Ticker

6/recent/ticker-posts

Shaƙo Uku A Gulbin Waƙa: Faɗaɗawa A Nazarin Waƙoƙin Hausa

  Daga taskar Farfesa Abdullahi Bayero Yahya.

Abdullahi Bayero Yahya
Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya
Jami’ar Usmanu ƊanfodiyoSakkwato
Email: 
bagidadenlema2@gmail.com 
Phone: 
 07031961302

Tsakure

A ƙoƙarin yin nazarin sabon fannin ilmi ga al’ummar da ke fafutukar bunƙasar da shi ta yadda ya shafe ta domin ta cimma tsara, musamman idan har ta yi nisa ga tattara abubuwan da suke a zahiri na fannin, to hanya mafi dacewa ita ce ta mayar da himma kan zaƙulo abubuwan da suke a ɓoye. Zaƙulo waɗannan abubuwa da ke a ɓoye ko ƙirƙiro waɗanda da can ba a san su ba amma suke iya kwarzanta fannin, yunƙuri ne da sai an tsananta natsuwa tare da zurfafa bincike ake iya gano su sannan a iya faɗaɗa wannan fanni har ya yi rahhu. Wannan maƙala tana yin nuni ne da cewa a yanzu ya kamata nazarin waƙoƙin Hausa ya fuskanci zaƙulo sigogin waƙoƙin da masana da manazarta fagen ba su wada bankaɗo ko haskaka su ba. Maƙalar ta zaƙulo malamai uku na nazarin adabi, musamman na waƙoƙin Hausa, waɗanda daga cikin nazarce-nazarcen da suka yi sun duƙufa a kan wannan hanya ta shaƙo da fitowa da ayyukan da suke lu’ulu’u ne mai kwarzanta nazarin waƙoƙin. Ta gabatar da abubuwan da suka ƙirƙiro ko suka gano, sannan ta yi tsokaci a kansu don ɗalibai su samu hasken ƙalailaice su ko su zurfafa bincike da zimmar su ma su fito da wani abu sabo a nazarin waƙoƙin Hausa na baka da rubutattu, wato su ma su shaƙo wani lu’ulu’u cikin gulbin nazarin. Maƙalar tana a kan koyarwar Farfesa Ɗalhatu Muhammad da ke ƙoƙarin ƙwaƙwalo sabon abu ko ƙara haskaka abin da ba a riga aka fahimce shi sosai da sosai ba.

1.0    Gabatarwa

A farko-farkon rubuce-rubucen da ɗaliban jami’o’i da manyan makarantun gaba da sakandare suka yi domin samun takardun shaidar kammala makarantun, galibin nazarinsu ya fi ƙarfi ne wajen rattaba abin da suka yi bincike da nazari. Sukan ɗauki mawaƙi ɗaya sai su gabatar da taken binciken da za su gudanar wanda kan ƙunshi kalamai kamar “Rayuwar Malam Buba da Waƙoƙinsa”, ko “Jigogin Waƙoƙin Alhaji Abdullahi Birnin Hutawa”, ko kuma “Taskace Waƙoƙin Makaɗa Zaune”.

Babu laifi ga irin wannan nazari ko bincike ko ƙalilan, saboda ko babu komi, da ba a yi su ba da kuwa waƙoƙin magabata tuni sun ɓace. Nasarta a cikin ranka cewa manazarta kamar Ɗandatti Abdulƙadir (1975) da Ɗalhatu Muhammad (1977) da Abdulƙadir Ɗangambo (1980) da Bello Sa’id (1978; 2002) da Sutura Sa’idu Mukoshy (1979) da Sa’idu Muhammad Gusau (1983; 1988) da sauransu masu ɗimbin yawa ba su yi waɗannan ayyuka ba, haƙiƙa da maƙalu ire-iren wannan da take a gaban mai karatu ba su samu ba. A ganin mai wannan maƙala da tunanin rubuta ta bai ma tusgo ba. Babban abin da maƙalar ke son ta yi ishara da shi, shi ne irin wannan bincike na shaƙo kasancewar wani lu’ulu’u cikin nazarin waƙoƙin Hausa yana da fa’ida sosai. A marrar da nazarin waƙoƙin Hausa yake ciki a wannan zamani, lokaci ya yi ga manazarta na su mai da hankali kan zaƙulo ko ƙirƙiro abubuwan da za su ƙara kwarzanta da faɗaɗa nazarin. Haƙiƙa tun tuni ne lokaci ya yi da ya kamata masana da manazarta su gurgusa daga ilmantar da mu yawan waƙoƙin wane da wane ko jigogi kaza da kaza su ne ke cikin waƙa kaza ko waƙoƙin wane da wane, amma fa ko kusa ba wai su kawar da idonsu ko ƙoƙarinsu gaba ɗaya daga irin ayyuka da magabatan da aka ambata ɗazu suka yi ba. A’a, bukata dai ita ce su ƙara sa ido, da ƙwaƙulo, da ƙirƙiro sabbin hajojin kwalliyar nazarin waƙoƙin Hausa, kuma masu kaifafa tunanin duk mai nazarin ayyukansu.

Wannan lura ko kira ba yau ne aka fara shi ba. Manazarta waƙoƙin Hausa a yau suna sane da cewa ita wannan hanya ita ce wadda sanannen malamin nan na Jami’ar Ahmadu Bello a Zariya, Farfesa Ɗalhatu Muhammad, Allah ya yi masa rahama, ya goya ya kuma shahara da ita a nazarin adabi, musamman na waƙoƙin Hausa.

Tunani na shaƙo wani lu’ulu’un nazarin waƙoƙin Hausa, tunani ne ko hanyar da, a iya binciken da mai wannan maƙala ya yi, ta samo asali ne daga Farfesa Ɗalhatu Muhammad. Shi ne malamin nazarin waƙoƙin Hausa wanda ya fara yunƙurin Hausantar da nazarin Hausa a jami’o’in ƙasar nan, ta hanyar zaburar da masana don samar da kalmomin fannu na nazarin Hausa. Ya fara wannan ƙoƙari ne lokacin da yana aiki a Jami’ar Bayero, Kano inda ya samu haɗin kan sauran malaman Cibiyar Nazarin Harsunan Nijeriya da Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, har aka yi taron ƙara wa juna sani don samar da kalmomin nazarin adabi a 1973. Shi ne ma wanda daga baya ya tace sakamakon wannan taro har ya gabatar da maƙalar da ya kira ‘A Ɓocabulary of Literary Terms in Hausa’. Tun a wannan lokaci ne wannan taliki mai tsananin hangen nesa da basira ya ci gaba da share wa manazarta adabin Hausa, musamman a fannin waƙa, hanyar nazarin waƙa.[1]

 Ɗalibansa da dama, kamar Abdulƙadir Ɗangambo, sun zo sun rungumi hanyar. Shi kuma Ɗangambo sai wasu ɗalibansa ciki har da Sa’idu Muhammad Gusau da mai wannan maƙala, da ya koya musu bin wannan hanya yin ta nuta da shaƙo, sun zo suka are, suka goye kuma suka talle ta raɗam. To wannan maƙala, domin ta ba da haske kan wannan hanya ta Ɗalhatu Muhammad ta yi ƙoƙarin kawo ayyukan malamai uku a matsayin misalai.

Malamai uku ɗin da maƙalar ta kawo ayyukansu uku kuwa sun fito ne daga jami’o’i biyu da ke cikin Birnin Sakkwato, Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo da Jami’ar Jihar Sakkwato. Malaman su ne Farfesa Atiku Ahmad Dunfawa da Farfesa Bello Bala Usman da kuma Majiɓinciyar Farfesa Aliyah Adamu Ahmad. Malamai biyu na farko daga Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo suke yayin da ita kuwa Aliyah ta fito daga Jami’ar Jihar Sakkwato. Abin lura da sha’awa game da waɗannan malamai shi ne dukansu suna daga cikin waɗanda suka samu tasirin marigayi Farfesa Ɗalhatu Muhammad kai tsaye ko kuma ta samun tasiri daga waɗanda suka samu tasirinsa kai tsaye. Biyu na farko su suka samu tasirinsa kai tsaye, ta ukun kuwa ta samu tasirinsa daga ɗalibinsa, Ɗangambo, da Gusau, da Yahya, da ma biyun na farko da aka kawo misalai da ayyukansu, wato Dunfawa da Usman.

