ta kasance ɓacin rai duka ba. Haka ne zai yi da sauran faɗi-tashin rayuwa. Hasali ma yakan yi ƙoƙarin sassauta su.

 Da wannan bayani ne maƙalar za ta juya zuwa ga taƙaitaccen tarihin rayuwar Alƙali Alhaji Haliru Wurno.

Alƙali Alhaji Haliru Wurno

A wannan ɓangare za a fi mayar da hanakali a kan halayen Haliru Wurno kamar yadda marubucin wannan maƙala ya san shi.3

An haifi Haliru Wurno cikin shekarar 1925 a ƙauyen Ƙwargaba na ƙasar Wurno ta Jihar Sakkwato. Abin lura a nan shi ne Haliru Basakkwace ne kuma Bagiɗaɗe. Sarauta ce ta kai kakansa a Wurno inda ya yi Sarkin Rima. A wata waƙar madahu wadda ya kira ‘Ƙorama’ Haliru ya ce:

Waƙar yabon Manzo ga raina nif fake

Ƙarin bayanina usulu ina shike

Bari in faɗa maka inda dangina suke

Kwat tambaya birni na Sakkwato nan suke

 Manyan Giɗaɗawa gidan albarka.

(Ƙorama)

 

Haliru ya sake kawo irin wannan bayani a wata waƙarsa mai suna ‘Jirgi’, ita ma ta madahu, inda ya ce:

Alhaji yay yi waƙag ga Alƙali ga dauri

Nan shinkafi niy yo ta niy yabi Annabin ga

 

Bayan Azzuhur tat taho min nir rubuta

Ran Narba watan Hajji niy yabi Annabin ga

 

Salla na da kwananta ukku ji in faɗa ma

Ƙarshen Rajmu mai hajji shi ka sanin hakan ga

 

Kun san Wurno birninsu ta can anka haifai

Sakkwato yay yi wayo cikin Birnin ƙasag ga

 

Sarkin Rima Kakansa na bari in faɗa ma

To Maigandi tsohonsa na in ka ji wagga

 

Shi ad Daudu can Wurno wan Mallam Alu na

Mallam Shaihu Mallam Yahayya ‘yan uwan ga

 

Sa da Magaji Mamman Marafa ji in faɗa ma

Diba “Ƙorama” na yi ma zanen waɗanga.

(Jirgi)

 

Saboda haka Haliru yana da dangi a Sakkwato kuma yana da su a Wurno, kamar dai yadda Sakkwatawa da dama suke. Bari ma ta wannan, da Sakkwato da Wurno sun yi tarayya ga sunayen shiyyoyin da ke cinkinsu.

Haliru Wurno ya tashi cikin zuri’ar da ilmi ne safararsu. Wato Giɗaɗawa, waɗanda suka samo sunansu daga Usman Giɗaɗɗan Laima. Shi kuwa Giɗaɗo shi ne wazirin Sarkin Musulmi Muhammadu Bello ɗan Shehu Usmanu ɗan Fodiyo, Allah ya yi mu su rahama, amin. Bagiɗaɗe ba ya da wani abin tinƙaho da ya wuce ilmi da neman sa. Saboda haka Haliru ya buɗe ido da neman sani. Ya yi karatu a gida da kuma makaranta kamar sauran giɗaɗawa. Ya yi karatun allo da na sani a makarantar Liman Macciɗo a garin Sakkwato4 Haka nan kuma ya yi karatu wurin wasu malamai, a cikinsu kuwa har da dangisa musamman kakanni da iyaye. Waɗannan sun haɗa da Waziri Junaidu da Malam Joɗi. A Wurno ya yi karatu wurin Malam Bayero da Malam Abubakar Uban Lale. Waƙoƙin Alƙali Haliru Wurno sun isa shaida ga irin tarin sanin da ya tsotsa daga waɗannan malamai. A cikinsu yakan kafa wa duk maganar da ya faɗa hujja daga Alƙur’ni Mai Tsarki da Hadissai da kuma littattafan magabata. Misali, bayan da ya ambaci sunayen iyaye da ‘yan uwansa cikin wasu baitoci na waƙarsa ta madahu, sai ya kawo wannan baiti:

An so sanin dangi ga aya na ga ta

Ka sano zumunta taka to kyauta mata

Wada nig gani kuma nik karanta tabbata

Ban yo faɗin ga ba don fahar na tabbata

Li ta’arafu ayag ga tah hore ka.

(Ƙorama)

 Kai mai karatu da ganin wasu waƙoƙin Haliru ka san sai zuzzurfan ilmi yake iya saƙa su. A wata waƙarsa ta wa’azi ya taɓo tauhidi inda yake cewa:

4Mu yo kalimar shahada tun da farko

Mu tabbata shi kaɗai na bai gushewa

5.Mu yarda mu shaida shi Ɗai na Guda na

Da yaz zam tun azal yake babu kowa

Ina rani ina kaka da ɗari

 Ina suke tun da babu ruwan zubawa

Azal yake tun azal yake ko azal ma

Ga Allah ba azal don babu kowa

(Yana Wa’azin Ku Har Shi Bai Cirewa)

Tsakanin shekarar 1943 da 1947 Haliru ya yi makarantar horar da alƙalai ta Sakkwato, wato “Sokoto Qadi School” a Turance. Daga cikin malamansa a wannan makaranta akwai Waziri Junaidu da Malam Ahmadu Ɗan Hannun Giwa.

Haliru yana sauka a wannan makaranta sai ya zarce zuwa makarantar nazarin ilmin Sharia ta Kano, wato ‘Kano Law School’. Ya shekara huɗu a can inda ya kammala a 1951. Malamansa a wannan makaranta sun haɗa da Shaikh Awad Muhammad Ahmad da Malam Nasiru da kuma Malam Abubakar Gumi.

An ɗauki Haliru aiki bayan da ya kammala karatu a makarantar Kano, a matsayin malami mai karantar da ilmin addinin Musulunci da Larabci a makarantar Maru wadda a lokacin ake kira Elementary Training Centre (E.T.C.) Maru. To amma bayan shekara ɗaya da wata shida sai aka ɗauke shi aiki a ma’aikatar shari’a ta lardin Sakkwato. Ya yi aiki nan a matsayin akawun kotu tun daga 1952 har zuwa 1965, lokacin da ya bari ya koma ga karantarwarsa. Ya zauna a makarantar Nizamiyya ta ‘Yar Akija a garin Sakkwato a matsayin malamin addini da Larabci. A lokacin ne ya rubuta ‘Waƙar Fanda’ ko ‘Waƙar Danja’ wadda ta shahara a tsakankanin ‘yan makaranta a Sakkwato da kewaye.

Shekara biyu da ‘yan watanni ya yi yana karantarwa a Nizamiyya kafin ma’aikatar shari’a ta neme shi da ya koma ya yi alƙalanci. Ya karɓi wannan gayyata ya kuma ci gaba da aikin har zuwa 1981 lokacin da ya bari don ganin damarsa, ya sake komawa ga karantarwa.

Ta fuskar aikin shari’a Haliru ya zauna garuruwa da ƙauyuka da dama na jihar Sakkwato. Haliru ya ambaci wasu daga waɗannan wurare cikin wata waƙar wa’azi da nasiha da komawa ga Allah Ta’ala:

Ji Alhaji Wurno Alƙali na dauri

Ina tuba ga Rabbul alamina

Ka yafe min zaman Maru har Bakura

Maradun mufti wayyo ni jiƙai na

A Sabon Birni Gobir nai zama can

Bakwai na shekare Gobir zamana

Ka yafe min zaman Gwadabawa shi ko

Kurena ko da gangancin halina

(Sabilul Haƙƙi Bi Ƙaulis Sidƙi)

 Sauran wuraren da ya sha ambata cikin waƙoƙinsa sun haɗa da Yaldu da Silame da Tangaza da Raɓa. Su kuwa garuruwan da ya zauna lokacin karantarwar da ya yi sun haɗa da Maru da Wurno da Sakkwato. A Sakkwato ne kuma Allah ya karɓi ran Haliru cikin gidansa na Kwalejin Abubakar Gumi Ta Fasaha Da Larabci, ranar

Alhamis 16 ga Oktoba na 2003 bayan sallar La’asar kuma kusan sallar magariba.

Alƙali Alhaji Haliru Wurno mutum ne wanda duk wanda ya san shi zai tabbatar da kasancewarsa mutum mai fara’a da sakin fuska. Da wuya mutum ya iya haƙiƙance fushinsa, muddin dai fushin bai danganta da saɓon Mahalicci Allah Ta’ala ba. A nan ma Haliru ya kasance mai hucewa ya dawo yana lallashin mai saɓon, yana nuna masa aibin saɓon da ya sa shi Haliru ya fusata. A ƙarshe zai saka wannan mutum cikin halin nadama da kuma dariyar kansa da kansa duk a lokaci guda. Haliru ba ya bari abokin hulɗarsa ya bar gidansa cikin ɓacin rai, saboda wai wata magana da shi Haliru ya faɗa masa. Shi a kullum na’am-na’am yake yi da jama’a. A ra’ayin marubucin wannan maƙala, tabbas! Haliru ya gadi abubuwan da shi kansa ya faɗi game da kakansa Waziri Junaidu cikin wannan baiti:

In mutum ya ƙi gaisai shi gaishe shi

Shi da baƙonsa dan nesa zai tashi

In fa ya san ka ko kai fa kas san shi

Ba ka cewa da baƙi ga ƙirjinshi

Ga sakin fuska ko ba ka san shi

(Waƙar Yabon Waziri Junaidu)

Haka kuma lalle baitin nan da Haliru ya yabi Sarkin Musulmi Abubakar III da shi, shi kansa Haliru Wurno tsaf da tsaf ya dace da shi:

Son zumunta da hani da alheri

Ga zalaƙa kuma ga shi ba kibri

Ga sakin fuska ga shi mai sabri

Ga amana koyaushe ba sharri

Ƙeta ko can bai gane sunanta

(Safiya Da Gaskiya Taka Aiki)

Wani halin Haliru shi ne karimci. Duk wanda ya san wannan bawan Allah to kuwa zai shede shi da irin wannan hali. Haliru masoyin zuma ne kuma mai yin iyakar ƙoƙarinsa ne ya ga ya yi tanadin ta a gidansa. Idan ya yi baƙo sai ya haɗo da faraufarau na zuma cikin tarbar da zai yi masa. Abu ne mawuyaci ka baƙunci Haliru ya kasa tarbon ka da wani abu na sa wa a baka, sai dai abin nan ya ƙaranta. Idan ma baƙo bai tarar da kome ba to aƙalla Haliru zai cusa masa fara’a da maganganun da zai yi masa. Wani ƙanen mai maƙalar nan ya ba da labarin cewa lokacin da yana ɗan makaranta a Tangaza shi kuma Haliru yana alƙalanci a can. To takanas ne Haliru zai aika a ɗauko masa ƙanensa daga makaranta, ba don kome ba sai don ya gane shi ya yi masa alheri. Yakan zaunar da shi a kan shimfiɗarsa ya sa a kira mai balangu, ya yi ta yanka masa nama. Yaron zai ci naman nan har ya gundure shi, amma ba fasa yanko masa ake yi ba. Kai ta kai har sai ya kaikaici idon mutane ya yi sauri ya hankaɗa shinfiɗa ya ɓoye nama. Bayan duk wannan, idan zai koma makaranta sai a ƙumsa masa a kuma haɗa masa da masu gida rana!5 Babu wata tantama idan mutum ya san Haliru zai tuna da wannan karimci nasa idan ya karanta waɗannan baitoci na waƙarsa ta madahu:

Baƙo idan ka yo shi kawo mai zuma

Masa da ƙosai to ka yo mishi sallama

Kuma kai fura sannan da ƙosan alkama

Daifun mabuɗi na ga Aljanna zama

Manzon Ta’ala yaf faɗi mun ɗauka

In ka ga baƙo ya taho maka kar ka ce

 Koma ka ba ni wuri ka san suturakka ce

Ka yi mai maraba ka ba shi ci haka anka ce

Koway yi baƙo yay yi mai wada anka ce

An buɗa aljannakka don baƙonka.

