Tasirin Bikin Auren Hausawa A Kan Yarbawa Mazauna Gusau

    MuÆ™alar da aka gabatar a ajin ALH 400 (Seminar), a Sashen Harsuna da Al’adu, Jami’ar Tarayya, Gusau, Jahar Zamfara, Nijeriya, (Disamba 2022 - Janairu, 2023).

    Kayan Lefe

     
    Ruƙayya Yusuf S/Fada

    08034978078
    rukayyasfada@gmail.com 

    Tsakure

    Wannan muÆ™ala mai taken ‘Tasirin Auren Hausawa a kan Yarbawa mazauna Gusau’ muÆ™ala ce da ta yi duba a kan aladun Hausawa na aure waÉ—anda suka yi tasiri a kan Yarbawa mazauna Gusau. MuÆ™alar ta gano al’adun waÉ—anda su ke al-adu ne na Hausawa Yarbawa mazauna Gusau suka É—auka suka saka a cikin al’adun Auren su sanadiyyar cudanya ta tsawon lokaci. A yayin gudanar wannan bincike an yi amfani da manya-manyan hanyoyin gudanar da bincike waÉ—anda suka hada da:

    a.      Bitar ayyukan da suka gabata

    b.      Fira da wasu Al’ummar Yarbawa da ke  Gusau

    c.       Ziyarar wasu shafukan yanar gizo

    d.      Karatun bugaggun Littafai

    1.0 Gabatarwa

    Hausawa da Yarabawa al’ummu ne daban-daban, sai dai kuma sun kasance suna maÆ™wabtaka da junansu. Wannan ya sa al’ummun suke da kusanci har wasu sukan kasance a Æ™asar wasu. Maana dai Hausawa kan je Æ™asar Yarabawa su zauna su yi kasuwanci ko wata sanaa. Haka ma Yarabawa kan zo Æ™asar Hausa su zauna su yi kasuwanci ko wata sanaa. Wannan ba sabon al’amari ba ne idan aka yi la’akari da yadda kowace al’umma ta kasance a Æ™asar wata.

    Kasancewar Æ™asar da ake kira Nijeriya a yau ta haÉ—a da wani yanki na Æ™asar Hausa da kuma Æ™asar Yarabawa wannan ya taimaka wajen haÉ—uwar al’ummun biyu (Hausawa da Yarabawa). Akwai kuma sana’ar fatauci wadda tun kafin a raÉ—a wa Nijeriya suna ake yin ta wadda Hausawa kan je a wasu Æ™asashe daga ciki har da Æ™asar Yarabawa. Wannan ma ya taimaka wajen samun cuÉ—anya tsakanin Hausawan da Yarabawa. Dangane da Yarabawa da suke zaune a garin Gusau, wannan dalili yasa aka samu musayar auratayya a tsakanin al’ummun biyu sanadiyyar zama wuri  guda

    1.1 Manufar Bincike

    Babbar manufar wannan binciken ita ce, binciko irin hulÉ—a da ke tsakanin Hausawan garin Gusau da Yarabawan mazauna garin Gusau. Akwai kuma wasu manufofi da suka haÉ—a da:

    i.                    Fito da irin cuÉ—anya da ta gudana tsakanin al’ummun biyu wato Hausawa da Yarabawa.

    ii.                 Fito da al’adun Hausawa na Aure da sukayi tasiri a kan na Yarbawa mazauna Gusau.


     

    1.2 Matsalolin Bincike

                Nazarce-nazarce sun gudana a kan abin da ya shafi tasirin aure ko wata al’ada ko wani harshe a kan wani ko ma cuÉ—anya tsakanin wata al’umma da wata daban wadda ke hardasa tasirin wani abu a kan wani kamar da Burgress da Locke, (19530 da Rauf, (1977) da Funtua, (2010) da Rambo, (2013) da Auta, (2014) duk sun yi magana a kan aure. Sai dai duk binciken da aka zo da shi babu wanda ya kalli cuÉ—anyar Hausawa da Yarabawan gari Gusau. Babu shakka waÉ—annan al’ummu biyu sun yi cuÉ—anya a tsakaninsu kuma cuÉ—anyar ta haifar da wani sakamako, amma manazarta hankalinsu bai kai ga wannan cuÉ—anyar ba. Yin wannan cuÉ—anyar ya haifar da tasirin bikin Hausawa a kan na Yarabawa mazauna garin Gusau.