 

2.0 Shaƙo Daga Malamai Uku

2.1 Atiku Ahmad Dunfawa

An haifi Farfesa Atiku Ahmad Dunfawa a shekarar 1953 a garin Dunfawa da ke cikin ƙaramar hukumar Zurmi ta Jihar Zamfara. Kamar yadda al’adar ƙasar Hausa ta kasance tun aƙalla zamanin Shehu ɗan Fodiyo, mahaifan Farfesa Atiku sun fara saka shi makarantar Alƙur’ani kafin ta Boko. Makarantar kuwa ita ce ta Sheikh Ibrahim Ƙaya inda ya yi shekaru goma daga 1959 zuwa 1969. Bayan ya sami shekaru biyar a cikinta sai aka saka shi ta Boko wadda ta haɗa karatun Addinin Musulunci da na Boko. Za a lura da cewa al’ummar ƙasar Hausa tun a wancan lokaci, da ma kafin sa, ba ta yarda ta yi watsi da makarantar Allo ba. Atiku ya kasance ɗan makarantu biyu a lokaci guda, wato da ta gadin-gadin, ta Allo da ta zamani, ta Boko. Har zuwa yau kuma haka tsarin yake, sai ‘yan sauye-sauye da suka zo ko ake ƙoƙarin sakawa.

Atiku ya ci gaba da karatunsa har ya yi digiri na farko da na biyu sannan a 2002 ya samu didirin digirgir, wato Ph.D. a fannin Adabin Hausa. Karatu bai bar Atiku ba shi kuma bai bar shi ba har sai da a shekara ta 2011 ya ga ya zama farfesa. Kai har yau ma ba su rabu ba! Takardar da ke bayani game da ayyukansa har zuwa shekara ta 2021 ta nuna yana da rubuce-rubuce har talatin (30) waɗanda aka buga cikin sanannun mujallu da kundaye masu daraja.

Za a iya lura da cewa tun daga lokacin da Atiku ya shiga makaranta a 1959 har zuwa 1973, kamar wada takardar bayanin ayyukan rayuwarsa ke nuni, karatunsa ya kasance tare da na ilmin Addinin Musulunci da na Larabci. (Dunfawa, 2021, Curriculum Ɓitae)

 

2.1.1 Ma’aunin Waƙa

Ma’aunin Waƙa shi ne sunan littafin da ake son a yi magana a kai a matsayin misali na shaƙon da Atiku ya yi cikin gulbin nazarin waƙoƙin Hausa. Kamar wada mai littafin ya faɗa, tushensa shi ne a 1986 lokacin da yake ɗalibin Farfesa Ɗalhatu Muhammad, da kuma cewa ya karanta wata maƙalar da malamin nasa ya rubuta. An buga wannan maƙala a 1984[2]. Ke nan Atiku a wannan fuska ya kasance wani tabi’in Ɗalhatu kamar wada Farfesa Abdulƙadir Ɗangambo da wasu da dama suke.

Wannan littafi da aka kira Ma’aunin Waƙa yana da babi har huɗu da kuma goshi da kammalawa na littafi. Muhimman ɓangarori biyu ne littafin ya yi magana a kai: da ɓangaren da ke magana a kan ma’aunin waƙoƙin Larabci wanda Hausawa suka ara suka aza rubutattun waƙoƙinsu a kai. A dalilin nazarin waƙoƙin Hausa da ake yi a makarantu tare da la’akari da wannan ilmin ma’aunin waƙoƙin Larabci, wanda ake kira arud cikin harshen Larabcin, ga dukkan alamu shi ne ya sa marubucin ya saka wannan ɓangare cikin littafin. Shi kuwa ɓangare na biyu ya shafi yadda ake iya auna waƙoƙin baka na Hausa. Wannan ɓangare shi ne maƙalar take ɗauka a matsayin shaƙon da Dunfawa marubucin Ma’aunin Waƙa ya yi.

Iƙirarin da mai Ma’aunin Waƙa ya yi biyu ne, da cewa ana yin la’akari da kiɗan da waƙa ke tafiya tare da shi a muhimman gaɓoɓin da ake auna karin waƙar; sannan da cewa a koyaushe waɗannan muhimman gaɓoɓi su ne guda huɗu na ƙarshen kowane layi/ɗangon waƙar. Wato dai karin waƙa na samuwa ta hanyar lura da daidaita kiɗanta da yake maimaita kansa tare da sautin gaɓoɓi huɗu na ƙarshen kowane layi ko ɗango. Malamin ya ƙara da cewa wannan hanya,

‘ita ya (rbc) kamata a yi amfani da ita wajen auna Bahaushen kari, ya Alla ga waƙar baka ko rubutatta. (Dunfawa, 2003, Ma’aunin Waƙa: sh.25).

 

2.1.2 Awon Kari

Ita wannan hanya Dunfawa ya yi bayanin cewa Bahaushen kari ya ƙunshi kari har guda bakwai (7). Waɗannan karuruwa masu gaɓoɓi huɗu na ƙarshen kowane layi/ɗango sune:

1.Cikakken Kari. Ana alamta shi da waɗannan gajerun layuka kamar haka - - - -. Ma’ana kowace gaɓa doguwa ce.

2.Kari Mai Dungu Ɗaya. Yana da alama haka: ɓ - - -. Wato gaɓa ta farko gajeruwa ce, sauran uku na ƙarshe kuwa dogaye ne.

3.Kari Mai Dungu Biyu. Wannan kari yana da gaɓoɓi biyu na farin gajeru, biyu kuwa na ƙarshe dogaye ne. Ana alamta shi a haka: ɓ ɓ - -.

4.Kari Mai Wushirya. Kari ne wanda tsakanin doguwar gaɓar farko da doguwa ta ƙarshe ake samun gaɓoɓi biyu gajeru. Ga yadda alamar wannan kari take: - ɓ ɓ -.

5. Kari Mai Cissawai. Wannan shi ne karin da yake da gajeruwar gaɓa a farkon gaɓoɓi huɗu na ƙarshe, sannan mai bi mata duguwa, kana ta ukun kuma gajeruwa, sannan ta ƙarshen ta kasance doguwa. Ana alamta wannan kari haka: ɓɓ -.

6. Kari Mai Giɓi Gaba. Shi wannan kari wanda yake gaɓoɓinsa huɗu na ƙarshen layi suka fara da doguwar gaɓa ɗaya sannan gajeruwa ta bi ta, sannan biyu dogaye su zo a ƙarshe. Alamar wannan kari ita ce: - ɓ - -.

7. Kari Mai Giɓi Baya. Shi kuwa wannan kari shi ne wanda gaɓoɓin huɗu suke kasancewa biyu na farko dogaye, sannan mai bi musu ta kasance gajeruwar gaɓa, ta ƙarshe kuwa ta kasance doguwar gaɓa. Alamar wannan kari na bakwai kamar haka ake yin ta: - - ɓ -.

 

Mai karatu ya lura, domin jaddadawa, da cewa dukkan gaɓoɓin da aka yi magana a kansu dangane da waɗannan karuruwa bakwai ana nufin gaɓoɓi huɗu na ƙarshen kowane layin ko ɗangon waƙa. Haka kuma marubucin ya jaddada cewa waɗannan karuruwa guda bakwai da su ne ya kamata a auna Bahashen kari, ko na waƙar baka ko kuma na rubutattar waƙa. Karuruwan bakwai dangane da rubutattun waƙoƙi, da marubucin ya kawo misali ɗaya daga cikinsu (waƙoƙin), sai ya rufe da cewa,

Wannan hanyar ita ce ake iya amfani da ita a auna sauran rubutattun waƙoƙi waɗanda aka tsara su ba a bisa karin Larabci ba.

(Dunfawa, 2003, Ma’aunin Waƙa: sh. 33).

 

A nan ne wannan maƙala take ganin za a iya cewa shi ne muhimmin lu’ulu’u wanda Dunfawa ya shaƙo a gulbin nazarin waƙoƙin Hausa dangane da yadda ake auna su. Lu’ulu’u ne na auna waƙoƙi musamman waƙoƙin baka da yake Hausawa sun riga sun aro wa nasu rubutattu ma’aunin waƙoƙin Larabci. To sai dai kamar wada muka gani, Dunfawa ya ƙara da cewa wannan ma’auni da ya shaƙo ana iya amfani da shi har ga auna rubutattun waƙoƙin Hausa waɗanda murubutansu ba su tsara su a kan ararren ma’aunin waƙoƙin Larabci ba.

A nan ne maƙalar za ta jingine bayani a kan lu’ulu’u na farko, wato Bahaushen Kari wanda Atiku Ahmad Dunfawa ya shaƙo wa manazarta waƙoƙin Hausa.