(Ƙorama).

Idan kuwa aka nemi sanin kamannu da suturar Haliru6, to wannan ɓangare zai misalta. Haliru dai mutum ne mai tsayi wanda tun daga nesa ake iya hango cewa ya kere mafi yawan na tare da shi Baƙi ne ga launi kuma mai tsawon fuska. Idonsa matsakaita ne ga girma, sannan kuma yana da faɗin goshi da tsawon hanci, da baki mai siraran leɓɓa. Idan yana maganar da ya tabbatar da cewa ƙaƙƙarfar hujja ce, tun ma ba a ce daga nassi hujjar take ba, idonsa sukan turo waje su kuma kafe a kan wanda yake magana da shi.

Haliru ya kasance mai son sutura wadatacciya, mai kammala Bahaushen mutum.Wato tufafinsa su ne riga da taguwa da wando mai faɗi da hula da rawani. Idan akwai rana mai kaifi yakan sanya baƙin tabarau. Waɗannan tufafi su ne na fitarsa. Idan kuwa a gidansa yake, to idan bai zauna haka nan da su ba yakan cire riga ya bar taguwar, wadda a koyaushe mai tsawo ce har zuwa rabin ƙwaurinsa. Haƙiƙa wannan baiti na tafe ya zayyana irin fitar Haliru:

In za ka salla yo naɗi da mubarrashi

Manyan tufafi masu kyau na haɗallashi

Kuma zanka yin fara’a ka samu tagomashi

Azumin da kay yi yini guda lillahi shi

Ka tsira shekarru da kai da wutakka

(Ƙorama)

A fagen waƙa Haliru gwani ne na ji da gani. Waƙa a wurinsa kamar maganar yau da kullum ce. Wato mai ƙaƙa waƙa ne a duk lokacin da ya tashi ko aka bukace shi da ya yi ta. Baiwa ce Allah ya yi masa. Haliru marubucin waƙa ne a koyaushe, kuma cikin kowane irin hali yana iya yin ta. An taɓa tambayar sa yadda waƙa takan zo masa sai ya ce babu yadda ba ta zo masa, matsalarsa guda ita ce idan bai da alƙalami da takarda a hannunsa. Wato muddin dai yana tare da waɗannan to kuwa waƙa tana zo masa7 Tamkar dai lisafin da za a gabatar wa Ka-fi-Komfuta-Sauri na Zariya8

Haliru ya fara rubuta waƙa tun yana ɗan shekara goma sha biyar, kuma abin mamaki da harshen Larabci ya fara9 Wato ke nan ba a Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya ne kurum za a iya nazartar gudunmawar da Haliru ya bayar ga al’umma ba. A’a, har ma da Sashen Koyar da Harshen Larabci. To a ɓangaren rubutattun waƙoƙin Hausa Haliru ya faɗi cewa shi kansa bai san ko waƙoƙi nawa ne ya rubuta ba. Abin da wannan bincike da waɗanda suka gabata suka tabbatar shi ne waƙoƙin ba kaɗan ne ba. Da yawa daga waƙoƙinsa bai ba su suna ba, abin da manuniya ce ga cewa Haliru mai zara ne ga tunani da rubuta waƙa da kuma ƙaiƙayin hannu wajen rubuta ta10.

Jigogin waƙoƙin Haliru masu yawa ne. Ya rubuta a kan madahu da wa’azi da nasiha da yabo na mutane da kishin ƙasa da waƙa ita kanta. Haka nan kuma ya rubuta a kan gyaran al’umma da ɗanɗana da faɗakarwa da ilmi da tauhidi da ƙwarewa ga harshen Hausa da addu’a da marsiyya da kuma soyayya, kai, har ma da waƙoƙi a kan kansa. Ya kuma rubuta waƙoƙi a kan al’adu da waƙoƙin yara da martani da siyasa ta gaba ɗaya da ban kwana da abokai da ‘yan uwa.Waƙa a wurin Haliru zuwa take yi ba ƙaƙƙautawa, kamar yadda baitocin nan suke da saresarin faɗar haka:

Waƙar da niy yi yabon mutane na tuna

Na wa aminnai ‘yan uwa na yo kina

Wasu ko ga fili nif faɗi nib bayyana

Na ɗaura waƙoƙi ubana yah hana

Ta yabon mutane na bari sai taka

….

Waƙar mutane na yi ga ta a kai a kai

Wasu na yi zambo sun ji har aike nikai

Wasu na yaba su suna biɗa aike sukai

Na rera waƙoƙin saraki hakimai

Na ya da saiɓi ‘yan kazagge ka ɗauka

(Ƙorama)

Haliru bai tsaya a kan rubuta waƙoƙinsa kurum ba. Ya yi wa waƙoƙin wasu tahmisi sannan kuma ya yi wa nasa tahmisin! Ya kuma yi wani abu wanda saboda rashin kalmar da ta dace, zan kira bin sawu na wani mawaƙi ko wata waƙa. Bin sawu yana nufin a samu mawaƙi ya rubuta waƙa wadda ta ɗauko jigo ko jigogi, da kari da jimloli, har ma da salo, irin na wata waƙɗaya (ko fiye) ta wani mawaƙi dabam, har wannan waƙa ta daga baya ta kasance kamar dai waccan ce ta farko. To amma fa akwai bambanci duk da waɗannan kamannu. Waƙar Haliru mai suna “Tura Ta Kai Bango” misali ne na bin sawu. Waƙar ta bi sawun shahararriyar waƙar nan ta Wazirin Gwandu Alhaji Umaru Nasarawa, mai suna ‘Zaɓaɓɓiya’. Dubi wannan misali:

 

Zaɓaɓɓiya

(Alhaji Umaru Nasarawa Wazirin Gwandu)

Tura Ta Kai Bango

(Alƙali Alhaji Haliru Wurno)

1. Na kirayi mai iya jinƙai na

 Wanda shi ka ɗaukaka sunana

 Nan da nan shi kammala girmana

 Tun da na kirai ban donewa

 

7.Ko da ban yi ƙwazon komi ba

 Ya Azimu kai ɗai nika duba

 Tun da ko daɗai ban san wani ba

 Ban da kai Guda Mai gyarawa

 

9. Can wurin da kac ce ‘Fad’u ni

 Astajib lakum’ ba nisyani

 ‘Ba-ni-ba-ni’ bai sa ma ramni

 Naka arziki bai ƙarewa

 

12. Dauri anka kasan nid daure

 Anka koma kasan nij jimre

 Yanzu hanƙurina ya ƙare

 Ƙadiran nufan ni da ramawa

 

18.Ga garinmu ban kwana daji

 Ga Ka ban biɗar wani budeji

 Tun da na sani Kai am Munji

 Malja’inka nan nika dagewa

 

50.Wanda yay yi waƙa sunanai

 ‘U’ da ‘Ma’ da ‘Ru’ ga mazamninai

 Sai ka zo ka ‘Bi Ke’ birninai

 Nasarawa can kaka komawa

1. Na kirayi Allah Ƙahharu

 Wanda ad da baiwa Jabbaru

 Shi ka yafane mini Sattaru

 Ga ni na yi laifi Gaffaru

 Nai kure ina son yafewa

 

18. Ko da ban yi aikin daidai ba

 Jalla ban fa mance laifi ba

 Ban ga wanda za ni ya cetan ba

 Ban da Kai Ilahi don Ɗaiba

 Ba ni nau muƙamin takawa

 

23. Rabbu tun da ka ce ‘Fad’u ni’

 ‘Astajibu’ Allah kama ni

 Na ɗime jikina yai ramni

 Ba ni kai ka bai in ka ba ni

 Ba ni duk wadat da ka ɗorewa

 

14 Rabbu dut abina ya ƙare

Dauri anka yo mini na jimre

Yanzu hankalina ya tsere

Ga shi hanƙurina ya ƙare

 An buge ni ban iya ramawa

 

11 Na ɗimauta har na kwan daji

Na yi kwance ba inwar gamji

Ni kaɗai ga rana sai tuji

Wanda bai kiyo ga hakin samji

 Ya Ƙawiyyu na so komawa


49 Mai biɗat sanin ma’ajin waƙa

‘Ha’u’ ‘Dadu’ ‘Ra’ shi yas sarƙa

Wurno ag garinsu gida haƙƙa

Fassararsa Alhaji Ishraƙa

 Ko da yaushe bai rasa shiryawa


Wannan, a taƙaice, shi ne bayani a tarihance na wannan mashahurin mawaƙi mai basira kuma haziƙi. Mutum ne mai tsoron Allah, mai ƙasƙantar da kai, ma’abuci raha, ga kuma sakin fuska da karimci da son zumunta. Malami ne gwanin bayanin darussa, mai koyi da Sunnar Manzon Rahma (S.A.W.). A duk inda ya zauna, musamman a makarantun da ya karantar, ya kasance malami wanda ɗalibai suke matuƙar ƙauna da kuma son su zama kusa da shi, suna masu girmama shi. Shi ne kuma limami a wuraren. Karantarwa ta kasance cikin jininsa, domin ko a cikin aji, ko a gidansa, ko a hanya, a shirye yake da ya ba da sani, kuma a haka ya bar gidan duniya. Ɗiyauci ne wata jami’a musamman Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo ta karrama wannan bawan Allah da digirin girmamawa na D.Litt. Wannan shi ne Alƙali Alhaji Haliru Wurno. Allah ya yi masa gafara ya ba shi mafi darajar karramawa, gida a aljannar Firdausi. Amin.

