Ticker

6/recent/ticker-posts

Tasirin Bikin Auren Hausawa A Kan Yarbawa Mazauna Gusau

Muƙalar da aka gabatar a ajin ALH 400 (Seminar), a Sashen Harsuna da Al’adu, Jami’ar Tarayya, Gusau, Jahar Zamfara, Nijeriya, (Disamba 2022 - Janairu, 2023).

Kayan Lefe

 
Ruƙayya Yusuf S/Fada

08034978078
rukayyasfada@gmail.com 

Tsakure

Wannan muƙala mai taken ‘Tasirin Auren Hausawa a kan Yarbawa mazauna Gusau’ muƙala ce da ta yi duba a kan aladun Hausawa na aure waɗanda suka yi tasiri a kan Yarbawa mazauna Gusau. Muƙalar ta gano al’adun waɗanda su ke al-adu ne na Hausawa Yarbawa mazauna Gusau suka ɗauka suka saka a cikin al’adun Auren su sanadiyyar cudanya ta tsawon lokaci. A yayin gudanar wannan bincike an yi amfani da manya-manyan hanyoyin gudanar da bincike waɗanda suka hada da:

a.      Bitar ayyukan da suka gabata

b.      Fira da wasu Al’ummar Yarbawa da ke  Gusau

c.       Ziyarar wasu shafukan yanar gizo

d.      Karatun bugaggun Littafai

1.0 Gabatarwa

Hausawa da Yarabawa al’ummu ne daban-daban, sai dai kuma sun kasance suna maƙwabtaka da junansu. Wannan ya sa al’ummun suke da kusanci har wasu sukan kasance a ƙasar wasu. Maana dai Hausawa kan je ƙasar Yarabawa su zauna su yi kasuwanci ko wata sanaa. Haka ma Yarabawa kan zo ƙasar Hausa su zauna su yi kasuwanci ko wata sanaa. Wannan ba sabon al’amari ba ne idan aka yi la’akari da yadda kowace al’umma ta kasance a ƙasar wata.

Kasancewar ƙasar da ake kira Nijeriya a yau ta haɗa da wani yanki na ƙasar Hausa da kuma ƙasar Yarabawa wannan ya taimaka wajen haɗuwar al’ummun biyu (Hausawa da Yarabawa). Akwai kuma sana’ar fatauci wadda tun kafin a raɗa wa Nijeriya suna ake yin ta wadda Hausawa kan je a wasu ƙasashe daga ciki har da ƙasar Yarabawa. Wannan ma ya taimaka wajen samun cuɗanya tsakanin Hausawan da Yarabawa. Dangane da Yarabawa da suke zaune a garin Gusau, wannan dalili yasa aka samu musayar auratayya a tsakanin al’ummun biyu sanadiyyar zama wuri  guda

1.1 Manufar Bincike

Babbar manufar wannan binciken ita ce, binciko irin hulɗa da ke tsakanin Hausawan garin Gusau da Yarabawan mazauna garin Gusau. Akwai kuma wasu manufofi da suka haɗa da:

i.                    Fito da irin cuɗanya da ta gudana tsakanin al’ummun biyu wato Hausawa da Yarabawa.

ii.                 Fito da al’adun Hausawa na Aure da sukayi tasiri a kan na Yarbawa mazauna Gusau.


 

1.2 Matsalolin Bincike

            Nazarce-nazarce sun gudana a kan abin da ya shafi tasirin aure ko wata al’ada ko wani harshe a kan wani ko ma cuɗanya tsakanin wata al’umma da wata daban wadda ke hardasa tasirin wani abu a kan wani kamar da Burgress da Locke, (19530 da Rauf, (1977) da Funtua, (2010) da Rambo, (2013) da Auta, (2014) duk sun yi magana a kan aure. Sai dai duk binciken da aka zo da shi babu wanda ya kalli cuɗanyar Hausawa da Yarabawan gari Gusau. Babu shakka waɗannan al’ummu biyu sun yi cuɗanya a tsakaninsu kuma cuɗanyar ta haifar da wani sakamako, amma manazarta hankalinsu bai kai ga wannan cuɗanyar ba. Yin wannan cuɗanyar ya haifar da tasirin bikin Hausawa a kan na Yarabawa mazauna garin Gusau.