 

2.2 Bello Bala Usman

A shekarar 1962 ce ranar 8 ga watan Afrilu aka haifi Farfesa Bello Bala Usman, a unguwar Nasarawa, Shiyyar Sarakuna cikin garin Birnin Kebbi. Ya fara karatunsa, kamar sauran ‘ya’yan ƙasar Hausa, a makarantar allo da ake samu a kowane birni da ƙauye na ƙasar Hausa. Yana da shekaru uku na haihuwa aka saka shi a makarantar Malam Namadina a Shiyyar Sarakuna, Unguwar Nassarawa ta Birnin Kebbi. Ya shiga makarantar Boko ta furamare mai sunan Palace Primary School, Birnin Kebbi, ya yi ta daga 1967 zuwa 1974. Daga 1974 zuwa 1979 ya yi makarantar gaba da furamare wadda ake kira Goɓernment Secondary School, Kamba a garin Kamba. Sannan ya kammala karatunsa da ya fara cikin wannan makaranta a Kwalejin Fasaha da Kimiyya ta Sakkwato, wadda da Ingilishi aka kira State College of Arts and Science, Sokoto daga 1979 zuwa 1980. Har ila yau dai a wannan kwaleji ce daga 1980 zuwa 1982 ya yi karatunsa na gaba da Sakandare, wato IJMB, wanda da shi ne ya samu shiga Jami’ar Ahmadu Bello ta Zariya. Ya yi karatunsa na digiri a wannan jami’a daga 1982 zuwa 1985 inda ya samu digiri a fannin Hausa, wato B.A. Hons Hausa. Digirinsa na biyu, M.A. a fannin harshen Hausa a Jami’ar Bayero ta Kano daga 1987 zuwa 1990, sannan ya yi digirin digirgir, Ph.D., a fannin Adabin Hausa daga 2001 zuwa 2008 a Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo ta Sakkwato, wato Usmanu Ɗanfodiyo Uniɓersity, Sokoto. Sai dai kafin lokacin, daga 1983 zuwa 1985, ya yi wani kwas na neman takardar shaida ta Faransanci, wato Professional Certificate in French.

Likkafar Bello Bala Usman ta riƙa ci gaba tun yana mataimakin malamin jami’a (Graduate Assistant) a 1986, yana mai hawa matakan ilmi na malamin jami’a guda shidda har ya kai shi ga mataki na ƙarshe ya zama Shaihin Malami, wato Farfesa (Peofessor), na fannin Adabin Hausa a shekara ta 2021. Wannan cigaba kuwa ba kyautar ‘amshi-tashi’ ce ba, domin kuwa ƙwazonsa na karantarwa da bincike-bincikensa na ilmi da sanin makamar aiki ya kai shi ga waɗannan muƙamai. Misali, maƙalun Farfesa Usman kurum da aka buga cikin mujallu da littattafai sanannu kuma masu daraja a faɗin duniya sun kai talatin da biyar (35). (Usman 2021, Curricullum Ɓitae).

 

2.2.1 Ruwa-Biyu: Sabon Zubin Waƙoƙin Ƙarni na 21

Ruwa-Biyu maƙala ce wadda Usman ya rubuta aka kuma buga ta cikin fitowa ta 6 ta mujallar da Sashen Koyar da Harsunan Afirika da Ilmin Harshe na Jami’ar Jihar Yobe yake bugawa. Sunan Mujallar shi ne, Yobe Journal of Language, Literature and Culture, YOJOLLAC a taƙaice. Usman ya lura, kamar sauran manazartan waƙoƙin Hausa, da cewa a wannan ƙarni na ashirin da ɗaya mawaƙan Hausa sukan gwama sigogin ire-iren waƙa guda biyu da aka san Hausawa da su tun aƙalla a ƙarni na goma sha takwas (ƙ.18). A kan haka ne Usman ya fito da ra’ayin samuwar wani zubin waƙa yana mai bayyana shi da cewa waƙa ruwa-biyu,

…wata hanya ce da ake samun gaurayuwar sigogin waƙar baka da rubutacciya haɗe, a cikin waƙa guda. Irin wannan tsari ya fi fitowa fili a wasu waƙoƙin Hausa a ƙarni na ashirin da ɗaya;.. (Usman, 2018, cikin YOJOLLAC 6, sh. 219).

Usman ya yi la’akari da sigogin da manazarta waƙoƙin Hausa suka gano su ne suka keɓantu da kowace irin waƙa na ire-iren guda biyu, da kuma sigogin da suka yi tarayya kamar wada Sa’id (1981) da Yahya (1997) suka luro. Bayan haka sai ya kawo mana ainihin sigogin da ya ce su ne na waƙa ruwa-biyu da yake son a lura da su a matsayin na ita waƙar. Waɗannan sigogi na waƙa ruwa-biyu su ne wannan maƙala za ta kawo ta kuma tattauna a matsayin lu’ulu’un da Usman ya shaƙo wa manazarta.

 

2.2.2 Sigogin Waƙa Ruwa-Biyu

Akwai aƙalla sigogi guda goma sha biyu (12) waɗanda Usman ya kawo na wannan waƙa da ya kira ruwa-biyu. Waɗannan su ne:

1.                     Kiɗa. Ita wannan siga ta karaɗe wannan irin waƙa kamar yadda take a waƙoƙin baka na gargajiyar Bahaushe. Bambancin da ke akwai shi ne a waƙa ruwa-biyu kiɗan ya haɗa da kiɗe-kiɗen baƙi kamar kiɗan Turawa ko Indiyawa ko Larabawa. A kan haka ne ake amfani da kayan kiɗa kamar ‘fiyano (piano) da gita (guita) da sauransu, amma kuma hakan bai hana amfani da kayan kiɗan gargajiya ba irin su kalangu da ganga. Wannan kiɗa da shi ne ake fara waƙa ruwa-biyu kamar yadda ake fara waƙoƙin baka na Hausa da aka sani. Abin nufi shi ne kiɗan ne ke samar da irin karin da waƙa za ta hau, abin da Dunfawa (1999) ya kira ‘ƙira’, kuma tare yake tafiya da waƙar. Usman ya faɗa cewa sai an fara yin wannan kiɗa ne sannan daga bisani a ji waƙa ta fito (YOJOLLAC 6, sh. 220), kamar yadda abin yake ga sauran waƙoƙin baka na Hausa.

2.                     Amshi. Sigar amshi tana cikin sigogin da waƙa ruwa-biyu take da kamar takwararta ta gargajiya da ma rubutatta. Usman ya nuna cewa waƙa ruwa-biyu takan yi amfani da sigar amshi ko da kuwa turkenta na wa’azi ko madahu ne (YOJOLLAC 6, sh. 220).

3.                     Karɓi. Ita ma sigar karɓi da akan samu cikin waƙar baka akwai ta cikin waƙa ruwa-biyu. Siga ce wadda ‘yan amshi ke cika maganar da jagoransu ya faro cikin wani ko wasu layukan waƙar da suke rerawa.

4.                     Karɓeɓeniya. Usman ya tabbatar da wannan siga cikin waƙa ruwa-biyu tare da kawo misalai kamar yadda ya saba cikin maƙalarsa. Siga ce mai siffar amshi amma wadda ta ƙunshi hira tsakanin jagora da ‘yan amshinsa (YOJOLLAC 6, sh. 221). Wannan siga, kamar wada za mu gani a tattaunawa ta gaba, muhimmiyar siga ce a wasu wurare. Haka kuma ya ce akwai wani fitaccen salon karɓeɓeniya wanda Aminu Ala da El Mu’azu da Yahaya suka yi amfani da shi a waƙar, ‘Haka Allah Yas So’.

5.                     Amsa-amo. Rubutattun waƙoƙin Hausa su aka sani da sigar da ake kira amsa-amo. Siga ce wadda ta shafi ƙarshen ɗangogin baitocin waƙa. Usman ya ce amfani da wannan siga a ƙarshen ɗango shi ne mawaƙan ruwa-biyu suka fi amfani da shi, [3] har ma a wasu wurare sukan karya ƙa’idar amsa-amon yadda aka san ta. (YOJOLLAC 6, sh. 222).

6.                     Zubin Layukan Baiti. A ɓangaren rubutattun waƙoƙin Hausa daidaita yawan ɗangogin baitocinta tilas ne, yayin da su kuwa waƙoƙin baka ba haka ba ne, ba lalle ne yawan layukan ya daidaita ba saboda akan samu waƙa wadda wasu baitocinta (ɗiyanta) su ƙunshi layi guda-guda ko bibbiyu ko goma-goma. Usman ya tabbatar da samuwar duka sigogin biyu cikin waƙoƙi ruwa-biyu. (YOJOLLAC 6, sh. 223).