Tsattsafi

Bayani ya gabata cewa tsattsafi wani salo ne na yayyafa ko barbaɗa wata magana (jigo), ko haliyya, ko ma wani salo daga salailai, cikin waƙa ko waƙoƙin mawaƙi. Idan a waƙa guda ce salon yake sai a ce akwai tsattsafin abu kaza a cikinta. Idan kuwa a cikin dukkan ko mafi yawan waƙoƙin mawaƙi ne salon yake, sai a ce akwai tsattsafin abu kaza cikin waƙoƙinsa. A nan sai a kalle shi a matsayin salon mawaƙi na gaba ɗaya domin kuwa salon tsattsafi a irin wannan siga yakan taimaka wajen tantancewa da waƙoƙin mawaƙi.

Waƙoƙin Alƙali Alhaji Haliru Wurno ɗauke suke da tsattsafin raha, duk kuwa da cewa ya rubuta waƙoƙin a kan ɓangarori da jigogi masu tarin yawa. A wannan ɓangare kaɗan daga waƙoƙin ne bayani zai mayar da hankali, amma kuma da nufin waƙoƙin su kasance wakilai na sauran.

Waƙoƙi ‘Yan Sakayau

Haliru ya rubuta waƙoƙin da za a iya cewa saƙonninsu sakayau suke. Wato ba masu nauyi ba ne, ba su bukatar zukata su kasance cike da natsuwa da ladabi. Ba kamar waƙoƙin wa’azi ko madahu ba waɗanda suke sa zuciya ta yi taushi ko ta natsu tare da tawali’u. Irin waɗannan waƙoƙi masu saƙonni sakayau na Haliru sun haɗa da na soyayya da wasu na yabon mutane da kuma wasu na ɗanɗana. Babu mamaki idan aka samu baitoci masu raha cikin waɗannan waƙoƙi, domin kuwa suna da dangantaka da ita, kuma wasu ma sakamakonta ne. Mai karatu ko saurare zai iya jin samatar raha a duk tsawon wata waƙa wadda ya yi wa Alhaji Giɗaɗo Yabo. Haliru ya gina waƙar da salon shillo11. Wato mawaƙin bai fara kai tsaye da ainihin jigon waƙarsa ba. A maimakon haka sai muka riƙa ganin sa a wannan wuri da wancan yana neman a riƙa shi ko a taimake shi, amma kuma a ko’ina ya tafi sai ya gane cewa babu madafa. A wani wuri ma fitar kutsu ya yi. To sai bayan ya ƙare duk wannan jerangiya (salon shillo) sannan ya samu wanda ya ɗauke shi ya kuma nuna masa ƙauna. Daga nan ne yabon gwarzonsa ya fito ɓaro-ɓaro.

Yin amfani da wannan salo na shillo ya taimaka wa Haliru wajen cusa haliyyar raha cikin wannan waƙa. To amma akwai baitocin da rahar ta fi bayyana. Dubi waɗannan baitoci:

Na ga dila da biri ga kura

Zaki na kusa yah haure ni

 

Na ce gawa ukku kuna nan

Ba ni zama ƙura ta bito ni

 

35Na yi gabas wajjen yanyawa

Kila dibaratai ta ishe ni

 

Na ishe limami yanyawa

Ga ni mu’allimu zo ka daɗe ni

 

Na ga ashe shi ma tai zahi

Sa’alabu ya ce tashi ka bar ni

 

Na yi zugum ya ce kai tashi

Ba ka ganin inwa ta bar ni

 

Na yi zufa rana ga zafi

Matata ita ma ta bar ni

 

 40Na ce Mallam ka san Allah

Yac ce min ai shi yay yo ni

 

Na ce dubi hadisin tanyo

Ba ka yi min girman Addini

 

Na ga kamar maganar ta kam mai

Sa’alabu ya ce kai ka fi ni

 

Na ga kana iya kanka da kawo

Kwanana huɗu ban da sukuni

 

Na yi biɗar ƙannen matata

‘Ya‘yana huɗu dut sun bar ni

 

Na ce assha na sa ƙaimi

Kar ya tumam mini ko ya buge ni

 (Gudale)

A waɗannan baitoci, Haliru ya yi amfani da jinsintarwa12 domin ya samu yin amfani da salon hira, 13 ya tattauna da shi da yanyawa, wato dai yanyawa ya yi magana da shi. Ba a nan ta ƙare ba. Haliru ya kira shi malami, shi kuma yanyawa ya yarda da wannan matsayi, wato mu’allimu. Haliru ya je wurin yanyawa ne domin wataƙila ya ƙaru da dubarunsa. To amma sai ya tarar ba haka abin yake ba. Kalaman yanyawa suna da ɓurɓushin raha ta fuskar ban-dariya. A wannan wurin ne, inda yanyawa ya karɓa sunan liman da malam, kuma har ya tabbatar da yana da ilmin tauhidi, ban dariyar take ga duk wanda ya san yanyawa. Haka kuma sai ban dariyar ta ƙaru lokacin da Haliru ya kawo masa karantarwar Hadisi dangane da taimaka wa masu rauni. A madadin ya amsa sunansa na malami kuma limami, ya tausaya wa Haliru, sai kurum ya mayar da jawabi da cewa / kai ka fi ni / ! Daga nan sai ya shiga maganganun da suka yi wa Haliru nuni da cewa yana iya mayar da shi Halirun namansa, ya yi watsi da malantarsa. Cewar da Haliru ya yi sai ya sa ƙaimi, ita ma magana ce mai ɓurɓushin ba da dariya ga mai saurare.

 

Haka nan kuma labarin da Haliru ya ba mu cewa ya ga dila da biri da kura a wuri guda, sannan kuma ga zaki kusa, labari ne mai ɓurɓushin ban-dariya. Kiran dabbobin nan uku a matsayin gawa uku alhali da ransu, shi ne yake ƙunshe da ban-dariyar. A nan take mai saurare zai yarda da maganar Haliru, domin kuwa zakin da yake kusa ne zai mayar da su gawa. Saboda haka ne Haliru ya yi gaba kada sanadin da zakara yake gudun shaho ya jawo masa, ya far masa, zaki ya haɗa da shi, shi ma ya zama gawa.

 

Duka duka dai, yadda Haliru ya kawo abin da yake son ya faɗa, wato zaɓen kalmomi da na salo, shi ya cusa sashen raha, wato ban-dariya, cikin waɗannan baitoci. Haliru yana da zaɓin kawo labarin dila da biri da kura, alal misali, cikin murya mai ban tausayi ko mai ƙarfafa irin ƙarfin da zaki yake da shi. Haka nan kuma yana iya nauyaya saƙonsa ta hanyar jan hankalinmu zuwa ga yadda rayuwa, musamman ta namun daji take, wato rayuwar fin ƙarfi. To amma mawaƙin bai zaɓi ko ɗayan waɗannan ba. Saboda me? Saboda yana son ya cusa raha cikin baitocin.

 

Wata waƙa da Haliru ya rubuta ita ce “Waƙar Fanda” (Honda) ko kuma “Danja” (danger da Ingilishi). Ita wannan waƙa tana cikin wannan rukuni na waƙoƙi ‘yan sakayau, domin kamar zambo ne (wani abu mai haifar da ban dariya) Haliru ya yi wa babur. Lalle Haliru ya sha kayen babur kuma har jinya sai da ya yi. To amma, kamar yadda halinsa yake, ya yi ƙoƙarin ya ba mutane labarin wannan haɗari cikin raha domin wannan lamari ya riga ya zo har kuma ya wuce, sai labari. Tun da kuwa labari ne zai bayar ai gara labarin ya nishaɗantar.

To a baiti na kusa da na ƙarshe ne raha ta fi bayyana a wannan waƙa. Abin da mawaƙin ya yi shi ne kawo mana bayani a kan yadda matansa suka kansance lokacin da yake jinya a sanadiyyar wannan haɗari da ya yi. Ga abin da ya ce:

A’i ka cewa Mallam na falke

Tumba ka cewa Mallam bai falke

Ga Ige na can ɗaka kai na soke

Babu zama Joɗa da hannu rabke

Balki kiran Nana da wa ba ƙwabri

 (Waƙar Fanda)

Idan aka yi la’akari da yanayin zaman matan Hausawa, wannan baiti a jere ya kawo sunayen matan Haliru. Wato uwargida da kishiyarta sannan mata ta uku wadda daga hannunta ne amarya (mata ta huɗu) ta karɓi muƙamin amarci. Saboda haka A’i ce uwargida sannan Tumba sannan Ige, sannan Joɗa wadda ita ce ba ta daɗe da zuwa ba. Wato amarya ce.

 Yadda Haliru ya bayyana irin halin da kowace mata ta samu kanta lokacin da yake jinya abu ne mai muhimmanci ta fuskar ƙoƙarin cusa raha cikin wannan baiti. Halayen a mataki-mataki suke kuma daga mafi ƙarancin damuwa zuwa mafi tsanani. A’i wadda ita ce uwargida kuma wadda ta riga ta saba da Haliru, ta san rashin lafiyarsa mai tsanani ko marar tsanani. Wato tana iya gane idan rashin lafiyarsa ta tsananta. Saboda haka ita hankalinta bai tashi ba. Don haka take faɗin ai Haliru a falke yake. Tana nuni da cewa bai yi nisa ba. Ita kuwa Tumba ta san Haliru amma ba kamar yadda A’i ta san shi ba. Saboda haka ba mamaki idan ta kasa gane cewa hutawa ce kurum yake yi, ba suma ya yi ba! Ita dai a ganinta ba a falke yake ba (a sakaye, ya suma)! Ige kuwa saninta bai ko kai irin na Tumba ba, balle na A’i. Tsoro ya kama ta. Za ta rasa miji. Joɗa fa wadda ita ce amarya? Ita kam ta gigice, sai zullumin abin da zai biyo baya. Ba wai rasa miji kurum ba, a’a, ai ga al’adar ƙasar Hausa akan camfa matar da mijinta ya rasu ɗan lokaci kaɗan bayan tarewarta a gidansa. Akan ce duk wanda ta aura zai rasu ba da daɗewa ba. Wannan tunanin ne ya ɗimauta Joɗa. A raƙaice, a cikin wannan baiti Haliru yana zolayar matansa ne. Jin haka kuwa kan sa mai sauraren sa aƙalla ya yi murmushi. Su kuwa su Balki da Nana ƙannen Haliru ne. Balki ce ta ruɗe saboda ganin yayansu cikin wannan hali, don haka ne kuma ta ƙwala wa ‘yar uwarta, Nana, kira domin ta zo ko za su samu ganawar ƙarshe da shi.