1.3 Hanyoyin Gudanar da Bincike

Wannan maƙalar ta kammala ne ta hanyar hira da wasu mazauna unguwannin da Yarabawa suke a garin Gusau da ma wasu Hausawa da suke zaune a garin na Gusau. An kuma tambayi wasu masu ilmi dangane da kasantuwa da cuɗanya tsakanin al’ummu biyu. Haka kuma an bi hanyar karance-karancen bugaggun littattafai da kundaye da muƙalu da masana da manazarta suka gudanar. Wannan ya ba da damar tattara dukka bayanan da aka gina wannan bincike.

1.4.     Ra’in Bincike

An zaɓi a ɗora wannan maƙalar a kan ra’in Cuɗanya Bourhis (Interraction). Bourhis ya assasa wannan ra’i, kuma ya bayyana cewa, ta fuskar hulɗa da cuɗanya tsakanin wata al’umma da wata ana samun wata al’umma ta yi tasiri a kan wata. Bourhis ya ƙara da cewa, ana samun cuɗanya ta fuskar karɓar horo,wato mutum ya samu horo kafin ya tsunduma cikin sha’anin rayuwar wasu[1]. Wannan maƙalar ta mayar da hankali ne wajen duba cuɗanya tsakanin Hausawan garin Gusau da Yarabawa mazauna garin Gusau tare da duba irin tasirin da harshen Hausa ko Hausawan suka yi a kan Yarabawa.

Al’ada kalma ce da aka aro ta daga Larabci aka mayar da ita Yar Gida a Hausa ma’anar ta ita ce sabbaben abu wato abin da aka saba da shi kenan

Dangambo (1984) cewa ya yi Al’ada it ace abin da aka saba yi yau da gobe.

2.0 Tasiri

Tasiri ya nufin wani abu ya yi amfani a kan wani abu na kwarai ko na banza. Kamar yadda aka sani idan Kabila biyu  wuri guda to wadda ta fi karfi a ciki zata nashe mai raunin.

Kasancewar garin Gusau gari ne na Hausawa daga bisani Yarbawa suka shigo garin sai aka samu hulda tsakanin al’ummun biyu wanda haka ya haifar da mu’amula a tsakaninsu wadda ta hada da harda ta aurenya, wannan dalilin ne yasa aka samu sauyin al’adu ta fuskar yadda suke gudanar da bikin aurensu sakamakon auren Hausawa ko kuma bayar da aure ga Hausawa.

2.1 Ma’anar Aure

Aure alaƙa ce ta halaccin zama tsakanin miji da mata, ana yin sa ne domin shi aure sunna ce ta Annabi Muhammada Rasulullahi (S.A.W) domin tsarkaka zuri’a. Aure muhimmin abu ne ga al’umma saboda haka akwai hanyoyi da matakai na tabbatar da shi. Mataki na farko shi ne neman aure. Haka kuma akwai wasu matakai na wali, da dukiyar aure da sauransu.

Rambo, (2013), ya ruwaito, Burgress da Locke, (1953) na cewa “Aure zamantakewa ce ta amincewar mutum ɗaya ko fiye da ɗaya ko mace ɗaya ko fiye da ɗaya mai dangantakar mata da miji”. Rauf, (1977:78) ya bayyana aure da: “Ƙulla  yarjejeniya da za ta haifar da halaccin saduwa da mace da samun zuri’a. Kuma wani ɓangare ne na mu’amala da ibada”.

Auren gargajiya na Hausawa ya danganci zaman tare a tsakanin namiji da mace a bisa yardar juna ko amincewar dangi ta hanyar wasu ƙa’idoji na al’ada ko na addini. Ibrahim, (1985:i). Aure muhimmin al’amari ne ba kawai a wurin al’ummar Hausawa, har ga sauran al’ummomin duniya gaba ɗaya.[2]

A gudummuwa irin wannan za a iya cewa: “Aure na nufin haɗuwa ko ratsawar wani abu a cikin wani abu, mutum ko dabba ko tsiri da makamantansu. Domin samun albarkar da ke tattare da abubuwan da suka haɗu ko suka ratsa juna”.