7.                     Sharar Fage. Usman ya bayyana wannan siga ta waƙa ruwa-biyu da cewa shi ne, ‘inda mai waƙa zai buɗe waƙarsa da wani abu kafin ya koma ga zubinsa na rubutacciyar waƙa mai ƙwar huɗu’. Ya kawo misali da waƙar Dauda Kahutu, ‘Ƙurunƙus’.

8.                     Mabuɗi. Ita kuwa sigar mabuɗi tana nufin, duk kuwa da Usman bai faɗi ma’anar ‘mabuɗi ba, mawaƙi ya fara waƙarsa da yabon Allah (s.w.) da Annabi (s.a.w.). Ya ce mawaƙan ƙarni na 21 masu tsara waƙa ruwa-biyu sun ari wannan fitacciyar sigar rubutattun waƙoƙin Hausa.

9.                     Amfani Da Sanƙira. Kamar yadda Usman ya faɗa sigar amfani da sanƙira a waƙoƙin baka na Hausa abu ne sananne. Sanƙira yana daga cikin ƙungiyar mawaƙi, sai dai ba aikinsa guda da sauran mutanen da ke cikin ƙungiyar ba. Shi ba rera waƙa yake yi ba, sai dai yakan furta kalamai ko dai masu ƙarin haske ga abin da jagora ke faɗa ko ya cika maganar da jagora ke yi ko kuma ya yi zuga ga mawaƙi ko ga wanda ake yi wa waƙar. Haka kuma yakan furta kalaman da suke zambo ne ga abokin hammayar wanda ake yi wa waƙar ko ma abokan hamayyar jagoran waƙar. Duk waɗannan kalamai da sanƙira kan yi yana yin su ne cikin sautin maganar yau da kullum, ba rerawa ba. Ƙololuwar maganar sanƙira ita ce amfani da karin magana. Duk wannan bayani abin da aka fahimta ne daga abin da Usman yake nufi ne da amfani da sanƙira cikin waƙoƙi ruwa-biyu. (YOJOLLAC 6, sh.226-227).

10.                 Kari. Sigar amfani da kari wurin tsara waƙa dole ne, to sai dai Usman ya ce waƙoƙi ruwa-biyu kan yi amfani da karin waƙa na Hausa (Bahaushen Kari) da kuma karin waƙoƙin Larabci da Hausawa suka ara.

11.                 Tsarmin Ɗan Waƙa. Usman ya ce a waƙa ruwa-biyu akan samu an cusa wani ɗa irin na wani nau’in waƙa da ba da shi ne ya mamaye waƙar ba. Wato idan waƙar tana cikin tsarin rubutattar waƙa sai kuma a tsinci ɗa guda ko biyu na waƙar baka. A bayanin Usman babu samuwar akasin haka, misali a ce waƙa ruwa-biyu wadda ke a kan tsarin waƙar baka sai a samu ɗa guda ko biyu na rubutattar waƙa. (YOJOLLAC 6, sh. 228-229).

12.                 Gaza. Gaza kamar yadda Usman ya yi bayani, magana ce cikin taƙaitacciyar ‘tsawa da mawaƙan baka ke yi don su mayar da hankulan ‘yan amshi da makaɗansu ga aikin da ake yi na waƙar, musamman idan suka ga wani abu na neman janye mataimakan daga waƙa’. Ya ba da misalin kalmomi kamar, ‘haba’ da ‘sama’ da ‘hayya kai’, dukansu tare da alamar motsin rai, wato ‘!’.

 

Waɗannan su ne sigogi goma sha biyu (12) waɗanda Farfeasa Bello Bala Usman ya shaƙo cikin gulbin waƙa a matsayin lu’ulu’u na biyu da wannan maƙala take ganin mai faɗaɗa nazarin waƙoƙin Hausa ne. A wata tattaunawa da shi Usman ya shaida ma mai wannan maƙala cewa yana nan yana ƙoƙarin sabunta maƙalarsa da ya saka ma suna, “Waƙa Ruwa-Biyu”.

 

2.3 Aliyah Adamu Ahmad

Majiɓinciyar Farfesa Aliyah Adamu Ahmad malama ce a Jami’ar Jihar Sakkwato wadda saura ƙiris da yardar Allah ta ɗare a kan kujerar Farfesa (wato daga Associate Professor zuwa Professor), kuma a fannin adabi da tarihinsa. An haife ta ranar 25 ga watan Yuni na shekara ta 1979, cikin birnin Sakkwato a unguwar Minanata. Kamar sauran ‘ya’yan Hausawa Aliyah ta fara karatun Addinin Musulunci tun tana da shekaru uku na haihuwa, kuma mahaifinta ne ya fara koya mata da karatun Alƙur’ani. Daga bisani kuma ya kai ta Makarantar Malam Bala Maiɗori a unguwar Minanata. Mahaifin Aliyah ya kasance mutum mai son ‘ya’yansa su samu ilmi na Addini da na Boko. A dalilin haka ne, kamar yadda Aliyah ta faɗa wa mai wannan maƙala, ko bayan da ita da ‘yan’uwanta suka girma har suka kama aiki, da yake mahaifin yana da ilmin Larabci da na Addinin Musulunci, sannan ga shi ma’aikacin gwamnati, sai ya keɓe musu lokacin da zai zaunar da su ya karantar da su daga abin da Allah ya hore masa. Lokacin da Aliyah ta kai tana da shekaru shidda a duniya sai ya shigar da ita makarantar furamare ta Boko a 1985. Wannan makarantar furamare ita ce Uniɓersity Primary School, Sokoto. Ta kammala ta a 1990, lokacin da kai tsaye ta samu shiga makarantar gaba da furamare ta haɗin kai, wato Unity Secondary School, Illela a jihar Sakkwato daga 1990 zuwa 1992. An mayar da ita zuwa makarantar Goɓernment Girls College, Sokoto a 1992 inda ta kammala a 1995. Daga shekarar 1995 zuwa ta 1997 Aliyah ta yi Kwalejin Fasaha da Kimiyya ta Haliru Binji da ke Sakkwato, wato wadda a turance ake taƙaitawa da Haliru Binji S.C.A.S.. A wannan kwaleji ta samu takardar shaidar karatun IJMB mai darajar maki 10. Wannan shi ya ba ta damar shiga kwas na yin digirinta na farko a Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo da ke Sakkwato. Ta shiga wannan Jami’a a 1997 ta kuma kammala a 2000 da samun digirin B.A. na ilmin Hausa.

Bayan da Aliyah ta karɓi takardar shaidar digirin a 2001 ta yi hidimar ƙasa (NYSC) a shekarar 2002. Wannan shi ne dalilin da ya sa ba ta ci gaba da neman ilmi ba a wannan shekara. To amma fa da kammala Hidimar Ƙasa nan take sai ta nemi ta koma jami’a don ta samo digiri na biyu, a nan dai Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo. Ta kuma yi nasara saboda ta samu gurbin neman digirin M.A. Hausa Studies daga 2002 zuwa 2004. Tana kammala wannan karatu sai Aliyah ta ƙara tsunduma cikin neman digirin digirgir, wato Ph.D.. A wannan karo sai ta tsallaka zuwa Jami’ar Bayero ta Kano a shekarar da ta kammala karatun M.A., wato a shekarar 2004. Aliyah ta kammala wannan karatu a 2009, aka kuma ba ta takardar kammala karatun a watan Fabrairu na shekarar 2010 lokacin da ta kare kundin da ta rubuta. Wannan haziƙa fa duk tsawon shekarun nan tun kammala digirinta na farko ba ta daina fafutukar ƙara neman ilmi ba, domin kuwa a ‘yan tsakankanin nan sai da ta yi wasu ƙananan kwasakwasai. Waɗannan kwasakwasai sun haɗa da na takardar shaidar samun ilmin sadarwa wadda da Ingilishi ake kira, Certificate in Mass Communication da ta samu a 2003, da ta Difloma a fagen ilmin koyarwa, wato wadda ake kira Graduate Diploma in Education, a 2004, da kuma takardar shaidar nazarin ilmin na’ura mai ƙwaƙwalwa, wato, Certificate in Computer Studies, ita kuwa a shekarar 2005.