“Ko Ba Ka Raƙumi Ka San Cau” waƙa ce daga ɗaiɗaikun waƙoƙin da Haliru ya ba suna da kansa. Wannan waƙa ta ƙunshi wasa da maganganun hikima na Hausa, musamman karin magana. Manufar waƙar ita ce ishara, Wannan kuwa shi ya sa waƙar ta zama ta nasiha. Duk kuwa da kasancewarta haka saƙonninta ‘yan sakayau ne ba nauyaya ba. Hasali Haliru ya faɗa cewa waƙarsa wasa ƙwaƙwalwa ce:

Da mallammai da su yara

Kurallu ku daina kisnawa

(Ko Ba Ka Raƙumi…)

A cikin wannan waƙa Haliru ya yi amfani da kare-karen magana masu ban-dariya. Ya yi haka ne ta ɗabi’ar nan da aka san mawaƙa da ita ta jan harshen ɗan Adam har iyakar gaɓa, dab da wurin da nan take bami zai auka. Haka ne Haliru ya yi a waɗannan baitoci na tafe. Da shi bami ne ko jahili da kuwa batsa ta cika su. To amma gwani ne kuma mai ilmi. Raha ce kurum manufarsa kuma ya san iyakar gonarsa. Don haka ba zai wuce ta da iri ba:

Mutum komi rashin kumya

Garai ba za shi damƙowa

Tulin nonon uwar mata

Bajinta ba za shi shahowa

Bale walle gaban suruki

Da gangan ba shi farawa

(Ko Ba Ka Raƙumi…)

A baya kaɗan misali ya zo daga waƙar da Haliru ya rubuta a kan haɗarin da ya yi da babur. To ko bayan babur mota ma ta ɗan girgiza shi. Haliru ya yi haɗari da ita, kuma tasa ce ba ta ƙanensa ba. Wannan mota ta lalace a sakamakon wannan haɗari, shi kuwa ya samu fita / amma fa ba da alheri ba/, ta bakin Nomau Na Magarya, in ji Kassu Zurmi. Nan take ya zama marar mota. Tun a baiti na farko ya faɗa mana:

Yi zafi tafi kai iske ƙanen naka da kanka

Faɗa mai bari shakkar ka faɗa mai maganakka

Ta motakka da taf faɗi da kyar kaf fita kanka

Faɗa mai haɗari wanda ya faɗa bisa kanka

Ji ta ɓaci ƙwarai yanzu zama ba ta ɗagawa

 (Babban Bajini Bello Ƙanena)

Wannan shi ne farkon waƙar da Haliru ya rubuta domin ya shaida wa ƙanensa irin haɗari da hasarar da suka same shi. Haka nan kuma yana son ya samu taimako daga ƙanen, watakila ma ya samu wata mota don ga abin da ya ce ma ƙanen:

….

Sanin ka isa yas sa ni barin Gwaggo da Inna

In shawo firi in ga ka gamo na da cikawa

(Babban Bajini Bello Ƙanena)

To, a cikin wannan waƙa akwai wuraren da Haliru ya yi tsattsafin raha. Misali a baiti na 14 ya nuna cewa asalinsa ne kurum zai tuna ya kasa kiɗa taushi ga wannan ƙane nasa. Zancen wai Bello ƙanensa ne bai ma taso ba, mun kuwa san cewa a al’adar Bahaushe wa bai roƙon ƙane. To amma shi Haliru ya yi watsi da wannan al’ada. Shi kam gudun a ce ga Batoranke nan, kuma jinin Shehu Usmanu Ɗanfodiyo, yana kiɗa, shi ne kurum dalilin da ya hana shi ɗaukar kalangu ya kiɗa wa ƙanensa. Ga dai baitin wanda ta amfani da kirari da waskiya Haliru ya cusa ban-dariya cikinsa:

Babban bajini Bello ƙane ka zama wana

Haskenmu ɗiyan Baba ina son ka ga raina

Na Abbas bahagon Manuga walla maɗi na

Ba don asuli wanga da yah hau bisa kaina

Tabshi nika yo ma na kiɗi za ni kiɗawa

(Babban Bajini Bello Ƙanena)

Dubi yadda Haliru ya zaɓo kalmomi kamar /ɗiyan Baba/ da /ina son ka ga raina/ da /walla/ da /ba don asuli wanga/ da kuma /yah hau bisa kaina/, ya ƙirƙiro irin yadda Bahaushe na gidi (wato wanda Hausarsa ba ta gurɓata ba ko don zaman birni ko kuwa saboda tasirin ilmi) yakan bayyana ƙauna ga masoyinsa. Wannan zaɓi yana daga abubuwan da suka haɗu suka cusa raha cikin wannan baiti.

Wani misali daga waƙar shi ne baiti na ƙarshe:

Halir Alhaji Alƙali da yay yo shi na dauri

Shari’a jiya yay yo ta ga yau ya fita uri

Gidana nake can Wurno ina rangaɗa gari

Ga yau na fita na bar jama’an nan na Ilori

Nufina mu aje wagga da sauran furtawa

(Babban Bajini Bello Ƙanena)

Haliru ya ce ya / fita uri /. Abin da yake nufi shi ne ya hutar da kansa daga shiga cikin wahala da shirme yana ji yana gani, alhali ba wanda ya tilasta shi ya shige su tun da fari. A taƙaice dai ya ‘yantar da kansa. Wato aikin shari’a na alƙalanci irin na zamani wanda ya yi, aikin wahala ne da kuma wani ‘babban shirme’- a addinance. Aiki ne mai wuya, marar yanci, a wurin Haliru, ko da kuwa mai daɗi ne ga wasu. Daɗi da ‘yanci a wurin Haliru kam suna nan cikin gidansa a garin Wurno inda yake /rangaɗa(-r)/ garinsa. Da farko dai kalmar “rangaɗa” kalma ce da aka fi jin ta a bakin mata. Watakila maza za su fi amfani da kalmomi kamar “kwankwaɗa” da “shari” da “zuƙa” da “zuba” To, wannan amfani da kalmar da mata ne suka fi furta ta da kuma kwatancen bambanci da ya yi tsakanin alƙalanci da zama a gidansa, kai har ma da sukar da ya yi wa wasu mutane (watakila alƙalai), duk sun haɗu sun mayar da baitin mai ba da dariya.

Daga cikin waƙoƙin Haliru na soyayya akwai waɗanda suke ‘yan sakayau ne saboda jigogin ƙauna da kyawo ne suka mamaye su. Waƙar 'Soyayya Ruwan Zuma’14 da “Waƙar Habbi” suna daga cikin waɗannan waƙoƙi. Ya rubuta ‘Waƙar Habbi’ cikin samartakarsa, yana matashi ɗan kimanin shekara ashirin da bakwai.

Samartaka ta yi tasiri a kan wannan waƙa. To amma ko bayan ita akwai wasu salailai waɗanda suke da tasiri a kan shigar da raha ta yi cikin wannan waƙa. Na farko shi ne salon kamancen kasawa wanda shi kuma sai ya haifar da salon kambamawa. Bayyana matarsa a matsayin wadda babu wata mace da ta kai ta kyawo ko hali, ko dai duk wani abu mai daraja da za a danganta ga mata, magana ce mai ɓurɓushin ƙarin gishiri, wato kambamawa. A al’adar Bahaushe a ji irin wannan magana daga bakin namiji game da matarsa, dalili ne sat da ya isa a ce mutum mai saiɓi ne. Shi kuwa saiɓi a cikin al’adun Bahaushe yakan ba mai sauraren wanda yake yin sa dariya. ‘Waƙar Habbi’ tana cikin irin wannan tsari na saiɓi. Dubi wannan baiti mai cike da ban-dariya:

Ita af fara ko Azbinawa sun saki

In sun ga Habbi suna faɗin ba mu kai ba

(Waƙar Habbi)

A nan wai Azbinawa ne da kansu, waɗanda farar fata ce da su, kuma su ne Hausawa suka fi gani a matsayin fararen mutane, su ne da kansu suka sallama nan take da ganin matar Haliru, suka ce /ba mu kai ba/! Haliru bai yi amfani da lamiri ga’ibi na “su” a ƙarshen baitin ba, kamar yadda ya faro shi. A madadin haka sai ya yi amfani da lamirin “mu”. Wannan shi ya taimaka ga cusa raha cikin wannan baiti domin kuwa mai sauraren zai ji ainihin maganar da Azbinawa suka faɗa, ba wai cewa aka yi sun ce ba.

Wasu baitoci makamantan wannan, kuma tattare da saiɓi su ne:

Ni na yi begen Habbi ya kai Ummaru

Begenta cilas na garan ban so ba.


In ta shigo shigifa shi zan kuma ga duhu

Huskatta ah hitila duhu bai zam ba.


In Larabawa sun gane ta kira sukai

Ya aljamalu ɗiyanmu dub ba su kai ba.

Gashin idanun Habbi ba shi da lanƙwasa

Duba giratta ka so ta ko ba ka so ba

Tabshin jiki tabshin hali kyawon wuya

Kyawon ɗuwawu macce dut ba ta kai ba

Kwad damƙi damtsen Habbi ba shi baƙin ciki

Maganarta ta fi zuma ruwa ba su kai ba

Tsaye zamne Habbi irinta kam ba a gan ta ba

Na dubi mata ba kamar mahbuba

Mata ku hanƙura Habbi ta wuce macce dut

Halirunku Alhaji Wurno na ba wai ba.

(Waƙar Habbi)

Waƙoƙi Nauyaya

Waɗannan su ne waƙoƙin da suke ɗauke da jigogi ko saƙonni masu nutsar da hankali cikin tunani, masu kawo natsuwa, idan na addini ne su kawo tawali’u da taushin zuciya. Nauyin da ake nufi a nan bai nuni da muhimmancin waƙa ga mai saurare ko mai ita ba. Manufa ita ce a maimakon waƙar ta cusa masa raha sai ta saka shi cikin halin tunani da tsokaci da nazari da natsuwa da makamantan haka.