Idan kuma aka kalli ma’anar a addinance za a iya cewa, “Aure wata hanya ce ta baiwa namiji da macce damar zama tare da saduwa ta hanyar jin daɗi da mutunta junansu. Ita wannan hanya ko yarjejeniya ana gabatar da ita ne a gaban shaidu tare da yanka sadaki, kuma yadda addinin musulunci ya ƙayyade a kuma zartar da shi ta hanyar da sunnar Manzon Allah (SAW) ta tanada.

Daga ma’anoni da suka gabata za’a iya cewa aure hanya ce ta hada ko kulla dangantaka tsakanin Mace da Namiji waɗanda za su zauna tare kuma a guri daya a matsayin mata da miji wacce kowace irin al’ada ta duniya ta amince da ita a kan dangantaka ta din-din-din domin yawaitar al’umma da kuma cigabanta.

2.2 Hausawa

Al’umma ce dake zaune a Arewa masu yammacin tarayyar Nijeriya. Da kudu masu yammacin jamhuriyar Nijar. Al’umma ce mai dinbin yawa, sun bazu a cikin kasashen Afirka. Da kasashen Larabawa, kuma a al’adance masu matukar hazaka ne, akalla akwai sama da miliyan hamsin waɗanda harshen Hausa shi ne asalin harshen su. A tarihi kabilar Hausawa na tattare a salsalar birane watau alkarya. Hausawa dai sun samu kafa daularsu ne tun daga 1300’s, sa’adda suka sami nasarori kamar su daular Mali, Songhai, Borno da kuma Fulani, a karni na 19 Hausawa suna amfani da Doki ne domin yin sifiri da balaguro. Mutane sama da miliyan hamsin ne magana da harshen Hausa a Nijeriya da Nijar da Arewacin Ghana da kuma wasu Al’umma daga yankin Kaolak a Senigal har zuwa Khartum dake kasar Sudan asalin inda zuciyar Hausawa take shine garin Kano, Katsina da Sokoto.

2.3 Tsokaci a Kan Al’ummar Yarabawa

            Al’ummar Yarabawa kamar sauran al’ummu da suke zaune a cikin ƙasar Afrika. Kamar yadda ya zo a ƙarni na 19, cewa al’ummar sun samu asalin sunan na su daga Hausawa, wato ‘YARRIBA’. Wanda ya samu karɓuwa har bayan da Turawan Mulkin Mallaka da masu ‘yaɗa addinin Kirista suka sauya yadda ake furta kalmar ta koma “Yaruba” cikin sauƙi.Usman (2003:107-111). Manazarcin dai ya ƙara da cewa, wannan suna na Yoruba ya samu asali ne ga daga cibiyar Yarabawa wato Oyo. A cikin wannan ƙarni na sha tara. Babu tantama wannan ra’ayin yana da tangarɗa, musamman idan muka lura da kalmar da aka ta’allaƙa da ita a matsayin asali. Haka kuma za a iya yarda da cewa, kalmar ta samo asali ne daga su kansu Yarabawan da suke cewa, “AWA OMO YORUBA” wato (Mu ɗiyan Yoruba), wannan ya fi zama ƙwaƙƙwaran dalilin da za a iya dogaro da shi fiye da wancan.Usman (2003:107-111),

            Ban da waɗannan ra’ayoyi akwai ma wasu ra’ayoyi da aka samu a cikin wasu rubuce-rubucen tarihi da tarihihi. Misali mu duba wani aikin da Shaihin Malami Muhammadu B. Masani Al-katsinawi (d. 1078 A.H.-1667 A.D) ya yi da wani littafi mai taken Azharul-Ruba Fi Akhbar Bilad Yarba. Akwai wani littafi na Muhammadu Bello mai taken Infaqul Maysur. Wanda ya yi bayani a kan Yarabawa a yunƙurinsa na bayanin ƙasar Baƙaƙen fata (Tukrur). Bayansa kuma akwai wani aiki da wani limamin Kirista mai suna Rev. Samuel Johnson ya rubuta a 1897 A.D. kuma ya ƙara tabbatar da abin da Muhammadu Bello ya faɗa a cikin aikinsa game da Yarabawa.