Ta fuskar rubuce-rubuce kuwa Aliyah ba mai sanyin jiki ba ce. A halin yanzu akwai bugaggun littattafai biyar (5) nata, uku (3) daga ciki ita ce kurum ta rubuta su, biyu (2) kuwa na haɗin gwiwa ne waɗanda guda da ita da wasu a kan rubutacciyar Hausa domin makarantun gaba da furamare, guda kuwa da ita da wani. Littattafai ke nan! Amma ta ɓangaren maƙalu, a halin rubuta wannan maƙala, Aliyah tana da guda-guda har talatin (30) waɗanda aka buga cikin fitattun mujallun da suka shahara a fagen ilmi. A halin da ake ciki kuma, kamar malaman da aka ambata cikin wannan maƙala, Aliyah tana da tarin maƙalun da ko dai suke jiran a buga su ko take kan rubutawa. Haka kuma ba ta yi sanyin ƙafa ba wurin riƙa muƙamai da dama cikin jami’ar da take yi wa aiki, da kuma wasu wurare da ke biɗar ta domin ta kama musu kamar gidan rediyon BBC da ta sha yi wa alƙalancin gasar rubuce-rubucen adabi. (Aliyah 2022, Curricullum Ɓitae).

 

2.3.1 Waƙa-kwaikwaye: Daɗaɗɗen Adabin Hausawa na Auren Waƙa da Wasan kwaikwayo

 

Waƙa-kwaikwaye sakamakon binciken da Majiɓinciyar Farfesa Aliyah Adamu Ahamad ta yi ne, ta kuma gabatar a wani taron ƙara wa juna sani a Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya na Jami’ar Jihar Sakkwato da aka gudanar a farkon shekarar 2021. Daga bisani sai jami’ar ta amince da bukatar da wannan sashe ya yi na ya gudanar da gasar tsara waƙoƙi na baka da rubutattu cikin nau’in nan na waƙa-kwaikwaye. Sai kuwa Jami’ar ta aminta da wannan hangen nesa da Sashe ya yi, ta kuma naɗa Aliyah a matsayin jagorar kwamitin tsara da gudanar da wannan gasa. Aliyah ta ce ta yi murna da wannan nauyi da jami’arta ta ɗora mata saboda kamar wada ta sheda wa mai wannan maƙala, tana da yaƙinin samun damar nuna wa duniya ingancin sakamakon binciken da ta gudanar. An gudanar da gasar tun daga tarurukan gudanarwa har zuwa ga yin alƙalancin tarin waƙoƙin da mawaƙa suka aika wa kwamitin wannan gasa. Matakin ƙarshe, wato bikin rera waƙoƙin da aka samu kurum ya rage sai wasu dalilai, ciki har da yajin aikin da malaman jami’o’in Najeriya suka shiga, suka yi tarnaƙi ga gudar da shi.

Wannan maƙala ta Aliyah ita ce ta uku daga cikin lu’ulu’an da malamai uku suka shaƙo waɗanda maƙalar nan da ke a gaban mai karatu take tattaunawa a kai. Ana ganin ta dace kamar biyun ɗin da aka gabatar, ta shiga jerin lu’ulu’an da ke cikin gulbin nazarin waƙoƙin Hausa na baka da rubutattu saboda dalilin da za su bayyana cikin bayanin da ke tafe yanzu.

 

2.3.2 Sigogin Waƙa-kwaikwaye

Aliyah ta fara gabatar da asalin wannan nau’in waƙa da cewa nau’i ne daɗaɗɗe cikin waƙoƙin Hausa. Nau’i ne wanda yake da tushe daga waƙoƙin baka na Hausa, kuma da Hausawa suka sadu da adabin baƙi kamar na Larabawa sai suka ga duk da yake sun karɓi Musulunci da Larabawa suka kawo musu, addinin bai hana tsara waƙa-kwaikwaye ba. Aliyah ta kafa hujja da misalai daga waƙoƙin da ake samu cikin daɗaɗɗun wasannin kwaikwayo na Hausa, da kuma waƙoƙin Larabci. (Aliyah 2021, Waƙa-kwaikwaye: sh.5-7). Daga nan sai ta kawo sigogin waƙar kamar yadda suke a nan ƙasa.

1.                     Zubi da Tsari. Bambancin da ake iya samu ta fuskar zubi da tsari tsakanin waƙa-kwaikwaye da sauran na’o’in waƙoƙin Hausa ƙalilan ne, domin ita ma tana cikinsu, saboda ko dai ta kasance rubutatta ko ta baka ko kuma ruwa-biyu. A kan haka ne Aliyah ta fi mayar da hankali kan rerawa da aiwatarwa ko sadarwa da kuma salo. Ta ce zubi da tsarin waƙa-kwaikwaye tilas ne ya ƙunshi rerawar muryoyi fiye da ɗaya, ko dai mutum biyu ko fiye ne ke yin ta ko kuwa muryar rerawar ta yi naso ga mawaƙin da ke rera waƙar idan mawaƙi guda ne ke yin ta. Naso a nan marubuciyar tana nufin mawaƙi guda ya riƙa sassauya muryarsa daidai yadda ma’anar waƙa take ayyanawa, idan basarake ne ke magana sai mawaƙin ya rera waƙar kamar yadda Hausawa suka ɗauka basarake kan yi magana. Idan kuwa talakka ne sai mawaƙin ya rera kamar yadda talakka kan yi. A kowace rerawa an so mai saurare ya nasarta a ransa cewa ainihin wanda ake nufi ne ke magana ta fuskar furucin ko motsi da gaɓoɓin jiki. Aliyah ta ba da misali da wasu rubutattun waƙoƙin ƙarni na goma sha tara, kamar ‘Waƙar ‘Yan Jihadi/Halin Duniya Karuwa’ da ‘Jama’a Da Ku Nike’ ta Waziri Buhari. Haka kuma ta kawo misalai daga waƙoƙin Hausa na baka kamar waƙar Korona ta Maigida da Uwargida wadda AbdusSamad Babson ya yi (Aliyah da Yahya, 2020), da waƙar ‘Shayi’ wadda Kassu Zurmi ya yi. (Magaji, 2016, sh. 68-69). Waɗannan su kuma na ƙarni na 20 da na 21 ne.

Cikin duk waɗannan misalai akwai muryoyin rerawa fiye da ɗaya. Aliyah ta bukaci mai karanta maƙalarta da ya lura da cewa ba lalle ne mawaƙa biyu ko fiye su rera waƙa-kwaikwaye ba. Muhimmin abu shi ne ma’anar ɗan waƙa ko layinsa ko baitin waƙa ko ɗangonsa ta ayyana cewa maganganun da ke ciki na fiye da mutun ɗaya ne. A dalilin haka ne ta yi amfani da kalmar ‘naso’ cikin bayaninta. (Aliyah 2021, Waƙa-kwaikwaye, sh.7: 5.0.1, da sh. 12: ii).

2.                     Aiwatarwa. Aliyah (sh. 11-12) ta jaddada cewa yayin aiwatar da waƙa-kwaikwaye, wato sadar da ita ga jama’a, akwai bukatar mutune fiye da ɗaya ne za su rera ta. To amma hakan ba tilas ba ne muddin mutum ɗaya yana iya kwaikwayon wanda ma’anar layi ko ɗa/ɗango ko baiti ta ayyana. Haka za a gani cikin misalan da ta kawo na waƙar Kassu Zurmi ta ‘Shayi’ da waƙar ‘Karuwa’ wadda Mu’azu Haɗeja ya yi (Aliyah 2021, sh. 9-10 da 10-11).

3.                     Sutura. Daga cikin sigogin waƙa-kwaikwaye da Aliyah ta ambata akwai amfani da suturar mai muryar da aka ambata cikin waƙar. To sai dai hakan kan dace idan a dandali ko cikin bidiyo ne kuma mutane da yawa ne ke rera waƙar. Haka kuma mawaƙi guda ba zai iya kasancewa yana sassauya sutura wai don muryoyin waɗanda ke cikin ma’anar waƙa. Sutura a cikin waƙa-kwaikwaye ba ta da ƙa’idoji kamar yadda rerawa da sadarwa ta ƙunsa.

4.                     Salo. Idan mai karatu ya lura da ƙa’idojin da aka ambata kamin nan, ba zai rasa fahimtar cewa salo a waƙa-kwaikwaye yana cikin manyan muhimman ƙa’idojinta. A kan haka ne Aliyah ta fito da waɗannan ire-iren salon waƙa waɗanda tilas ne waƙa-kwaikwaye ta ƙunshe su. Ga su:

a.                     Hira. Marubuciyar ta ce,

salon hira kan samu a musayar magana ko dai tsakanin mutane (ko tsakanin mutum) da wani abu da ba mutum ba, kamar tsuntsu ko damisa. Kai hasili har ma da abin da yake ba na zahiri muraran ba irin duniya. (Aliyah 2021, sh.13).