    1.3 Hanyoyin Gudanar da Bincike

    Wannan maÆ™alar ta kammala ne ta hanyar hira da wasu mazauna unguwannin da Yarabawa suke a garin Gusau da ma wasu Hausawa da suke zaune a garin na Gusau. An kuma tambayi wasu masu ilmi dangane da kasantuwa da cuÉ—anya tsakanin al’ummu biyu. Haka kuma an bi hanyar karance-karancen bugaggun littattafai da kundaye da muÆ™alu da masana da manazarta suka gudanar. Wannan ya ba da damar tattara dukka bayanan da aka gina wannan bincike.

    1.4.     Ra’in Bincike

    An zaÉ“i a É—ora wannan maÆ™alar a kan ra’in CuÉ—anya Bourhis (Interraction). Bourhis ya assasa wannan ra’i, kuma ya bayyana cewa, ta fuskar hulÉ—a da cuÉ—anya tsakanin wata al’umma da wata ana samun wata al’umma ta yi tasiri a kan wata. Bourhis ya Æ™ara da cewa, ana samun cuÉ—anya ta fuskar karÉ“ar horo,wato mutum ya samu horo kafin ya tsunduma cikin sha’anin rayuwar wasu[1]. Wannan maÆ™alar ta mayar da hankali ne wajen duba cuÉ—anya tsakanin Hausawan garin Gusau da Yarabawa mazauna garin Gusau tare da duba irin tasirin da harshen Hausa ko Hausawan suka yi a kan Yarabawa.

    Al’ada kalma ce da aka aro ta daga Larabci aka mayar da ita Yar Gida a Hausa ma’anar ta ita ce sabbaben abu wato abin da aka saba da shi kenan

    Dangambo (1984) cewa ya yi Al’ada it ace abin da aka saba yi yau da gobe.

    2.0 Tasiri

    Tasiri ya nufin wani abu ya yi amfani a kan wani abu na kwarai ko na banza. Kamar yadda aka sani idan Kabila biyu  wuri guda to wadda ta fi karfi a ciki zata nashe mai raunin.

    Kasancewar garin Gusau gari ne na Hausawa daga bisani Yarbawa suka shigo garin sai aka samu hulda tsakanin al’ummun biyu wanda haka ya haifar da mu’amula a tsakaninsu wadda ta hada da harda ta aurenya, wannan dalilin ne yasa aka samu sauyin al’adu ta fuskar yadda suke gudanar da bikin aurensu sakamakon auren Hausawa ko kuma bayar da aure ga Hausawa.

    2.1 Ma’anar Aure

    Aure alaÆ™a ce ta halaccin zama tsakanin miji da mata, ana yin sa ne domin shi aure sunna ce ta Annabi Muhammada Rasulullahi (S.A.W) domin tsarkaka zuri’a. Aure muhimmin abu ne ga al’umma saboda haka akwai hanyoyi da matakai na tabbatar da shi. Mataki na farko shi ne neman aure. Haka kuma akwai wasu matakai na wali, da dukiyar aure da sauransu.

    Rambo, (2013), ya ruwaito, Burgress da Locke, (1953) na cewa “Aure zamantakewa ce ta amincewar mutum É—aya ko fiye da É—aya ko mace É—aya ko fiye da É—aya mai dangantakar mata da miji”. Rauf, (1977:78) ya bayyana aure da: “Ƙulla  yarjejeniya da za ta haifar da halaccin saduwa da mace da samun zuri’a. Kuma wani É“angare ne na mu’amala da ibada”.

    Auren gargajiya na Hausawa ya danganci zaman tare a tsakanin namiji da mace a bisa yardar juna ko amincewar dangi ta hanyar wasu Æ™a’idoji na al’ada ko na addini. Ibrahim, (1985:i). Aure muhimmin al’amari ne ba kawai a wurin al’ummar Hausawa, har ga sauran al’ummomin duniya gaba É—aya.[2]

    A gudummuwa irin wannan za a iya cewa: “Aure na nufin haÉ—uwa ko ratsawar wani abu a cikin wani abu, mutum ko dabba ko tsiri da makamantansu. Domin samun albarkar da ke tattare da abubuwan da suka haÉ—u ko suka ratsa juna”.