            Su dai Yarabawa sun kasance masu yin hijira daga ainihin ƙasarsu ta haihuwa zuwa wata domin nema. Kuma sun ɗauki Ile-Ife a matsayin wata cibiya ta su. duk da cewa ba a can kaɗai suke ba. ko dai yaya lamarin yake tarihi ya bayyana cewa, babu wani musu, asalin Yarabawa daga zuri’ar KWA ta yankin Afrika suka fito. Kuma suna da dangantaka da harsuna kamar Igala, da Igbo, da Edo, da Idoma, da kuma Nupe da Makamantansu.Usman (2003:107-111),

            Akwai Yarabawan yankin Arewa maso Yamma, wato Yarabawan Oyo da Oshun, da Ibadan, da yankin Arewacin Egba. Akwai kuma na Kudu maso Gabas waɗanda suka haɗa da Ondo, da Owo, da Ikale, da Ijebu da kuma na yankin Ekiti. Kuma suna da bambancin karin harsuna a tsakaninsu. Yanzu haka wurin da suka zaune shi ne Kudu maso Yamma wanda ya haɗa da jihar Legas, da Ogun, da Ondo, da Oshun, da kuma Oyo. (Usman, 2003:107-111).

2.4 ZuwanYarabawan Gusau

            Yarabawa sun zo Gusau rukuni-rukuni. Rukunin Yarabawan da suka zo Gusau na farko sun zo ne tun zamanin zuwan Turawan mulkin mallaka wato shekarar 1903-1960. Amma daga ƙididdigar ƙidaya da aka yi a 1952 an bayyana cewa, Gusau tana da kimanin mutane 83, 884, ciki kuwa harda Hausawa da Fulani da Igbo da Yoruba da Maguzawa. Daga cikin Yarabawa sun kai kimanin 963. Sai a shekarar 1991 aka sake ƙidaya yayin da aka samu adadin mutum 132, 390, daga ciki Yarabawa suna da 1,522.Usman, (2003:111)

            Rukunin farko na Yarabawa da suka zo a Gusau ana sa ran sun zo tun a shekarar 1910. Usman, (2003:113), ya bayyana cewa, a wata tattaunawa da ya yi da wani mai suna Mal. Raji mutumin Uyo ya bayyana masa cewa, “Yarabawan farko da suka zo sun zo ne sakamakon Turawan mulkin mallaka kuma sun zo ne domin yin aikin dafa abinci da raino da tuƙin mota. Kuma su Turawan suke yi wa wannan hidima.

            Rukuni na biyu da suka zo kuwa sun zo ne sakamakon gina hanyar jirgin ƙasa a shekarar 1917, bayan gama layin dogo a shekarar 1927 aka buɗe shi. Haka kuma an buɗe Coci a shekarar 1926 domin ma’aikata da suke kula da layin dogo.

            Sai kuma rukuni na uku da suka zo a shekarar 1965 har zuwa 1970 su kuma waɗannan sun zo ne a sakamakon aikin kamfani na masaƙu da kuma na casa da mai. Ko bayan waɗannan Yarabawan akwai waɗanda suka zo sakamakon tuƙin mota da dafa abinci da raino da masu aikin layin dogo.Akwai kuma ‘yan kasuwa,duk sun zo sun zauna a Gusau kuma sun zama ‘yan ƙasa. Yarabawa sun fi yawa a Unguwar Sabon-gari, kuma suna da sarki a unguwar. Duk da cewa ba unguwar Sabon-gari kaɗai suke ba, misali idan aka je unguwar Damɓa a Gusau za a tarar akwai Yarabawa masu yawa a can kuma suna da nasu Sarki. Yarabawan da suke a unguwar Sabon-gari sun fi Hausawa yawa, kuma sun kai kimanin kashi 95% a unguwar.Usman, (2003:111)