Wannan ya nuna ƙarara cewa dole ne waƙa-kwaikwaye ta kasance cikin salon hira.

b.                    Zayyana. Duk da yake kamar yadda ta yi amfani da ma’anar hira da zayyana kamar yadda Yahya (2016) ya bayyana su, Aliyah ta ƙara da faɗaɗa shi salon zayyana zuwa ‘sassauƙa’ da ‘mai kwarjini’ (Aliyah, sh. 13). Sassauƙan salon zayyana shi ne inda mai sauraren waƙar ba zai samu nasartawar wani aiki a zuciyarsa ba, yayin da zayyana mai kwarjini ke ayyana ‘siffar abu ko yanayi kar tamkar ga shi a gaban mai saurare ko karatu’ (Aliyah, sh. 13).

c.                      Labari. Salon labari shi ne waƙa ta kasance mai kawo abin da ya gudana tsakanin mutane biyu ko fiye kamar yadda Yahya (2016) ya bayyana, amma ita Aliyah ta ƙara da cewa, ‘har ma da a kan shi ma kansa mawaƙin ba za a ciire ba’ (Aliyah, sh.15).

Aliyah ta kammala maƙalarta da ƙarfafa cewa waɗannan ire-iren salo ‘su ne masu tabbatar da hujjar da ta sa aka kira’ waƙa-kwaikwaye da wannan suna. Duk kuwa sai da marubuciyar ta kafa hujja cikin maƙalarta da misalai daga tarihi da kuma duka nau’o’in waƙoƙin Hausa, na baka da rubutattu da kuma ruwa-biyu. Dangane da tarihi ta kawo misalai daga waƙoƙin wasanni daɗaɗɗu da rubutattun waƙoƙin ƙarni na goma sha tara (ƙ.19), kamar waƙar Duniya Karuwa ta Audi Sha’iri Gwandu da waƙar Waziri Buhari mai suna ‘Jama’a Da Ku Nike’, sannan ta kawo misalai daga tsoffi da sabbin mawaƙa na zamanin da muke ciki, kamar waƙoƙin Kassu Zurmi da na AbdusSmad Babson cikin waƙoƙin gargajiya da na yanzu, wato ruwa-biyu, da kuma daga cikin rubutattu kamar na Mu’azu Hɗeja da na Haliru Wurno.

Wannan shi ne lu’ulu’un da Majiɓinciyar Farfesa Aliyah Adamu Ahmad ta shaƙo daga cikin gulbin nazarin waƙoƙin Hausa. Ya rage ga manazarta da su daidaita matsayin waƙa-kwaikwaye, ko dai su amince da cewa nau’in waƙoƙin Hausa ne kamar yadda Aliyah ta ɗauke ta ko kuma wani abu dabam.

A wannan ɓangare ne ake fatar mai karatu zai fahimci lu’ulu’un da kowane daga farfesoshin uku, Atiku Ahmad Dunfawa da Bello Bala Usman da kuma Aliyah Adamu Ahmad ya shaƙo.

 

3.0 Tsokaci

 Sunsunen farko da maƙalar take da shi shi ne a kan littafin Dunfawa. Sunsunen ya zo ne da kira ga manazarta waƙoƙin Hausa, kira mai halshe biyu: da halshen da ya shafi sauran rubutattun waƙoƙin Hausa; da halshen da ya shafi waƙoƙin baka da ba na Hausa ba amma suna da wata alaƙa ko dai da waƙoƙin baka na Hausa ko da kuma rubutattu na Hausa ko ma duka.

Ta fuskar sauran rubutattun waƙoƙin Hausa waɗanda aka tsara a kan ma’aunin waƙoƙin Larabci, akwai bukatar a tantance ko duka waƙoƙin ana kuma iya auna su ta amfani da Bahaushen kari guda bakwai da Dunfawa ya kawo? Dalilin yin wannan kira shi ne, duk da shike Dunfawa ya ce hanyar ita ya kamata a bi wajen auna Bahaushen kari a waƙoƙin Hausa na baka ko rubutattu, bai kawo mana sauran misalai na karin Larabci guda goma sha biyar ba bayan misalin ɗaya daga cikinsu. Kira ne sassauƙa gare shi domin watakila lokacin rubuta littafinsa ya fi mayar da hankali kan ɗalibansa, bai yi la’akari da ire-iremmu na gefen hanya ba.

Idan kuwa aka koma kan waƙoƙi na baka ko rubutattu waɗanda ba na Hausa ba, kiran yana magana ne a kan waƙoƙin al’ummomi da ke da kusanci da Hausawa musamman waɗanda suke a Yammacin Afirka ko suka samu tasirin Musulunci kamar yadda Hausawa suka samu. Gudanar da bincike don a gano shin ana iya auna waƙoƙin waɗannan al’ummomi da Bahaushen kari, abu ne wanda zai ƙayatar ainun ta fuskar ilmi da zamantakewa.Waƙoƙin Fulfulde da Zabarmanci kan iya kasancewa matakin farko ga ɗalibai, musamman da shike wasu masana, kamar Farfesa Ibrahim Ahmad Mukoshy, na ganin cewa rubutattun waƙoƙin Fulfulde su ne tushen samuwar rubutattun waƙoƙin Hausa masu kammala ga tsari da siga.[4]

Wani sunsune shi ne, anya kuwa kari bakwai ne kurum waƙoƙin Hausa suke da kamar yadda Dunfawa ya ce shi ne Bahaushen kari? Ya kamata ɗaliban nazarin waƙoƙin Hausa su yi yadda Larabawa suka yi inda suka ƙara yawan karuruwan auna waƙoƙinsu. Al-Khalil ibn Ahmad al- Farahidi ya gano karuruwa goma sha biyar (15), sannan shi kuwa Al Akhfash al- Akbar ya gano ɗaya suka zama karuruwa goma sha shidda. (https/www.fluentarabic>introd).

 

Haka nan kuma maƙalar ta ɗauki lu’ulu’un da Usman ya shaƙo ta sunsuno bukatu biyu. Bukata ta farko ita ce a taƙaita bayani kan waƙa ruwa-biyu ta ɓangaren fitattar sigarta, wato a ce waƙa ce da ta ƙunshi sigogin rubutattun waƙoƙi da na baka na Hausa. Manufa ita ce ba sai an ce tana da sauran sigogin da Usman ya kawo ba. Dalilin wannan bukata shi ne duk sauran da ya ambata akan same su, har ma da waɗanda bai ambata ba cikin nau’o’in waƙar uku, ciki kuwa har da sigogin tsarma layi ko layuka ko ɗa ko ɗiya ko ɗango ko ɗangogi ko baiti ko baitoci cikin juna. Akan samu tsarmin waƙar baka cikin rubutattar waƙa, irin misalin da shi Usman ya bayar, kamar ‘Waƙar Mata’ wadda Aliyu Maikudu Giɗaɗawa ya yi. Wannan rubutattar waƙa ce da aka yi tun kafin waƙoƙi ruwa-biyu su bayyana. Ita wannan waƙa da sigar waƙar baka ta gargajiya ta fara. Sigar kuwa ita ce zubin kirari da zuga. (Sakina 2005, sh. 67). Dubi farkonta:

 

A’uzu billahi minas sheɗanir rajim

Bismillahir Rahmanir Rahim.

Wasallallahu-Ala man la nabiyya ba’adahu amin.

Assalamu alaikum ya masoyanmu, maƙiyanmu.

Ya babbaƙun mabiyanmu mata

Masoyan dare da rana a ƙi ku

In da ku gida shi yi kyawo, in kun yi yawa gida ya ɓaci

Mai ku ba shi da kowa don baƙin ciki ka isa tai,

Ko kun yo dare kuna yin rana

Koway yabe ku sai ya ɓata, ciyon ajali komi haƙurin mutum

Shinai muku raki, mata.

Ba a yi sai da kuwa,

Ba ku da magani ga kowane mai rai.

Ɗiyan tahwasa masu daɗin kuka

Sharrinku ya hi hairinku yawa

Ƙaƙa za mu yi da ikon Allah?

Maganinku Allah shi tsare mata

(Sakina Adamu Ahmad 2005, Mata a Idon Marubuta Waƙoƙin Hausa, sh.80).