    Idan kuma aka kalli ma’anar a addinance za a iya cewa, “Aure wata hanya ce ta baiwa namiji da macce damar zama tare da saduwa ta hanyar jin daÉ—i da mutunta junansu. Ita wannan hanya ko yarjejeniya ana gabatar da ita ne a gaban shaidu tare da yanka sadaki, kuma yadda addinin musulunci ya Æ™ayyade a kuma zartar da shi ta hanyar da sunnar Manzon Allah (SAW) ta tanada.

    Daga ma’anoni da suka gabata za’a iya cewa aure hanya ce ta hada ko kulla dangantaka tsakanin Mace da Namiji waÉ—anda za su zauna tare kuma a guri daya a matsayin mata da miji wacce kowace irin al’ada ta duniya ta amince da ita a kan dangantaka ta din-din-din domin yawaitar al’umma da kuma cigabanta.

    2.2 Hausawa

    Al’umma ce dake zaune a Arewa masu yammacin tarayyar Nijeriya. Da kudu masu yammacin jamhuriyar Nijar. Al’umma ce mai dinbin yawa, sun bazu a cikin kasashen Afirka. Da kasashen Larabawa, kuma a al’adance masu matukar hazaka ne, akalla akwai sama da miliyan hamsin waÉ—anda harshen Hausa shi ne asalin harshen su. A tarihi kabilar Hausawa na tattare a salsalar birane watau alkarya. Hausawa dai sun samu kafa daularsu ne tun daga 1300’s, sa’adda suka sami nasarori kamar su daular Mali, Songhai, Borno da kuma Fulani, a karni na 19 Hausawa suna amfani da Doki ne domin yin sifiri da balaguro. Mutane sama da miliyan hamsin ne magana da harshen Hausa a Nijeriya da Nijar da Arewacin Ghana da kuma wasu Al’umma daga yankin Kaolak a Senigal har zuwa Khartum dake kasar Sudan asalin inda zuciyar Hausawa take shine garin Kano, Katsina da Sokoto.

    2.3 Tsokaci a Kan Al’ummar Yarabawa

                Al’ummar Yarabawa kamar sauran al’ummu da suke zaune a cikin Æ™asar Afrika. Kamar yadda ya zo a Æ™arni na 19, cewa al’ummar sun samu asalin sunan na su daga Hausawa, wato ‘YARRIBA’. Wanda ya samu karÉ“uwa har bayan da Turawan Mulkin Mallaka da masu ‘yaÉ—a addinin Kirista suka sauya yadda ake furta kalmar ta koma “Yaruba” cikin sauÆ™i.Usman (2003:107-111). Manazarcin dai ya Æ™ara da cewa, wannan suna na Yoruba ya samu asali ne ga daga cibiyar Yarabawa wato Oyo. A cikin wannan Æ™arni na sha tara. Babu tantama wannan ra’ayin yana da tangarÉ—a, musamman idan muka lura da kalmar da aka ta’allaÆ™a da ita a matsayin asali. Haka kuma za a iya yarda da cewa, kalmar ta samo asali ne daga su kansu Yarabawan da suke cewa, “AWA OMO YORUBA” wato (Mu É—iyan Yoruba), wannan ya fi zama Æ™waƙƙwaran dalilin da za a iya dogaro da shi fiye da wancan.Usman (2003:107-111),

                Ban da waÉ—annan ra’ayoyi akwai ma wasu ra’ayoyi da aka samu a cikin wasu rubuce-rubucen tarihi da tarihihi. Misali mu duba wani aikin da Shaihin Malami Muhammadu B. Masani Al-katsinawi (d. 1078 A.H.-1667 A.D) ya yi da wani littafi mai taken Azharul-Ruba Fi Akhbar Bilad Yarba. Akwai wani littafi na Muhammadu Bello mai taken Infaqul Maysur. Wanda ya yi bayani a kan Yarabawa a yunÆ™urinsa na bayanin Æ™asar BaÆ™aÆ™en fata (Tukrur). Bayansa kuma akwai wani aiki da wani limamin Kirista mai suna Rev. Samuel Johnson ya rubuta a 1897 A.D. kuma ya Æ™ara tabbatar da abin da Muhammadu Bello ya faÉ—a a cikin aikinsa game da Yarabawa.