            Mafi yawan kayan da Yarabawa suka zo da su daga ƙasarsu ba su wuce, goro da ayaba ba. Idan suka zo nan ƙasar Hausa kuwa sai su sayi gishiri da barkono da fatar dabbobi da gyaɗa da rogo da albasa da makamantansu.Usman, (2003:111)

            Akwai rukuni na huɗu da ake sa ran sun zo a shekarar 1969 zuwa 1970 sakamakon sana’a da neman mafaka, duk da cewa ba kowane Bayarbe ne ya zo don neman mafaka ba, (Usman, 2003: 111-120).

2.5 Taƙaitaccen Tarihin Garin Gusau

            Garin Gusau, gari ne da a can baya yake a cikin tsohuwar daular Katsina, yanzu kuma ita ce babban birnin jihar Zamfara. Mafi yawan mutanen da ke zaune a wannan gari Katsinawa da Zamfarawa ne, su kuma waɗannan ƙabilu dukkansu Hausawa ne. Gusau, (2014:18) Kasancewar wannan gari (Gusau) yana a ƙasar Hausa kuma akwai albarkatun noma, ya sa ya albarkatu da yawan baƙi kamar Yarabawa da Inyamurai (Igbo) da wasu ƙabilu masu saye da sayarwa na daga kayan da ake nomawa a wannan gari da ma jihar baki ɗaya.          

            Kamar yadda tarihi ya gabata an kafa garin ne a shekarar 1811, bayan tasowa daga ‘yandoto a shekarar 1806. Gusau na daga cikin manyan garuruwan tsohuwar jihar Sakkwato kafin daga bisani ya zama babban birnin jihar Zamfara a shekarar 1996. Kundin bayanin tarihi na ƙasa na 1920 ya nuna, garin yana kan titin Sakkwato zuwa Zariya ne, kilomita 179 tsakaninsa da Zariya, kolimita 210 tsakaninsa da Sakkwato. Daga gabas ya yi iyaka da ƙasar Katsina da ta Kwatarkwashi daga Arewa kuma ya yi iyaka da ƙasar Ƙaura, daga Yamma kuwa ya yi iyaka da ƙasar Bunguɗu. Ta ɓangaren Kudu kuma ya yi iyaka da ƙasar Ɗansadau da Tsafe, (Gusau, 2012:7)

            Kasancewar almajirin Shehu Usmanu Ɗanfodiyo wato malam Sambo Ɗan Ashafa ya kafa Gusau, wanda yake da shi da jama’arsa ba ruwansu da bautar iskoki, ko tsafi irin wanda Hausawa ke yi kafin zuwan addinin Musulunci, wato garin Gusau ba ya da tarihin jahiliyya, haka ta sa duk al’adun Gusawa, al’adu ne irin na Musulunci, kuma shigowar wasu mutane wato baƙi a Gusau, ba ta gurɓata waɗannan kyawawan al’adu ba, domin kuwa mafi yawan baƙin da suka tahowa malamai ne na Musulunci da almajirai, Fulani da wasunsu kan taho garin don tsira da addininsu da mutuncinsu da kuma dukiyarsu.

3.0 Tasirin Auren Hausawa A kan na Yarbawa

Kasancewar kowace al’umma tana da nata tsarin yadda take gudanar da bukukuwanta amma sakamakon cudanya a kan samu nason al’adu ta sanadiyyar cudanya a tsaninsu.