 

Wannan misali da ji da gani an san siga ce ta zubin waƙar baka. To ba nan kurum ba. Can cikin sauran baitocin waƙar akan samu wani tsarmin waƙar baka na kalma guda ko biyu tare da baitin waƙar kamar waɗannan:

 

 16. Sherinku mata na ga ba shi ƙidayuwa,

 Zambarku ni na sheda ba ta misaltuwa,

 In don jini kaɗ ɗauki babe yassuwa,

 Duw wanda yab bi macce shi taka kasuwa,

 Kuma wohoho wayyo dalilin mata.

Modde ya’e

 …

 

 21.Sha burkuta! Sha dadaƙa! Dungazumi,

Kasko!

 Mai sanya ƙato nan da nan ka ga yai gumi,

 Kowah haye maka yanzu na shi yi tagumi,

 Sa maigida kullum shi kwana da zullumi,

Makarinku sabri ja-bugayya na mata

 …

 

 30.Kayanta ta kwashe su dut ta saisuwa,

 Tasa da kwanna haka za zannan ƙawa,

 Ta kai ma bokaye tanai musu gaisuwa,

 Su ko su cinye sun iza ta ga ɗemuwa,

An ɓad da ‘yan kicihi ɓarayi mata.

 Gwai Allah!

 31.Ga son shiga yawon gidaje swahe dut,

 Ta shigam ma nema tana hwasadi swahe dut,

 Sai ga ciki ka gane ta rai ya ɓaci dut,

 Kumya ta kamma ta ga cikin a gane shi dut,

 Daɗa sai shiga gashi macuta mata.

 Kaico!!

(Sakina Adamu Ahmad 2005, sh.83, 84, 85, 86)

 

Kalmomin ‘modde ya’e’ da ‘kasko; da ‘gwai Allah’ da kuma ‘kaico’, duk an fi samun su cikin waƙoƙin baka kuma irinsu ne Usman ya faɗa muna ake kira ‘gaza’, to amma gashi an same su cikin rubutattar waƙar da aka yi tun ma ba a haifi Hausawan da suka fito da waƙoƙi ruwa-biyu ba. Mai wannan maƙala ya san wannan waƙa tun cikin gomiyar shekarun 1970 lokacin da yake makarantar sakandare.

Ta ɓangaren waƙar baka kuwa sanannen abu ne cewa akan sami wasu mawaƙan baka da kan aro wasu sigogin rubutattun waƙoƙi, kamar saka ayoyin Alƙur’ani Mai Tsarki ko fara waƙa da basmala. Sarkin Taushin Katsina misali ne cikin mawaƙan baka na Hausa na gargajiya. Haka Sani Aliyu Ɗandawo da Sani Sabulu Kanoma.

Idan haka lamarin yake to ya kamata a dubi waƙa ruwa-biyu ta fuskar kasancewarta mai haɗa waƙar baka da rubutatta, wato kai tsaye a kira ta waƙar baka ruwa-biyu saboda ba dukan sigogin abin da ake kira waƙa ne mawaƙi kan saka cikin waƙarsa ba, abin da ya sa ba za mu iya ƙididdige sigogin da waƙa ruwa-biyu kan ɗauko daga nau’o’in biyu ba.

Wani sunsune shi ne ganin yadda Usman ya ɗauka cewa kamar duk waƙar da take da zubin rubutatta amma take da kiɗa sunanta waƙa ruwa-biyu. To amma akwai wata waƙar Haliru Wurno ta madahu mai suna ‘Gulbin Yabo’. Marubucin wannan maƙala ya mallaki waƙar kuma daga hannun mawallafinta Haliru Hurno ya same ta, Tana cikin rubutun ajami na hannun shi Haliru take.[5]. Ya yi wannan waƙa cikin 1970 amma sai bayan da ya rasu cikin 2003 wani Bashiru Haliru Wurno wanda shi Halirun ya riƙa, saboda ganin yadda zamani ke tafiya a yau sai ya je sutudiyo aka saka wa waƙar kiɗa irin na zamani, shi kuma yana rera ta a kan haka. To idan aka bi bayanin Usman, tambayar da za a iya yi ita ce, ‘Shin ana iya kiran wannan waƙa da sunan ruwa-biyu a dalilin saka mata kiɗa da Bashir ya yi bayan rasuwar wanda ya yi ta da shekaru fiye da goma sha biyar (15)?’

 

Sunsunen da ya zo daga lu’ulu’un waƙa-kwaikwaye na Aliyah shi ne, tunanin cewa yana da wuya a rasa samun raha cikin waƙar da ta ƙunshi nau’in waƙa-kwaikwaye. Da yawa daga cikin misalan da ta kawo na waƙa-kwaikwaye a maƙalarta suna ƙunshe da raha a wasu wurare na baitocinsu ko ɗangoginsu. A kan haka ne ake ganin ya kamata manazarta su tantance matsayin raha cikin waƙa-kwaikwaye. Shin rahan nan da ake samu siga ce ta waƙar ko kuwa naso ne kurum na salon waƙoƙin mawaƙi? Ko kuma raha kan bayyana cikin waƙa-kwaikwaye dangane da jigon da waƙar ta ƙunsa? Misalin nan da marubuciyar ta kawo daga waƙar Wazirin Sakkwato Buhari mai suna ‘Jama’a Da Ku Nike’, bai ƙunshi raha ba. Watakila wannan ya kasance ne saboda jigon zuhudu, musamman tsoron Allah da aka gina waƙar da shi, shi ya kawo haka. To amma nauyin wannan waƙa ta fuskar Addinin Musulunci kusan ɗaya ne da waƙar ‘Gulbin Yabo’ ta Haliru Hurno. A cikin wannan waƙa Haliru ya yi amfani da sigar waƙa-kwaikwaye ya kawo abin da ya gudana lokacin da sayyidi Umar ɗan Haɗɗabi ya karɓi Musulunci. To cikin wannan waƙa-kwaikwaye Haliru ya yi amfani da kalmomin da za su iya sa mai karatu ko saurare ya yi murmushi ya kuma ji daɗi saboda da jin wannan tambaya ta Ummaru da kuma martanin da ya yi ga amsar Annabi (s.a.w), mai karatu ko saurare zai ji lalle marar tsoro ke yin maganar kuma zai yi wani abu mai faranta rai kuma mai tayar da hankalin abokan gaba. Za a nasarta cewa ga mai ƙarfi nan ya zo wanda zai cire ma jama’a jin tsoro. Kalmomin /niƙatau/ da /Sidi ɓoyo anka sa ka/ da kuma /ba a ɓoyon ibada ga ni ga ka/, da su ne mawaƙin ya cusa raha cikin zukatan masu karatu ko sauraren baitocin. Ga dai baitocin:

 

127. Rannan gaskiya ta yi kaye ga niƙatau

Ummaru Sanda ya zam Musulmi wa ka jan ka

 

128. Sai Faruku yag gai da Ahmadu sunka gaisa

Yai kalimar shahada gaba ɗai yar riƙa ka

129. …

130. Sannan lokacin Azzuhur na ga su ɓoye

Sai yat tambaya Sidi ɓoyo anka sa ka

 

131. Ahmadu yaf faɗa mai ga fili ana forai

Ka ga mu yan kaɗan Sanda mi as shawarakka

 

132. Ummaru ya yi koyon kiran salla ga Manzo

Yac ce ba a ɓoyon ibada ga ni ga ka

 

133. Yaf fita nan da nan yai kiran salla ga taro

Rannan wanda am Makka ya san ɗaukakakka

 

Cikin waɗannan baitoci yanke ana samun muhimman salailan da Aliyah ta ambata, wato da hira da zayyana da labari. Ƙari a kan salailan shi ne ana kuma samun jigon raha cikin baitocin. Idan kuwa haka abin yake a mafi yawan waƙoƙi masu nau’in waƙa-kwaikwaye, to ba laifi ba ne idan saka jigon raha cikin muhimman sigogin wannan nau’i.

Kammalawa

Haƙiƙa sakamakon nazarin da malamai uku, Dunfawa da Usman da Aliyah, suka yi, sakamako ne wanda aka tattauna cikin wannan maƙala. Sakamakon nazarinsu ne wanda ya dace a kira da sunan lu’ulu’u daga gulbin nazarin waƙoƙin Hausa. Kowane lu’ulu’u daga cikinsu mai kwarzanta da kuma faɗaɗa nazarin waƙoƙin ne, saboda kasancewar kowane daga cikinsu abu ne da za a iya ƙara duban sa har ma a zurfafa bincike domin a goge shi. Ta yin haka sai nazarin waƙoƙin Hausa ya sami ƙarin ginuwa. Ya kamata ɗalibai su ɗauki salon yin nazari don gaggano abubuwan da ba a sani ba ko ba a ida ƙalailaice su ba.