Waƙoƙin Haliru waɗanda suke cikin wannan rukuni sun haɗa da na ilmantarwa da na wa’azi ko nasiha, da na kishin ƙasa da wasu na soyayya, da na madahu da na addu’a da na addini gaba ɗaya. Haka nan kuma akwai na faɗakarwa da na suka ko gyaran al’umma da kuma wasu na mayar da martani da zambo,

Haliru ya rubuta wata waƙa mai suna “Waƙar Maƙiya Amada” wadda a cikinta ya yi wa waɗansu mutane zambo. Ga dukkan alamu wannan waƙa tana magana ne a kan mutanen da Haliru yake ganin ko kuma ya haƙiƙance cewa sun cuta masa. Saboda haka ko bayan zambo tana kuma ɗauke da addu’a da mayar da martani. A baiti na ɗaya da na biyu ne mawaƙin ya yi nuni da duk waɗannan:

Na yi nufi don haka zan tsarawa

In yi rubutu wada zan ganewa

In yi bayani wada zan shiryawa

Rabbu riƙa min wada ban kasawa

Ba ni mataki wada ban ƙallewa

 

Kai ka isa Jalla ina nan gun Ka

Na natsu kallo bisa dut aikinKa

Ban da dibara wata baicin bin Ka

Alamu dut ga mu cikin mulkinKa

Ba mu fita babu wurin ɓoyewa

(Waƙar Maƙiya Amada)

Duk da cewa Haliru ya danganta waƙarsa da cewa ta maƙiyan Allah ne masu cuta masa, sannan kuma duk da cewa ya haɗa da zambo cikin waƙar, waɗannan duk ba su hana salonsa na tsattsafin raha fitowa fili ba. Addu’a da zambo da mayar da martani kamar wada Haliru ya gabatar da su cikin waƙar, abubuwa ne nauyaya. Addu’a dai tana bukatar natsuwa da ladabi. Zambo kuwa yakan taƙalo fusata a yayin da mayar da martani kan bukaci game fuska da kuma fushi. To amma dubi waɗannan baitoci:

Babu mutum wanda ka yo ma sheɗa

Ba ni biyar mai riƙa hauyar huɗa

Mai mutuwa mai gajiya mai son ɗa

Mai taɓa nono ya laɓe mugun ɗa

Ba ka ganin ya biɗi Mai shiryawa

 

Tashi hawa sai ka ga ya sha maƙil

Wai ya waye ka ganai can fotal

Ya bar gashi da yawa ɗan buntsul

Ba shi ibada ƙwanƙil ɗan ƙwanƙil

Ba shi amini illa lecewa

 

Shi aj jaki ƙasa ya sha kabra

Shi a aura bana ya sha kora

Ya yi shige sun bugi ɗan jan gora

Ya sha murza ƙasa ya yo ƙura

Ba shi da ƙarfi wada zai tserewa

(Waƙar Maƙiya Amada)

A nan mawaƙin ya bayyana rashin dacewar biyar mutum a matsayin wanda ake yi wa ibada saboda dalilai da dama. To a wajen zana waɗannan dalilai ne Haliru ya cusa raha. Mutum dai mai riƙa hauya ne, wato manemin abinci. Mutuwa dole ta zo masa. Ga shi kuma mai rauni na gajiya kuma mai son ‘ya’ya, mai rauni a hannun mata. Zurfin ma’ana kalmar / laɓe / take da. Bai son a gane shi yana wannan aiki amma kuma ma’abucin aikata shi ne. Wata ma’ana ita ce mai tsananin rauni ne na ƙarfi da hankali bayan ya aikata ƙololuwar wannan aiki. Mutum dai abin renawa ne, kome nasa na ƙasƙasci ne saboda raunin da yake da shi. Muzi ke nan! Haliru ya muzanta ɗan Adam, abin dariya!

Daga wannan baiti na huɗu sai Haliru ya ɗora da zambo inda ya zayyana sifar abokin adawarsa. Ya yi amfani da kalmomi bi-ma’ana, /maƙil/ /buntsul/ da /ƙwanƙil ɗan ƙwanƙil/, waɗanda ke ƙoƙarin kawo yadda mashayin giya yake tafiya. Bayan haka sai kuma aka sake kawo maganar neman mata inda aka ce wannan abokin adawa kwarto ne, wanda dubunsa ta cika ya sha wahala a hannun waɗanda suka kama shi.

Muzantawa da zayyana tafiyar abokin adawa da kuma yi masa zambo kai tsaye duk sun taimaka wajen cusa raha cikin waɗannan baitoci.

Wani abin sha’awa cikin wannan waƙa shi ne cewa Haliru ko shi kansa bai bari ba wajen yin zambo, amma fa mai taushi, mai armashi. Wato zambon da aka gauraya da kirari, abin da nake son in kira zambo-kirari.15 Kawo wannan a cikin baitinsa shi ya haifar da tsattsafin raha. Ga baitin:

52Ban da ruhi Alhaji yas shirya ta

Wanga da yaz zan Gado sarkin wauta

Dankali sha kushe mijin ‘Yar Auta

Wurno gida Alhaji yas shirya ta

Na karu na ɗuru wurin roƙawa

(Waƙar maƙiya Amada)

Haliru ya kira kansa /Gado sarkin wauta/ da /dankali sha kushe/ da kuma mijin /yar auta, /, waɗanda dukansu suna ɗauke da kirari amma kuma mai ɓurɓushin zambo. Sai dai zambon ba mai cutarwa ba ne, nuƙurar da take cikinsa ba ta taka kara ta karya ba. Wautar da ya yaba kansa da ita a haƙiƙani ba wauta ba ce. Da ita yake yi wa maƙiyansa alka. Su suna ganin sa a matsayin wawa alhali tasu wautar ta fi tasa, idan har za a iya a kira ta haka nan. Haka kuma Haliru sha-kushe ne amma fa ya riga ya tsira kuma tilas a yi da shi ko da an kushe masa. Kushe bai yi masa kome.

Salon raha ya taka muhimmiyar rawa cikin waƙar Haliru mai ɗauke da wa’azi da nasiha ga Musulmi, ciki kuwa har da shi kansa, wato “Sabilul Haƙƙi Bi Ƙaulis Sidƙi”. Nauyin saƙon wannan waƙa da kuma kasancewarta mai tsawo16 suna iya gundurar da mai saurare ko karatun ta. To amma saboda amfani da wannan salo da mawaƙin ya yi sai gunduraswar ta ragu, idan har ba ta kau gaba ɗaya ba. Wannan shi ne muhimmancin salon a cikin waƙar. Wannan shi ne yanzu abin da wannan maƙala za ta duba, wato, tabbatar da samuwar salon a cikin waƙar.

 Haliru ya kawo hujjojinsa bayan ya ba mai sauraren waƙarsa shawara cewa kar ya nemi sanin addini daga malaman da suka kasance miyagu masu fallasa. Daga cikin waɗannan hujjoji akwai masu ɗauke da raha Misali, dubi waɗannan baitoci: G

Ƙurungu daɗai ga tabki in shina nan

Baƙin kifi da uri a nan faɗi na

 

Gida ko in akwai mussa ciki nai

Zaman kusu a nan shi kam ba’a na

 

Ruwa da wuta cikin kasko guda ɗai

Gudansu ka ɗaukaka ciki ɗan uwana

 

Masallacin kare kura ta zona

Ina liman kare yake in ya zona

(Sabilul Haƙƙi Bi Ƙallis Sidƙi)

Tunani a kan yadda kyanwa da bera za su zauna a wuri ɗaya kuma lami lafiya, shi zai ba mai sauraren waɗannan baitoci dariya, domin ya san cewa haka ba zai taɓa aukuwa ba. Mai saurare zai shiga mamaren kalmar da za ta bayyana rashin yiwuwar wannan zama. Haliru ne ya hutar da shi a ƙarshen baitin inda ya kawo masa kalmar / ba’a /, mai kaifin ma’ana.

Baiti mai ɗauke da raha cikinsa na biyu shi ne na 65, kuma kamar na 63 yake. To amma yadda aka cusa raha cikinsa ya bambanta da na farkon. A yayin da aka yi amfani da kalma mai kaifin ma’ana a na farko, a baiti na 65 tambaya mawaƙin ya kawo. Wannan tambayar kuwa ba ta bukatar jawabi domin yana nan ƙumshe cikinta. Duk wanda ya san taren kura da kare to kuwa ya san jawabin wannan tambaya. Ba su shan inwa guda. Kare naman kura ne. Ashe kuwa ko da shi ne ya gina masallaci da kuɗinsa kuma wasu suka zaɓe shi a matsayin limami, daɗewar wannan limanci nasa shi ne idan kura ba ta zo ba! Idan ta zo ba limanci ba, ko ma ya yi sallar a matsayin mamu ya san gatana ce don ba zai tsaya ba!

Waɗannan su ne hujjoji biyu da Haliru ya bayar. Fashin baƙin wannan shi ne samun koyarwar kirki daga miyagun malamai “faɗi” ne, “ba’a” ce, kuma babu tabbas ga ko akwai amfanin da za a iya a samu, sai dai aibi. Idan mai neman sani ya nemi ya san addini daga waɗannan malamai, to ya kwan da sanin cewa wanda ma ya riga ya samu zai salwanta, tabbas kamar yadda ta auku ga kare.

A cikin wannan waƙa Haliru ya yi magana mai yawa a kan aikin Alƙalin zamani. Ya soki shari’ar zamani. Haka kuma ya soki Alƙalan zamani. Cikinsu kuwa har da shi kansa. Hasili da kansa ya fara. Ya yi nadama, ya kuma yi tuba ga Mahaliccinsa Allah Mai gafara. Ya haƙƙaƙe cewa aje aikin Alƙalanci da ya yi babban arziki ne gare shi. A ganinsa Alƙalancin da ya yi babban kuskure ne kuma babbar ɓarna:

Wa man lam fasiƙi kake ka yi kufri

Dukan azzalumi Wuta za shi kwana

 

Zama shi wanda yaƙ ƙi ya yo hukumci

Na Allah kafiri na zalumi na

Ina hujjarka Alƙali Halir nau

Wane nassi gare ka na tabka ɓanna

 

Ƙisasi ba ka yi uznun bi uznin

Yadan bi yadin ka ce min ja’izun na

(Sabilul Haƙƙi…)

Cikin irin wannan magana mai nauyi ce Haliru ya yayyafa baitocin raha a wannan waƙa. Misali:

Da ɗarɗurinka ga ka da saulajani

Da zunnarinka zainul kafirina

 

Bale ƙiyyaru mai shafa ta hoda

Da barniɗa ji fullar kafirina

 

A sa gashi kamar namijin agwagwa

Ana bahasi da halshen zalimina

(Sabilul Haƙƙi…)

A nan Haliru ya kamanta shigar Cif Joji da siffar namijin agwagwa. Ban san wani kamancen daidaito mai ban-dariya da muzantawa wanda ya fi wannan ba!