Al’adun auren Hausawa sun sha bam-bam dana Yarbawa amma a sanadiyyar zamantakewarsu wuri daya yasa al’adun Hausawa sukayi tasiri akan na Yarbawan mazauna Gusau, gasu kamar haka:

        i.            Nagani Ina so: Wannan wata al’ada ce da Hausawa sukeyi wadda idan Namiji ya ga Macce yana so zai saye kayyaki kamar: Cingam, Biskit, Lemu, Goro da Ruwa ya tura akai gidansu domin neman aurenta. A da Yarbawa ba su yin wannan al’adar amma a yanzu suna yi kuma suna kiran nagani ina so da “IYOJU” a harshen yarbanci.

     ii.            Lefe: kalmar ta samo asali ne daga wani akwati na kaba da Hausawa ke sakawa wanda a da shi ne ake kai kayan aure. Lefe na nufin kayan da Ango ke kaiwa Amarya a lokacin neman aure waɗanda suka hada da: Atamfofi, Leshi, Takalmi, Jikka, kayan kwalliya akwati da sauransu. A al’adar Yarbawa namiji baya yiwa Mace Lefe Idan zai aure ta sai da akwai wata al’ada ta su wadda ta yi kama da wannan, al’adar itace Ango zai yi wa Amaryar kayan cin biki, galibi wadannan kayan basu wuce kala Ukku kuma yana yin wadannan kayan ne ta hanyar yin anko tsakanin shi da Amaryar, Idan Leshi zai dunka mata ya kan saye yadi goma sha biyar ya dauki yadi goma ya bata yadi biyar. A harshen Yarbawa suna kiran wadannan kayan da “IGBA IYAWO”. To amma a sakamakon auratayya tsakanin Yarbawa da Hausawa yasa yanzu suna yin Lefe

   iii.            Kayan Ɗaki: Komattsai ne da iyayen Amarya tare da taimakon dangi suke haɗuwa a kaiwa amarya waɗanda suka hada da: Manyan Kujeru, Gado, Katifa, Durowa da makamantansu. Al’ada ce wadda Hausawa suke yi amma a sakamokon cuɗanyar Yarbawa suna yin wannan al’ada, wanda a da can hakkin waɗannan kaya sun rataya a kan Miji ne a tasu al’adar.

   iv.            Gara: Al’adar Bahaushe idan zai aurar da ‘Yarshi yana yi mata Gara (Kayan Abinci) waɗanda suka hada da Shinkafa, Taliya, Makaroni, Manja, Mangida, Manshanu da makamantansu a kai ta da su, wadda Yarbawa ba su da wannan al’ada sai dai suna da makamanciyarta, sai dai kuma akwai saɓani a tsakaninsu. A Bahaushiyar al’ada iyayen Mace su ke kai gara amma a al’adar Yarbawa Namiji ne yake sayen kayan abinci ya kai gidan iyayen yarinya tare da kuɗi da za’a rabawa danginta, wannan al’ada suna kiranta da “ERU IDANA” amma a yanzu sakamakon auratayya tsakanin al’ummun biyu suna yin Gara.

 4.0 Sakamakon Bincike

Wannan muƙala ta kawo yadda al’adun Hausawa na Aure suka yi tasiri akan na Yarbawa mazauna Gusau. Sauye-sauyen al’adun waɗanda suka haɗa da:

a.      Nagani Ina so: Wannan al’ada ce da Hausawa su ke yi wadda a yanzu haka Yarbawa suna yin ta waɗanda suke zaune a garin na Gusau

b.     Lefe: Wanda a al’adar Yarbawa basu yin shi sai sanadiyyar cudanya da Hausawa

c.      Kayan Ɗaki: Wannan wata al’adar Bahaushe ce wadda ita ma a yanzu Yarbawa mazauna Gusau suna yin ta.

d.     Gara: Wannan al’ada ce ta Bahaushe wadda ake yi lokacin aure wadda a yanzu haka Yarbawa mazauna Gusau suna yin ta.

5.0 Kammalawa

Wannan maƙala ta duba lamarin cuɗanya tsakanin Hausawa da Yarabawa. Sakamakon wannan cuɗanya ya haddasa tasirin wasu al’adu da kuma harshen Hausa a kan na Yarabawa. Maƙalar ta gano cewa har alaƙa ta auratayya ta shiga tsakanin al’ummun biyu. An yi bayanin al’ada da abunda ake nufi da tasiri tare da kawo ma’anar aure. An yi tsokaci akan al’ummar Yarbawa tare da kawo takaitaccen tarihin Gusau. An kawo yadda Yarbawa suka samu kansu a garin Gusau da mu’amular da ta shiga tsakaninsu kamar ta fannin bukukuwansu waɗanda suka hada da Bikin aure, Haihuwa da sauransu. Muƙalar ta bayyana al’adun da suka yi tasiri na bikin auren Hausawa akan na Yarbawa mazauna Gusau.