MANAZARTA

1.      Aliyah, A. A. (2017), Rupert Moultrie East 1898-1975: Tarihinsa da Sharhi a kan Gudummawarsa ga Adabin Hausa, Kaduna: Whales Adɓerts Limited.

2.      Aliyah, A. A. da Yahya, A. B. (2020), Kukan Kurciya cikin Waƙoƙin Korona Biyu, Zaria: ABUPRESS.

3.      Dunfawa, A. A., (2003), Ma’aunin Waƙa. Sokoto: Garkuwa Publshers.

4.      Ɗangambo, A. (2007), Ɗaurayar Gadon Feɗe Waƙa (sabon tsari), Zaria: amana publishers ltd.

5.      Gusau, S. M, (2003), Jagoran Nazarin Waƙar Baka, Kano: Benchmark Publishers Limited.

6.      Gusau, S. M, (2015), Waƙar Baka Bahaushiya No 14, Kano: Bayero Uniɓersity

7.      Haɗeja, M. (1980), Waƙoƙin Mu’azu Haɗeja, Zariya: Northern Nigerian Publishing Company (NNPC).

8.      Hiskett, M., (1975), A History of Hausa Islamic Ɓerse, London: School of Oriental and African Studies (SOAS).

9.      Magaji, A. (2016), Kassu Zurmi Da Waƙoƙinsa. Ibadan: Spectrum Books Limited, tare da Jersy – Channel Island, UK: Safari Books (Eɗport) Limited.

10.  Muhammad, Ɗ. (1977), ‘Indiɓidual Talent in The Hausa Poetic Tradition: A Study of Aƙilu Aliyu and His Art’, kundin Ph, D. London.

11.  Muhammad, Ɗ. (1978), Waƙa Bahaushiya”, cikin Studies in Hausa Languages, Literature And Culture I, Kano: Bayero Uniɓersity.

12.  Muhammad, Ɗ.. (1973), “A Ɓocabulary of Literary Terms In Hausa”, cikin Harsunan Nijeriya III, Kano: Bayero Uniɓersity.

13.  Muhammad, Ɗ..(1990), Hausa Metalanguage-Ƙamus Na Keɓaɓɓun Kalmomin Hausa, Ibadan: I.U. P. Limited.

14.  Sakina Adamu Ahmad 2005, ‘Mata a Idon Marubuta Waƙoƙin Hausa’. Kundin digirin farko na B.A. Sokoto: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

15.  Sokoto, I. J. (2007), Tsarabar Waziri Buhari da Waziri Junaidu ga Manazartan Waƙoƙin Hausa. Sokoto: Al-Amin Printers ltd.

16.  Usman, B. B. (2018), “Ruwa-Biyu: Sabon Zubin Waƙoƙin Ƙarni na Ashirin da Ɗaya” cikin Yobe Journal of Languages, Literature and Culture (YOJALLAC), Damaturu: Yobe State Uniɓersity.

17.  Usman, B.B. (2006), “Hikimar Magabata: Nazarin Ƙwaƙƙwafi a kan Rayuwar Malam (Dr) Umaru Nassarawa Wazirin Gwandu (1916 – 2000) da Waƙoƙinsa”, kundin digiri na uku, Sokoto: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

18.  Yahya, A. B. (2013), ‘Tsattsafi: Wani Ɗigo cikin Gulbin Nazarin Salon Waƙoƙin Hausa’ cikin ƊUNƊAYE: Journal of Hausa Studies ɓol.1: 5, Sokoto: UsmanƊanfodiyo Uniɓersity.

19.  Yahya, A. B. (2016), Salo Asirin Waƙa (sabon bugu), Sokoto: Guaranty Printers.

20.  Yahya, A.B (1997), Jigon Nazarin Waƙa, Kaduna: Fisbas Media Serɓices.

21.  Yahya, A.B (2002), ‘Siffantawa Bazar Mawaƙa: Wani Shaƙo Cikin Nazarin Waƙa’, cikin Studies in Hausa Language, Literature and Culture 5: 220-240, (ed.) Bichi A.Y., Kafin Hausa, A.U. and Yalwa, L.D., Kano: Jami’ar Bayero.

22.  Yahya, A.B, (2004), “Tsattsafin Raha Cikin Waƙoƙin Alƙali Alhaji Haliru Wurno”, maƙalar da aka gabatar a taron ƙara wa juna sani a Sashen Koyar da Harsunan Nijeriya, Sokoto: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

23.  Yahya, A.B. (1986) “Tattalin Zaɓen Rubutattun Waƙoƙin Hausa Domin Yara”, in FAIS JOURNAL Of HUMANITIES Ɓol. 3/ N0.1 (2004), Kano: Jami’ar Bayero Uniɓersity,, shafi na 217 – 232. An gabatar da wannan maƙala a 1986 a taron ƙara wa juna sani wanda Hukumar Raya Wallafar Littattafai ta Nijeriya (wato Nigerian Book Deɓelopment Council, NBDC) ta gudanar a Durbar Hotel a Kaduna daga 5 zuwa 8 ga watan Mayu, 1986.

24.  Yahya, A.B., Wasu waƙoƙin Alƙali Haliru Wurno da marubucin wannan maƙala ya mallaka waɗanda kuma ya samo daga mawallafin waƙoƙin. Mafi yawan waɗannan waƙoƙi cikin rubutun Ajami suke kuma da hannun shi Haliru Wurno.

25.  ZAUREN WAƘA: Mujallar Nazarin Waƙoƙin Hausa 1, Sashen Koyar Da Harsunan Nijeriya (2013), Sakkwato: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.



[1] Kamar yadda bincike ya nuna, Ɗalhatu Muhammad ya ƙirƙiro ko ya yi sanadin samuwar aƙalla waɗannan muhimman ayyuka biyar a nazarin waƙoƙin Hausa: taron samar da kalmomin fannu, tace kalmomin fannu da suka haifar da ƙamus na Keɓaɓɓun Kalmomi (Hausa Metalanguage), zaƙulo zumuntar waƙoƙin baka da rubutattu na Hausa da ƙarfafa samar da rumbun taskace adabi (na baka da rubutacce) da al’adun Hausa. Don ƙarin bayani duba Champion of Hausa Cikin Hausa: A Festschrift in Honour of Ɗalhatu Muhammad (2012: Ahmad Halliru Amfani da wasu biyar editoci), da Graham Furniss (1996), Poetry, Prose and Popular Culture in Hausa. sh. 314-315, da Abdullahi Bayero Yahya (2016), Salo Asirin Waƙa (sabon bugu), sh.iɓ, da kuma ayyukan da aka ambata a wannan ɗure. Haka kuma Sa’idu Muhammad Gusau a maƙalarsa ‘Yanayin Ginin Tunanin Alhaji Mamman Shata Katsina a Zubin Waƙoƙinsa na Baka’, cikin Gusau, S. M. da wasu, editoci, (2018) Studies in the Songs of Dr. Mamman Shata Katsina, sh.17, ɗure na 16.

[2] Domin karanta wannan maƙala ta Ɗalhatu Muhammad duba I.Y. Yahaya da A. Rufa’I ((editoci), Studies in Hausa Language, Literature and Culture: Proceedings of the First International Conference, July 1978, sh. 47-62. Jami’ar Bayero, Kano.

[3] Ana iya samun cikakken bayani kan amsa-amo cikin Atiku Ahmad Dunfawa, Ma’aunin Waƙa (2003), sh. 63-78.

[4] Hira da Farfesa Ibrahim Ahmad Mukoshy a gidansa cikin garin Sakkwato, ranar Alhamis, 14 ga Afrilu, 2022, lokaci: 12.50 – 1.45 na rana.

[5] Haliru kuma ya ba da ramzin waƙar na Hijira da kuma Miladiyya duk cikin waƙar: 19/Jumada Auwal/1390 wanda ya yi daidai da Attanin 12/yuli/1970. (Haliru Wurno, Gulbin Yabo, bt. 158-160). Sai dai a ganin mai wannan maƙala ‘sin’ ce Haliru ya nufi rubutawa sai ya yi mata ɗigagga uku ta zama ‘shin’. Wato a madadin ɗango na biyu ɗin baiti na 158 ya fara da /Saa tara../ sai ya koma /Sha tara…/ Idan haka abin yake to 9 ga Jumada Auwal/1390 ramzin ya kamata ya kasance.

Post a Comment

0 Comments