                Su dai Yarabawa sun kasance masu yin hijira daga ainihin Æ™asarsu ta haihuwa zuwa wata domin nema. Kuma sun É—auki Ile-Ife a matsayin wata cibiya ta su. duk da cewa ba a can kaÉ—ai suke ba. ko dai yaya lamarin yake tarihi ya bayyana cewa, babu wani musu, asalin Yarabawa daga zuri’ar KWA ta yankin Afrika suka fito. Kuma suna da dangantaka da harsuna kamar Igala, da Igbo, da Edo, da Idoma, da kuma Nupe da Makamantansu.Usman (2003:107-111),

                Akwai Yarabawan yankin Arewa maso Yamma, wato Yarabawan Oyo da Oshun, da Ibadan, da yankin Arewacin Egba. Akwai kuma na Kudu maso Gabas waÉ—anda suka haÉ—a da Ondo, da Owo, da Ikale, da Ijebu da kuma na yankin Ekiti. Kuma suna da bambancin karin harsuna a tsakaninsu. Yanzu haka wurin da suka zaune shi ne Kudu maso Yamma wanda ya haÉ—a da jihar Legas, da Ogun, da Ondo, da Oshun, da kuma Oyo. (Usman, 2003:107-111).

    2.4 ZuwanYarabawan Gusau

                Yarabawa sun zo Gusau rukuni-rukuni. Rukunin Yarabawan da suka zo Gusau na farko sun zo ne tun zamanin zuwan Turawan mulkin mallaka wato shekarar 1903-1960. Amma daga Æ™ididdigar Æ™idaya da aka yi a 1952 an bayyana cewa, Gusau tana da kimanin mutane 83, 884, ciki kuwa harda Hausawa da Fulani da Igbo da Yoruba da Maguzawa. Daga cikin Yarabawa sun kai kimanin 963. Sai a shekarar 1991 aka sake Æ™idaya yayin da aka samu adadin mutum 132, 390, daga ciki Yarabawa suna da 1,522.Usman, (2003:111)

                Rukunin farko na Yarabawa da suka zo a Gusau ana sa ran sun zo tun a shekarar 1910. Usman, (2003:113), ya bayyana cewa, a wata tattaunawa da ya yi da wani mai suna Mal. Raji mutumin Uyo ya bayyana masa cewa, “Yarabawan farko da suka zo sun zo ne sakamakon Turawan mulkin mallaka kuma sun zo ne domin yin aikin dafa abinci da raino da tuÆ™in mota. Kuma su Turawan suke yi wa wannan hidima.

                Rukuni na biyu da suka zo kuwa sun zo ne sakamakon gina hanyar jirgin Æ™asa a shekarar 1917, bayan gama layin dogo a shekarar 1927 aka buÉ—e shi. Haka kuma an buÉ—e Coci a shekarar 1926 domin ma’aikata da suke kula da layin dogo.

                Sai kuma rukuni na uku da suka zo a shekarar 1965 har zuwa 1970 su kuma waÉ—annan sun zo ne a sakamakon aikin kamfani na masaÆ™u da kuma na casa da mai. Ko bayan waÉ—annan Yarabawan akwai waÉ—anda suka zo sakamakon tuÆ™in mota da dafa abinci da raino da masu aikin layin dogo.Akwai kuma ‘yan kasuwa,duk sun zo sun zauna a Gusau kuma sun zama ‘yan Æ™asa. Yarabawa sun fi yawa a Unguwar Sabon-gari, kuma suna da sarki a unguwar. Duk da cewa ba unguwar Sabon-gari kaÉ—ai suke ba, misali idan aka je unguwar DamÉ“a a Gusau za a tarar akwai Yarabawa masu yawa a can kuma suna da nasu Sarki. Yarabawan da suke a unguwar Sabon-gari sun fi Hausawa yawa, kuma sun kai kimanin kashi 95% a unguwar.Usman, (2003:111)