Manazarta

Abraham, R. C. (1962). Dictionary of the Hausa Language. London: Hodder Sydney.

Adamu, (2010) “The Major Landmarks in the History of Hausaland”. The Eleventh       Inaugural Lecture. Sokoto: Usmanu Ɗanfodiyo University.

Adamu, M. (1991) Hausa Factor In West African History, (Tasirin Hausawa a     Afrika ta Yamma. Zariya: Ahmadu Bello University Press.

Bargery, G. P. (1934). A Hausa-English Dictionary. London: Oɗford University Press.

Burgress, and Locke, (1953). The Family, 2nd (ed): New York. American Book. Co.

Bourhis, R. Y. (1997) Language in EthicInteraction: A Social Psychological Approach. England: Pergamon.

Bunza, A.M. (1991), “Ba Baƙo Ruwa ka sha Labari; (Ƙimar Baƙo da Baƙunci a Al’adar Bahaushe)”

CNHN (2006), Cibiyar Nazarin Al’adun Nijeriya Jami’ar Bayero Kano.

Funtua, da Gusau, (2010), Al’adu da Ɗabi’un Hausawa da Fulani El-Abbas Printers and Concepts Kaduna

Gusau, R. A. (2014) Garin Gusau a Taƙaice Gusau: Al-Huda Ventures.

Gusau, S. M da Gusau B. M. (2012) Gusau Ta Malam Sambo. Kano: Benchmark Publishers Limited.

Ibrahim, M. S. (1982) “Dangantakar Al’ada da Addini: Tasirin Musulunci a Kan             Rayuwar             Hausawa ta Gargajiya”. Kundin Digiri na Biyu. Kano: Jam’iar          Bayero.

Madabo, M.H (1979) Ciniki da Sana’o’i a Ƙasar Hausa Annuri Printers and Publication D/Rimi.

Mu’azu, A. (2013) Baƙin Al’adu a Ƙagaggun Littattafan Soyayya na Hausa.          Zariya: Ahmadu Bello University Press

Rambo, R. A. (2013), “Gwagwarmayar Kamancen Neman auren Hausawa Da Na Dakarkari”. Takardar da aka gabatar a taron ƙarawa juna Sani a Sashen Nazarin Harsunan Nijeriya. Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo, Sakkwato.

Rauf, M. A. (1977). Islamic View On Women and Family: New York: Cambrige Press.

Sallau, B.A. (2010) Wanzanci da Muhimmancinsa ga Rayuwar Hausawa. Kaduna:         Najiu             Professional Printers.

Smith, M.G. (1959) “The Hausa System of Social Status” in Africa Vol. XXVII. No. 1.

Usman A. F. (2003) “Inter-Group Relations in Gusau: A Case Study of Yoruba and Hausa C. 1920-1996. PhD Theses, Department of History Usmanu Ɗanfodiyo University Sokoto.

RATAYEN HIRARRAKI

S/No

Suna

Shekaru

Adireshi

Matsayi

Rana

1

Mal. Raji

57

Sabon-gari Gusau

Mamba a ƙungiyar Yarabawan Gusau

Alhamis 10/11/2022

Da 10:00ns

2

Haruna Umar Gusau

40

Sabon-gari Gusau

Ma’aikacin Gwamnati sashen lafiya a Gusau

Alhamis

8/12/2022

Da 5:31ny

3

Boda Radiyo

55

Sabon-gari Gusau

Mai Gyaran Radiyo

Alhamis 15/12/2022

Da 5:00ny

4

Mujiddat Abdulrauf

46

Sabon-gari Gusau

Malama

Lahadi

15/01/2023

Da 7:00nd

 

 

 



[1]A duba Bourhis, (1997) The Interactive Acculturation Model.

 

Post a Comment

0 Comments