Misali na ƙarshe da zan kawo daga wannan waƙa shi ne na da-na-sanin da Haliru ya yi lokacin da ya tuna da daular da ya yi a can da. A cikin baitocin da wannan misali yake mawaƙin ya kawo maganar ƙwazonsa na neman ya samu girma, da kuma shawarsa ta ya tara matan aure. Ya samu duka biyun. Yadda ya kawo wannan bayani tattare yake da haliyyar raha:

Biɗar girma biɗar in amri mata

Sabadda kwaɗan su niɗ ɗaukam ma kaina

Ji na tara su sun watse gaba ɗai

Ga yau sun bar ni fanko mulmulena

Ina nan duniya haka yak kasance

Bale can gobe ni nic cuci kaina

Aje su da na yi na yayo haramun

Suna lashe ta ni ko kuskure na

Ina ƙamnar su sun gudu sunka bar ni

Sakin wasu niy yi nif futad da raina

Bale su yi zamne tsufa ga shi ya zo

Inai musu mi ina ƙarfin jikina

Cikar ran kassuwa ta sunka yo min

Marece sunka watse min gidana

Sarautar ba ta ba samu na dauri

Bukata babu mi suka yi wurina

(Sabilul Haƙƙi…)

Dubi irin girma da samu da ni’ima waɗanda waɗannan baitoci suka ambata. Haka nan kuma dubi yadda baitocin suka bayyana salwantar da duk waɗannan ni’imomi suka yi. Sarauta ta tafi, ƙarfi ya tafi, tsufa ya kama, sannan matan nan duka sun tafi sun bar Haliru! Akwai tausayi ga jin wannan idan a zube aka rattabo shi. To amma a cikin waƙa mai tsattsafin raha aka yi rattaben. Ya yi amfani da salon kinaya ya kira kansa /fanko/ da /mulmule/, wato falalin dutsi. Kalmomin nan biyu na kinaya kalmomi ne masu kaifi da zurfin ma’ana gaba ɗaya. Kuma su ne suka sa baitin da suka fito cikinsa zama mai haliyyar raha. Haka nan kuma kalmar / lashe / tana da kaifin da ke bayyana kwaɗayin da matan Haliru suke da ga cin /’haramun/ ɗin da yake samo musu. Shi yana kan tafka kuskure, su kuwa suna murna da samun sakamakon kuskuren. Kalmar ce ta / lashe / ta barbaɗa ban-dariya cikin baitin.

Su kuwa baitoci na 215 da 217 ɗauke suke da salon tambaya domin su kasance masu cusa raha cikin ran mai saurare. A baiti na 215 tambaya biyu ne Haliru ya yi waɗanda ba su jiran jawabi domin yana nan tare da su, kuma shi ne “babu”. Shi kuwa baiti na 217 tambaya guda ce kuma makamanciyar na baitin da ya gabata. Dukansu dai masu ba mai saurare dariya ne.

Akan samu tsattsafin raha cikin waƙoƙin madahu kamar wada muka gani a cikin wƙoƙin wa’azi da nasiha. Waƙoƙin madahu dai su ne waɗanda aka yi a kan yabon Annabin Rahama, Muhammadu (S.A.W.). Saboda haka waƙoƙi ne masu bayyana tawali’u da nuna tsananin ƙauna zuwa gare shi tare da girmamawa mafificiya. A taƙaice waƙoƙi ne masu nauyi.

To amma duk da nauyin da waɗannan waƙoƙi suke da Haliru mai iya yin tsattsafin raha ne a cikinsu. Ya kuma san wuraren yin haka. Dubi waɗannan baitoci daga waƙarsa, “Jirgi”.

Yai hijira barin Makka dangi sun matsa mai

Za shi Madina Allahu yac ce mai hakan ga

Ya tafi Garba Siddiƙu sun tafi tare kogo

Su biyu sunka kwan ukku ko huɗu nan wurin ga

Kafirran da am Makka sunka bi swansu kogo

Ba su ganin su Allahu yaɓ ɓoye waɗanga

Sun tafi tare bokansu yac ce nan wurin ga

Ku duba nan ga kogon ga Ahmadu na wurin ga

Sai ɗai sunka duba ga kogo saƙe-saƙe

Ga yana da ƙwan kurciya ga kurciyag ga

 

Dut taron da an nan gaba ɗai sun yi zonai

Kafirran ga sun gane ƙaryar mai faɗin ga

 

Sai ɗai sunka ce mai Saɗifu irin hakan ga

Ƙarya ba mu ɗaukat ta ka mutu nan wurin ga


Kun san alkawal ba shi tashi sun kashe shi

Kun ga Saɗifu shi am musanyar Annabin ga

(Jirgi)

Haliru ya ba mu labarin Hijira cikin waɗannan baitoci. Wato lokacin da Annabi Muhammadu (S.A.W.) ya bar Makka zuwa Madina yana mai bin umurnin Mahaliccinsa. To bayan ya fita da shi da Sayyidina Abubakar sai kafiran Makka suka bi su da niyyar su kashe shi. To amma fa da bokansu suka bi Annabi (S.A.W.) Da ma kuwa bokan ya tabbatar musu cewa zai nuna musu inda Annabi (S.A.W.) ya ɓoye. Da ya nuna musu kogon da Annabi (S.A.W.) yake sai suka duba ba su ga kome ba in ban da yanar gizo-gizo da kurciya kusa da ƙwanta. Wannan mu’ujiza ce. Amma su ba su san da haka ba. Saboda haka sai suka fusata. Bokansu ya wahalar da su a banza ke nan. Nan take suka kashe shi.

 A baiti na 115 ne muka ji maganar da kafiran Makka suka yi wa Saɗifu, bokansu. A nan ne kuma Haliru ya cusa raha dangane da labarin da ya ba mu. To yadda maganarsu ta zo da kuma yadda maganar Saɗifu ta zo a baiti na 112, shi ya haifar da rahar. Shi dai Saɗifu da ƙarfafawa ya faɗi tasa magana, ba tare da wata shakka ba. Su ma da ƙarfafawa suka yi tasu kuma suka zartar da ita. Saboda haka ta amfani da salon hira Haliru ya ƙirkiro tsattsafin raha cikin waƙarsa.

Haka nan kuma tsakanin baiti na 122 da na 132 Haliru ya kawo bayani a kan Ɗan Mugira dangane da ƙiyayyar da ya nuna wa Annabi (S.A.W.). Ya kuma yi bayanin irin sunayen da Allah Maɗaukaki ya ba Ɗan Mugira, da yadda shi (Ɗan Mugira) ya yarda da dukansu in ban da guda. To yadda Haliru ya kawo waɗannan sunaye na zargi da yadda Ɗan Mugira ya yarda da su da ɗai ɗai, sai ga na ƙarshe ya yi musu; da kuma yadda Haliru ya kira shi, sun taimaka ainun wajen gina tsattsafin raha. Haliru ya ce:

Allah yaf faɗa mai saboda takabburatai

Hammazin namimin ji ba shi musun hakan ga

Massha’in wurin hairi manna’in matcaci

Allah yaf faɗa mai asimin duniyag ga

An ce Ɗan Mugira utillin mu’utadin na

Dut ya amsa sunansa ba shi musun batun ga

Sannan anka ce mai zanimin ɗan shige na

Shi ɗai yam musanya ma shegen duniyag ga

An ce tsohuwatai ga layi tai cikinai

Tal liƙa ma tsohon da yag gada gidan ga

(Jirgi)

Kalmar / matcaci / a baiti na 128, da / ɗan shige na / da / shegen duniyag ga / a na 130, musamman sun fi ƙunsar raha saboda takaicin da Haliru yake ji wanda kuma ya nuna cikin wannan zagi da ya nanata wa Ɗan Mugira, kamar wada Allah ya kira shi. Sannan kuma labarin da Haliru ya kawo a baiti na 131 ya ƙara kafa rahar.

Idan kuma aka dubi waƙoƙin da Haliru ya rubuta na yabon mutane, a nan ma akwai tsattsafin raha. A waƙar da ya yi ta yabon Sarkin Musulmi Abubakar III akwai waɗannan baitoci:

Ɗan Musulmi in dai Musulmi na

Ya sani ɗan Sarkin Musulmi na

Wa ka zagin tsofonsa zan shi na

Ban batun wancan shi kurege na

Fatiha ma bai i da ƙarshenta

Wanga Sarkin ɗa na karimi na

Ko da dai sun ɓoye sharifi na

Tabbata Bubakar ɗan waliyyi na

Hattara kila ma shi waliyyin na

Don akwai hanyoyin alamunta.

Wa ka ja mai wane na ka gasa tai

Wa kai i mai wane na ka tausa tai

Ba kamatai ko an yi tono nai

Ba irinai ra’ayi da hangenai

Ko’ina na maganag ga in yo ta

 

Son zumuta da hani da alheri

Ga zalaƙa kuma ga shi ba kibri

Ga sakin fuska ga shi mai sabri

Ga amana koyaushe ba sharri

Ƙeta ko can bai gane sunanta

(Safiya Da Gaskiya Taka Aiki)

Karanta ko sauraren waɗannan baitoci kan iya sa mutum ya ji kamar babambaɗe ne ya sa Sarkin Musulmi gaba yana furta su. Wato kamar kirari kumburau17 ne ake yi ma Sarkin Musulmi, shi kuwa kirari sai in akwai raha ake iya yin sa. Haka nan kuma wanda aka yi wa shi, an yi ne domin ya shiga wani nau’i na raha kafin ya kai ga kumburewar. Haliru ya yi nasarar kawo wannan tunani ga zukatan masu sauraren waƙarsa, tare da cusa raha cikinta ta hanyar zaɓen gaɓoɓi masu bukatar a fara furta su da sauti mai ƙarfi. Waɗannan gaɓoɓi kuwa sun zo ne a farkon kowane ɗango in ban da ɗango na ɗaya na baitin ƙarshe. Gaɓoɓin su ne ɗan da ya da wa da ba da fa da ta da wa da ga da ko da kuma ƙe. A wasu wurare ma kalmomin da suka ƙunshi waɗannan gaɓoɓi su ma da ƙarfi ne ake furta su. Misali, kalmomin tabbata da hattara.

Bayan wannan siga ta kirari akwai kuma shammata ko zambo da kuma salon kambanawa. A baiti na farko an yi amfani da salon kinaya ga wani mutum wanda yake zagin Sarkin Musulmi, aka kira shi “kurege”. Sannan kuma aka ce ba ya iya karanta Fatiha duk kuwa da cewa shi Musulmi ne. To a waɗannan ɗangogi biyu ne shammatar take. A nan kuma ban-dariya take saboda da ma akan yi shammata ne domin a yi dariya.

A baiti na ƙarshe Haliru ya yi amfani da salon kambamawa a ɗangon ƙarshe inda ya ce Sarkin Musulmi bai san kalmar ƙeta ba sam sam, balle daɗa ya san ƙetar ko ya aikata ta! Wannan salo na kambamawa da Haliru ya yi amfani da shi shi ya girka kirarin da muka ambata a kan ƙololuwar matakin kumburarwa. Shi kuma zai haifar da ban-dariya cikin baitin.