                Mafi yawan kayan da Yarabawa suka zo da su daga Æ™asarsu ba su wuce, goro da ayaba ba. Idan suka zo nan Æ™asar Hausa kuwa sai su sayi gishiri da barkono da fatar dabbobi da gyaÉ—a da rogo da albasa da makamantansu.Usman, (2003:111)

                Akwai rukuni na huÉ—u da ake sa ran sun zo a shekarar 1969 zuwa 1970 sakamakon sana’a da neman mafaka, duk da cewa ba kowane Bayarbe ne ya zo don neman mafaka ba, (Usman, 2003: 111-120).

    2.5 Taƙaitaccen Tarihin Garin Gusau

                Garin Gusau, gari ne da a can baya yake a cikin tsohuwar daular Katsina, yanzu kuma ita ce babban birnin jihar Zamfara. Mafi yawan mutanen da ke zaune a wannan gari Katsinawa da Zamfarawa ne, su kuma waÉ—annan Æ™abilu dukkansu Hausawa ne. Gusau, (2014:18) Kasancewar wannan gari (Gusau) yana a Æ™asar Hausa kuma akwai albarkatun noma, ya sa ya albarkatu da yawan baÆ™i kamar Yarabawa da Inyamurai (Igbo) da wasu Æ™abilu masu saye da sayarwa na daga kayan da ake nomawa a wannan gari da ma jihar baki É—aya.          

                Kamar yadda tarihi ya gabata an kafa garin ne a shekarar 1811, bayan tasowa daga ‘yandoto a shekarar 1806. Gusau na daga cikin manyan garuruwan tsohuwar jihar Sakkwato kafin daga bisani ya zama babban birnin jihar Zamfara a shekarar 1996. Kundin bayanin tarihi na Æ™asa na 1920 ya nuna, garin yana kan titin Sakkwato zuwa Zariya ne, kilomita 179 tsakaninsa da Zariya, kolimita 210 tsakaninsa da Sakkwato. Daga gabas ya yi iyaka da Æ™asar Katsina da ta Kwatarkwashi daga Arewa kuma ya yi iyaka da Æ™asar Ƙaura, daga Yamma kuwa ya yi iyaka da Æ™asar BunguÉ—u. Ta É“angaren Kudu kuma ya yi iyaka da Æ™asar ÆŠansadau da Tsafe, (Gusau, 2012:7)

                Kasancewar almajirin Shehu Usmanu ÆŠanfodiyo wato malam Sambo ÆŠan Ashafa ya kafa Gusau, wanda yake da shi da jama’arsa ba ruwansu da bautar iskoki, ko tsafi irin wanda Hausawa ke yi kafin zuwan addinin Musulunci, wato garin Gusau ba ya da tarihin jahiliyya, haka ta sa duk al’adun Gusawa, al’adu ne irin na Musulunci, kuma shigowar wasu mutane wato baÆ™i a Gusau, ba ta gurÉ“ata waÉ—annan kyawawan al’adu ba, domin kuwa mafi yawan baÆ™in da suka tahowa malamai ne na Musulunci da almajirai, Fulani da wasunsu kan taho garin don tsira da addininsu da mutuncinsu da kuma dukiyarsu.

    3.0 Tasirin Auren Hausawa A kan na Yarbawa

    Kasancewar kowace al’umma tana da nata tsarin yadda take gudanar da bukukuwanta amma sakamakon cudanya a kan samu nason al’adu ta sanadiyyar cudanya a tsaninsu.

    Al’adun auren Hausawa sun sha bam-bam dana Yarbawa amma a sanadiyyar zamantakewarsu wuri daya yasa al’adun Hausawa sukayi tasiri akan na Yarbawan mazauna Gusau, gasu kamar haka:

            i.            Nagani Ina so: Wannan wata al’ada ce da Hausawa sukeyi wadda idan Namiji ya ga Macce yana so zai saye kayyaki kamar: Cingam, Biskit, Lemu, Goro da Ruwa ya tura akai gidansu domin neman aurenta. A da Yarbawa ba su yin wannan al’adar amma a yanzu suna yi kuma suna kiran nagani ina so da “IYOJU” a harshen yarbanci.

         ii.            Lefe: kalmar ta samo asali ne daga wani akwati na kaba da Hausawa ke sakawa wanda a da shi ne ake kai kayan aure. Lefe na nufin kayan da Ango ke kaiwa Amarya a lokacin neman aure waÉ—anda suka hada da: Atamfofi, Leshi, Takalmi, Jikka, kayan kwalliya akwati da sauransu. A al’adar Yarbawa namiji baya yiwa Mace Lefe Idan zai aure ta sai da akwai wata al’ada ta su wadda ta yi kama da wannan, al’adar itace Ango zai yi wa Amaryar kayan cin biki, galibi wadannan kayan basu wuce kala Ukku kuma yana yin wadannan kayan ne ta hanyar yin anko tsakanin shi da Amaryar, Idan Leshi zai dunka mata ya kan saye yadi goma sha biyar ya dauki yadi goma ya bata yadi biyar. A harshen Yarbawa suna kiran wadannan kayan da “IGBA IYAWO”. To amma a sakamakon auratayya tsakanin Yarbawa da Hausawa yasa yanzu suna yin Lefe

       iii.            Kayan ÆŠaki: Komattsai ne da iyayen Amarya tare da taimakon dangi suke haÉ—uwa a kaiwa amarya waÉ—anda suka hada da: Manyan Kujeru, Gado, Katifa, Durowa da makamantansu. Al’ada ce wadda Hausawa suke yi amma a sakamokon cuÉ—anyar Yarbawa suna yin wannan al’ada, wanda a da can hakkin waÉ—annan kaya sun rataya a kan Miji ne a tasu al’adar.

       iv.            Gara: Al’adar Bahaushe idan zai aurar da ‘Yarshi yana yi mata Gara (Kayan Abinci) waÉ—anda suka hada da Shinkafa, Taliya, Makaroni, Manja, Mangida, Manshanu da makamantansu a kai ta da su, wadda Yarbawa ba su da wannan al’ada sai dai suna da makamanciyarta, sai dai kuma akwai saÉ“ani a tsakaninsu. A Bahaushiyar al’ada iyayen Mace su ke kai gara amma a al’adar Yarbawa Namiji ne yake sayen kayan abinci ya kai gidan iyayen yarinya tare da kuÉ—i da za’a rabawa danginta, wannan al’ada suna kiranta da “ERU IDANA” amma a yanzu sakamakon auratayya tsakanin al’ummun biyu suna yin Gara.

     4.0 Sakamakon Bincike

    Wannan muÆ™ala ta kawo yadda al’adun Hausawa na Aure suka yi tasiri akan na Yarbawa mazauna Gusau. Sauye-sauyen al’adun waÉ—anda suka haÉ—a da:

    a.      Nagani Ina so: Wannan al’ada ce da Hausawa su ke yi wadda a yanzu haka Yarbawa suna yin ta waÉ—anda suke zaune a garin na Gusau

    b.     Lefe: Wanda a al’adar Yarbawa basu yin shi sai sanadiyyar cudanya da Hausawa

    c.      Kayan ÆŠaki: Wannan wata al’adar Bahaushe ce wadda ita ma a yanzu Yarbawa mazauna Gusau suna yin ta.

    d.     Gara: Wannan al’ada ce ta Bahaushe wadda ake yi lokacin aure wadda a yanzu haka Yarbawa mazauna Gusau suna yin ta.

    5.0 Kammalawa

    Wannan maÆ™ala ta duba lamarin cuÉ—anya tsakanin Hausawa da Yarabawa. Sakamakon wannan cuÉ—anya ya haddasa tasirin wasu al’adu da kuma harshen Hausa a kan na Yarabawa. MaÆ™alar ta gano cewa har alaÆ™a ta auratayya ta shiga tsakanin al’ummun biyu. An yi bayanin al’ada da abunda ake nufi da tasiri tare da kawo ma’anar aure. An yi tsokaci akan al’ummar Yarbawa tare da kawo takaitaccen tarihin Gusau. An kawo yadda Yarbawa suka samu kansu a garin Gusau da mu’amular da ta shiga tsakaninsu kamar ta fannin bukukuwansu waÉ—anda suka hada da Bikin aure, Haihuwa da sauransu. MuÆ™alar ta bayyana al’adun da suka yi tasiri na bikin auren Hausawa akan na Yarbawa mazauna Gusau.