Haliru Wurno ya rubuta waƙoƙin soyayya a kan matansa. Wasu daga cikin waƙoƙin ‘yan sakayau ne, kamar waƙar “Soyayya Ruwan Zuma”, a yayin da wasu suka kasance nauyaya. ‘Waƙar Hassi’ wadda a haƙiƙanin gaskiya waƙa ce a kan soyayya da zaman aure a kan matan da ya aura, musamman wata da ake kira Hassi. To ita wannan waƙa tana daga cikin waƙoƙinsa na soyayya nauyaya. A cikinta Haliru ya kawo sunayen matan da ya taɓa yi da kuma halayensu waɗanda suka zama dalilan rabuwa da su. Wasu daga waɗannan dalilai masu ban tausayi ne, kamar yi masa sammu ko kwarce, wasu kuwa na tashin hankali da ɓacin rai kamar faɗa da shi ko ‘yan uwansa. Haka nan kuma akwai dalilan da suka shafi addini, kamar rashin yin salla da ƙazanta.

To, ɗaya daga cikin matansa ita ce Hassi, ga kuma abin da ya ce a kan ta:

Nata kwarce ya hau ni na ji shi

Na yi kuka rabuwarmu an ji shi

Na bi ko sawun Hassi domin shi

Ba ta nan kam halinta ta bar shi

Ba ni ƙamna tai ba ni begen ta.

 

Ta yi tashi na bi ta har daji

Na yi kwana da sununta har jibji

Na ɓakalkalce sai ka ce tuji

In dare na in rana har daji

Na yi kukan ‘yar Amma kwarcenta

Sai da nig gane na fice jama’a

Dariya ta aka yi ina far’a

Sai a ce ai Hassi akwai ɗa’a

Na yi roƙon Allah ya ban sa’a

In sakat ko raina ya ɗan futa

(Waƙar Hassi)

Baiti na 35 ya fito fili ya faɗi sakamakon abin da Haliru ya ce ya kasance a baiti na 30. A baiti na 30 ya ba mu labarin yadda ciyon so ya kama shi wanda a ganinsa ciyon kwarce ne. Ya bi Hassi ko’ina. Yar bar gidansa ya nufi dawa wai a zatonsa Hassi tana can. Haka nan kuma a wajen dakon ya gane ta ya ɓata darensa a wurin da bai dace ba, a juji. Watakila saboda babu wani wuri da zai raɓe in ban da juji! Hassi dai tashi ne ta yi amma maimakon Haliru ya yi abin da al’ada ta shimfiɗa, shi da kansa ya tafi biko ta! Wannan hali ne irin na son maso-wani. Yadda kuwa Haliru ya ba mu labari shi ne zai ba mu dariya, musamman kwanan da ya yi a juji. Haka nan kuma yadda ya kammala baiti na 35 da fatar cewa ransa zai samu hutu idan Allah ya ba shi sa’ar sakin Hassi, abu ne mai ban dariya. Haliru ya kasance mai tsananin son Hassi. Saboda son da yake yi ma ta har a juji ya kwana. To amma ga shi ya gane ashe kwarce ne ta yi masa. Wuya!! Saboda haka sai ya roƙi Allah sauƙi domin ransa ya samu ya huta! Ya dai gaji, ya gane!!

A waƙarsa ta tarbiya wadda tana cikin waƙoƙinsa na gyaran al’umma ko suka ga munanan halaye, Haliru ya surka da tsattsafin raha domin ya isar da wannan saƙo. A cikin waƙar ya yi bayani cewa ummul haba’isin taɓarɓarewar tarbiyya a ƙasar Hausa su ne shugabanni. Shugabanni kuwa a ganinsa sun haɗa da masu mulki da malamai da kuma masu hali. Su ne suka aza yara ga hanyoyin rashin tarbiyya. Su ne mayaudara waɗanda aka danƙa wa amanar dukiyar jama’a amma suka ci ta. Malamai ne suka yi watsi da tsoron Allah da ƙana’a, suka rungumi fadanci ga masu mulki da kuma kwaɗayin abin duniya. Haliru ya bayyana halayen waɗannan malamai a matsayin tushen rashin tarbiyya inda yake faɗin.

Mis sa haka wai ba a lura ba

Amsar rashawa ba a bar shi ba

Yau mallammai su ag gaba

Su ci hanci had da bugun gaba

Imani ya fita zucciya

Shafin kwalli ko karuwa

Ga biɗar mata ‘yan ga-ruwa

Da gida daji ko anguwa

An san haka balle karuwa

Wannan ita ak kan angaya.

 

Wa’azin mallammai don mitin

 Dammu Salmu matan kicin

Malam Alaramma da tai wurin

Ɗakinai Zainabu ga ta can

Shi kirat ta fito ta yi mazaya

13.Sannan Larabci za su yi

Bi ta’ala huna shayi ki yi

Ita ko ta yi mai wani masgayi

Bil aini walau shi ma shi yi

Manyan mallamman duniya

(Waƙar Yin Tarbiyya)

Yadda Haliru ya siffanta malami mai shafa kwalli domin matan banza su yi sha’awar sa, da yadda su kuwa matan (kamar Zainabu) suke jan hankalinsa ta hanyar motsi da jikinsu, da kuma yadda ya siffanta shi tare da kawo yadda yake juye baki zuwa harshen Larabci domin kada na kusa su gane, duk waɗannan dabaru ne na cusa raha cikin waɗannan baitoci. Lalle kam sukar da Haliru ya yi a waɗannan baitoci mai kaifi ce. To amma duk da wannan kaifi, baitocin sukan ba mai saurare dariya, musamman Larabcin da Haliru ya ce malamin ya yi.

Irin wannan amfani da baƙon harshe ne Haliru ya yi a wata waƙa inda yake yin kira ga Hausawa su kula da al’adunsu. Ya riƙa kawo kalmomin Ingilishi cikin baitocinsa domin a fahimci manufarsa. To amma fa kawo waɗannan kalmomi yakan ba mai saurare dariya domin ƙoƙarin muzanta masu dangantaka da su da baitocin suka fito suke yi. A cikinsu Haliru ya nuna wasu al’adu da yara matasa suka ɗauko daga wasu ƙasashe. Ya ce hatta su ƙasashen na waje daga baya ne suka tsiri waɗannan munanan al’adu. Haka nan kuma Haliru yana ganin cewa iyaye da malamai ne suka kai yara ga irin waɗannan munanan al’adu. Ga dai kaɗan daga waƙar:

20Suna cewa da an waye duhun kai

Zama wai yanzu gayu ne abutta

Akwai kuma har da Human Rait wajen su

Ga kowa na da ‘yancin kanshi ƙatta

 

A nan aka samu tsohon bai da iko

A kan ɗa sai da yardar ɗan ji wauta

Iyayen yara su suka ɓata yara

Ga tarbiyyad da su haka nif fahimta

Ɗabi’ar ƙetare da ɗiyan ka yin ta

Uwaye su ka sa su suna ta yin ta

 

Su sai mu su ‘yan tufafi ‘yan matsattsi

A tanke tsara da bel tamkar biri ta

 

A sai feskap baƙar hulla a sanya

A bar zancen ta saƙa wa ka son ta

 

A ba su baƙin madibi shi ka daidai

Da no raspet a ba su su sa fitarta

 

A yo gaye a sanya baƙi ga gashi

A yo askin ga fonk askin mugunta

 

Ana yawo da kai sake babu hulla

Ana wani tsalle wai na gudun ƙazanta

 

Bale mata idan sun shace gashi

Ji ɗan kwalin ga hannu ake riƙe ta

Wajen ilimi a can ne yay yi tushe

Kujerin ‘yan maza a haɗe da mata

 

A ce wai diskashin aka yi tsakani

Ga al’adarmu sam haka ba irinta

(Muhimmancin Al’adunmu…)

Kammalawa

ƙoƙarin da wannan maƙala ta yi na ta nuna cewa salon tsattsafin raha shi ne salon marubuci na gaba ɗaya a cikin waƙoƙin Alƙali Alhaji Haliru Wurno, maƙalar ta kawo misalai daga waƙoƙi da dama kuma mabambanta ta fuskar jigoginsu. Waɗannan waƙoƙi sun kasu gida biyu: waƙoƙi ‘yan sakayau da waƙoƙi nauyaya. An karkasa su ta wannan fuska domin a nuna cewa ko a waƙoƙin da ake sa ran babu kafar shigar da raha, Haliru yana iya ya kawo ta ba tare da ya raunana waƙarsa ba.

Haka nan kuma an kawo tarihin Haliru domin ya kasance wata manuniya ga dalilin da ya sa ake samun tsattsafin raha a cikin waƙoƙinsa. A ganina halin Haliru na rashin yarda da matsala ta tauye shi, kome tsananinta kuwa, shi ne ya yi tasiri a kan rayuwarsa gaba ɗaya, ciki kuwa har da kasancewarsa mutum mai raha da fara’a a ma’amalarsa da kuma rubuce-rubucensa na waƙoƙi.

 Salon tsattsafi na raha cikin waƙoƙin wannan bawan Allah inuwa ce ta halinsa mafi rinjaye a rayuwarsa. Halin kuwa shi ne ƙin barin matsala kome tsananinta ta tauye shi, halin da mai ilmi irin Haliru, tushensa shi ne tawali’u da tawakkali ga Allah Ma’ishin bawa ga kome.

Wannan maƙala wani yunƙuri ne na zurfafa nazari cikin sigogin waƙa musamman haliyya wadda har yanzu ba ta samu kulawar manazarta sosai da sosai ba. Nazari a kan haliyya cikin waƙoƙi wani fage ne da zai iya taimakawa wajen wasa ƙwaƙwalwa da kaifafa tunani. Ya kamata a yanzu a ga ɗaliban waƙoƙin Hausa sun fara maye hanyar rattabe da ta motsa ƙwaƙwalwa da kutsawa cikin surƙuƙin tunanin mawaƙi. Ɗaya daga waɗannan hanyoyi ita ce nazarin haliyya cikin waƙa.

Tushen Bayani

1. Duba maƙalar Abdulƙadir Ɗangambo (1981) “ Ɗaurayar Gadon Feɗe Rubutacciyar Waƙar Hausa”, wadda ya gabatar a Taron Ƙara Wa Juna Sani na Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Bayero, Kano, shafi na 12-13.

2. Domin ƙarin bayani game da haliyya duba maƙalar Abdullahi Bayero Yahya (1984) “Haliyya Cikin Waƙa”, wadda ya gabatar a Taron Ƙara Wa Juna Sani na Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Sakkwato (yanzu Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo) Sakkwato, musamman shafi na 1-3.