    Manazarta

    Abraham, R. C. (1962). Dictionary of the Hausa Language. London: Hodder Sydney.

    Adamu, (2010) “The Major Landmarks in the History of Hausaland”. The Eleventh       Inaugural Lecture. Sokoto: Usmanu ÆŠanfodiyo University.

    Adamu, M. (1991) Hausa Factor In West African History, (Tasirin Hausawa a     Afrika ta Yamma. Zariya: Ahmadu Bello University Press.

    Bargery, G. P. (1934). A Hausa-English Dictionary. London: OÉ—ford University Press.

    Burgress, and Locke, (1953). The Family, 2nd (ed): New York. American Book. Co.

    Bourhis, R. Y. (1997) Language in EthicInteraction: A Social Psychological Approach. England: Pergamon.

    Bunza, A.M. (1991), “Ba BaÆ™o Ruwa ka sha Labari; (Ƙimar BaÆ™o da BaÆ™unci a Al’adar Bahaushe)”

    CNHN (2006), Cibiyar Nazarin Al’adun Nijeriya Jami’ar Bayero Kano.

    Funtua, da Gusau, (2010), Al’adu da ÆŠabi’un Hausawa da Fulani El-Abbas Printers and Concepts Kaduna

    Gusau, R. A. (2014) Garin Gusau a Taƙaice Gusau: Al-Huda Ventures.

    Gusau, S. M da Gusau B. M. (2012) Gusau Ta Malam Sambo. Kano: Benchmark Publishers Limited.

    Ibrahim, M. S. (1982) “Dangantakar Al’ada da Addini: Tasirin Musulunci a Kan             Rayuwar             Hausawa ta Gargajiya”. Kundin Digiri na Biyu. Kano: Jam’iar          Bayero.

    Madabo, M.H (1979) Ciniki da Sana’o’i a Ƙasar Hausa Annuri Printers and Publication D/Rimi.

    Mu’azu, A. (2013) BaÆ™in Al’adu a Ƙagaggun Littattafan Soyayya na Hausa.          Zariya: Ahmadu Bello University Press

    Rambo, R. A. (2013), “Gwagwarmayar Kamancen Neman auren Hausawa Da Na Dakarkari”. Takardar da aka gabatar a taron Æ™arawa juna Sani a Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya. Jami’ar Usmanu ÆŠanfodiyo, Sakkwato.

    Rauf, M. A. (1977). Islamic View On Women and Family: New York: Cambrige Press.

    Sallau, B.A. (2010) Wanzanci da Muhimmancinsa ga Rayuwar Hausawa. Kaduna:         Najiu             Professional Printers.

    Smith, M.G. (1959) “The Hausa System of Social Status” in Africa Vol. XXVII. No. 1.

    Usman A. F. (2003) “Inter-Group Relations in Gusau: A Case Study of Yoruba and Hausa C. 1920-1996. PhD Theses, Department of History Usmanu ÆŠanfodiyo University Sokoto.

    RATAYEN HIRARRAKI

    S/No

    Suna

    Shekaru

    Adireshi

    Matsayi

    Rana

    1

    Mal. Raji

    57

    Sabon-gari Gusau

    Mamba a ƙungiyar Yarabawan Gusau

    Alhamis 10/11/2022

    Da 10:00ns

    2

    Haruna Umar Gusau

    40

    Sabon-gari Gusau

    Ma’aikacin Gwamnati sashen lafiya a Gusau

    Alhamis

    8/12/2022

    Da 5:31ny

    3

    Boda Radiyo

    55

    Sabon-gari Gusau

    Mai Gyaran Radiyo

    Alhamis 15/12/2022

    Da 5:00ny

    4

    Mujiddat Abdulrauf

    46

    Sabon-gari Gusau

    Malama

    Lahadi

    15/01/2023

    Da 7:00nd

     

     

     



    [1]A duba Bourhis, (1997) The Interactive Acculturation Model.

     

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.