3. Marubucin wannan maƙala ya fara saduwa da Alƙali Alhaji Haliru Wurno tun a farkon gomiyar 1970. To amma a lokacin sanin nesa ne domin bambancin yawan shekaru da lalurar zuwa makaranta ta marubucin maƙalar. Daga 1981 ne suka samu shaƙuwa da juna duk kuwa da cewa ‘yan uwan juna ne.

4. Liman Abdulƙadir Macciɗo ke nan, limamin Masallacin Sarkin Musulmi Muhammadu Bello. Ko kafin wannan mashahurin malami ya karantar da Alƙali Alhaji Haliru Wurno, ya karantar da wasu kakanninsa da babanninsa. Waɗannan sun haɗa da Waziri Junaidu ɗan Waziri Muhammadu Buhari da Yahya Nawawi ɗan Waziri Abdulƙadir Macciɗo. Domin ƙarin bayani duba Hamidu Alƙali (2002) The Chief Arbiter: Waziri Junaidu and His Intellectual Contribution, Kaduna: Baraka Press and Publishers, shafi na 30-36, littafin da mai wannan maƙala yake kan fassarawa da sunan ‘Shugaban Maslaha’.

5. Wannan ƙane shi ne Sambo Yahya Nawawi. Lokacin da zai fara tafiya makarantar sakandare ta garin Tangaza, mahaifinsa ya rubuta wasiƙa zuwa ga Haliru Wurno yana mai cewa, “… ga ƙanenka nan ka kula da shi game da karatunsa, na gida da na boko - - - “ Karatun gida a nan yana nufin karatun sani na addini. 

6. A shekarar 1994 marubucin wannan maƙala ya gayyato wa ɗalibansa na ALH.312 Haliru Wurno domin su tattauna da shi a kan tarihinsa da waƙoƙinsa da ma waƙa gaba ɗaya. An yi wannan saduwa ranar 08/01/1994 kuma an ɗauke shi hoto, an kuma ɗauki wasu waƙoƙin da ya rera cikin kases na rikoda.

7. Cikin hirar da ya yi da ɗaliban kwas na ALH 312 a shekarar 1994 a Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato, ranar O8/ 01 / 1994.

8. Wato Malam Musa Abdullahi Zariya wanda aka sha yin hira da shi a kafafen watsa labarai kamar Sokoto State Television (S.T.V.) (yanzu Rima Television, R.T.V.), da gidan telebijin na Nijeriya a Sakkwato (NTA). Mutum yana ƙare faɗa masa lisafin da yake bukatar amsarsa shi kuwa Ka-Fi-Komfuta-Sauri zai faɗi amsar. Mai wannan maƙala ya taɓa tambayar wannan bawan Allah yadda amsoshi suke zo masa ba tare da ɓata lokaci ko wahala ba. Sai ya amsa da cewa shi kansa bai sani ba illa haka kurum yake ganin amsar a gabansa, wato a idon zuciyrsa!

9. Duba Abdullahi Bayero Yahya (1987) ‘The Hausa Verse Category of Madahu With Special Reference To Theme, Style And The Background of Islamic Sources And Belief”, kundin digiri na Ph.D (Hausa), Sokoto: Jami’ar Sakkwato (yanzu Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo), shafi na 398 don ƙarin bayani. Haka nan kuma Mohammad Aminu Ibrahim (1984), ‘Alƙali Alhaji Haliru Wurno Da Waƙoƙinsa’, kundin digiri na B.A., Sokoto: Jami’ar Sakkwato, shafi na 15

10. Misali, marubucin maƙalar nan ya samu wata waƙar madahu a wurin Haliru mara suna, alhali ya mallaki “Korama da “Jirgi” da kuma ’Gulbi’. Da ya tambayi Haliru sunan wannan waƙa sai ya amsa da cewa, ‘To ai sai ka ba ta sunan, duka ɗai na” A nan ne ya ba mawaƙin shawarar a ba ta suna “Filafili” saboda an riga an samu “Ƙorama” da Jirgi” da kuma Gulbi, sai kuma Haliru ya aminta da haka.

11. Salon shillo shi ne yin jerangiya da wani jigo(wata magana) a farkon waƙa kuma jigon ya kasance ba shi ne ainihin babban jigon waƙar ba amma kuma daga bisani sai mawaƙi ya ƙulla su. Domin ƙarin bayani duba Abdullahi Bayero Yahya (2001) Salo Asirin Waƙa, Kaduna: FISBAS, shafi na 113 – 4

12. Jinsintarwa kamar wada Abdulƙadir Ɗangambo ya ba da shi salo ne wanda ‘mawaƙi yakan ɗauki wasu halaye, siffofi, darajoji da sauransu da mutum ne kawai aka sani da su, a laƙaba wa wani abu marar rai ko dabba, tsuntsu, ƙwaro da sauransu. To amma wani lokaci abin yakan zama akasin haka”. Saboda haka sai ya kasa wannan salo zuwa kashi uku; mutuntarwa da dabbantarwa da abuntarwa. Dubi maƙalarsa (1981) ‘Ɗaurayar Gadon Feɗe Rubutacciyar Waƙar Hausa”, a ƙarƙashin ‘Mutuntarwa’, shafi na 14. Haka nan kuma a cikin Salo Asirin Waƙa da kuma “Siffantawa Bazar Mawaƙa: Wani Shaƙo Cikin Nazarin Waƙa” cikin Audu Yahya Bichi da wasu (2002), Studies In Hausa Language, Literature And Culture 5, Kano: Centre For The Study Of Nigerian Lanuages, shafi na 226, an kira wannan salo da sunan jinsarwa.

13. Duba Abdullahi Bayero Yahya (2001) T.D.A.S. shafi na 108 – 113.

14. Akwai cikakkiyar wannan waƙa cikin Ahmed Abdullahi Sokoto (1998) ‘Soyayya Ruwan Zuma: Nazari Da Sharhi Kan Wasu Rubutattun Waƙoƙin Soyayya A Sakkwato’, kundin digiri na M.A. (Hausa), Sokoto: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, shafi na 133-135.

15. A nan ina kwaikwayon Aliyah Adamu Ahmad (2003) “Nazarin Zambo- Zagi A Adabin Hausa: Tsokaci Kan Siyasar Arewacin Nijeriya (1950-1966)” kundin digiri na M.A. (Hausa), Sokoto: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, inda ta yi amfani da abin da ta kira salon zambo-zagi.

16. Wannan waƙa nusuha biyu take da su. Shafukan nusuha ta farko ba su cika ba amma sun ƙunshi baiti 166. Wasu shafuka ne suka salwanta domin shafin ƙarshen takardun shi ne na 12 kuma yana da ja-makafi da ( بيا الله). Nusuha ta biyu kuma wadda nake ganin ita ce ta biyo baya, tana da baiti 251 da kuma tammat, wanda ya nuna cewa wannan nusuha cikakkiya ce. Ita ma shafuka goma sha biyu ne take da, sai dai takardunta sun fi tsawo da kuma ɗaukar baitoci, Kowane shafinta in ban da shafin farko yana da baiti 22. Na farkon yana da 17 saboda Bisimilla da kuma sunan waƙar. Nusuha ta ɗaya tana da baitocin da yawansu yake sauyawa daga wannan shafi zuwa wancan, sai dai babu shafin da yake da fiye da baiti 16. Tsakanin 10 da 16 suke ɗauka.

17. A nan ina kwaikwayon Atiku Ahmad Dunfawa ne inda ya karkasa zuga zuwa zuga kumburau, da zuga kariyau da zuga ingizau, duba maƙalarsa (2002) “Zuga A Waƙoƙin Fada’, wadda ke a kan hanyar bugawa. Kirari dai babbar manufarsa ita ce kwarzantawa da zugawa.

Manazarta

1. Alƙali, H. (2002) The Chief Arbiter: Waziri Junaidu And His Intellectual Contribution, Kaduna: Baraka Press and Publishers.

2. Ahmad, A. Aliyah (2003), ‘Nazarin Zambo-Zagi A Adabin Hausa: Tsokaci Kan Siyasar Arewacin Nijeriya (1950-1966), kundin digiri na M.A. (Hausa), Sokoto: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

3. Ɗangambo, A. (1981) “Ɗaurayar Gadon Feɗe Rubutacciyar Waƙar Hausa”, maƙalar da aka gabatar a Taron Ƙara Wa Juna Sani na Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya, Kano: Jami’ar Bayero.

4. Dunfawa, A.A. (1987) “Zuga A Waƙoƙin Fada”, maƙalar da aka gabatar a Taron Ƙawa Wa Juna Sani na Sashen Harsunan Nijeriya, Sokoto: Usmanu Ɗanfodiyo, kuma tana kan hanyar bugawa.

5. --------------- (2002) “Waƙa A Tunanin Yara”, kundin Digiri na Ph.D, (Hausa), Sokoto Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

6. Sokoto A.A. (1998) “Soyayya Ruwan Zuma: Nazari Da Sharhi kan Wasu Rubutattun Waƙoƙin Soyayya A Sakkwato”, kundin digiri na M.A. (Hausa), Sokoto: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

7. Furniss, G. (1996) Poetry, Prose And Popular Culture In Hausa, Edinburgh: Edinburgh University Press.

8. Bunza. A.M. (2003) “Ibarahim Yaro Yahya A Mizanin Hasabi: Mamaren Ƙyallaro Ɗabi’unsa Da Shahararsa A Mahangar Malaman Hisabi”, cikin Ɗegel: Journal Of The Faculty Of Arts and Islamic Studies VI, shafi na 266-275, Sokoto: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

9. Yahya, A.B. (1984) “Haliyya Cikin Waƙa”, maƙalar da aka gabatar a Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya, Sokloto: Jami’ar Sakkwato.

10. -------------- (2001) Salo Asirin Waƙa, Kaduna: FISBAS Media Services

11. -------------- (2003) “Kana Shire Baban ‘Yan Ruwa Na Bello Jikan Ɗanfodiyo: Waƙa A Kan Guri Da Hange Da Dahir”, cikin Ɗegel: Journal Of The Faculty of Arts & Islamic Studies VI shafi na 252 – 265, Sokoto: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

12. ------------ (2002) “Siffantawa Bazar Mawaƙi: Wani Shaƙo Cikin Nazarin Waƙa”, cikin Studies In Hausa Language, Literature And Culture V, shafi na 220 – 240, Kano: Jami’ar Bayero.

13. Wasu waƙoƙin Alƙali Alhaji Haliru Wurno waɗanda mai wannan maƙala ya samu daga hannun mawallafinsu. Waɗannan waƙoƙi da ajami aka rubuta su kuma da hannun Haliru.

Post a Comment

0 Comments