Wakar Sardaunan Hamma’ali Malami Maigandi Ta Alhaji Musa Danba’u Gidan Buwai

    Sauraro Da Rubutawa

    Hirabri Shehu Sakkwato

    08143533314

    Amshi: Sardaunan Hamma’ali zaki,

    Malami Maigandi bi da arna. 

    Jagora: Hamma’ali mukai mu kwan biyu,

    Yara:    Malami Maigandi na bid’ata.

     

    Amshi: Sardaunan Hamma’ali zaki,

    Malami Maigandi bi da arna.

     

    Jagora: Abin da kai man hamdullahi,

    Malami Maigandi ba mu ramma.

     

    Amshi: Sardaunan Hamma’ali zaki,

    Malami Maigandi bi da arna.

     

    Jagora: Malami ka ima shirya dambe,

    Malami ka ima shirya dambe,

    In ka bugi baki da zuciya,

    Ka tabbata k’ato ya suma,

    Yara:   Sai ka yi wajen wuya ka isai.

     

    Amshi: Sardaunan Hamma’ali zaki,

    Malami Maigandi bi da arna.

     

    Jagora: Kada ka ce ni ina gama ni,

    Kada ka ce ni ina gama ni,

    Kowa na gaya maka da zahi,

    Yara:   To kai ma gaya masa da zahi.

     

    Jagora: In kowa na gaya maka da zahi,

    Yara:   To kai ma gaya masa da zahi.

     

    Jagora: Don zaki in ya kai k’arhi,

    Yara:    Bai jin tsoron karo da giwa

    Jagora: A d’an sarki in ya gawurta,

    Yara:    Bai jin tsoron karo da sarki.

     

    Amshi: Sardaunan Hamma’ali zaki,

    Malami Maigandi bi da arna.

     

    Jagora: A Hamma’ali na tafi yawo,

    Ga wani nai muna kurin banza,

    Ya ce shi aka wa Sardauna,

    Sai nac ce kauce da nesa,

    Yara:   Kusun kusumi ba ya kyau da sarki.

     

    Amshi: Sardaunan Hamma’ali zaki,

    Malami Maigandi bi da arna.

     

    Jagora: Cikin ‘yan sarki na Hamma’ali,

    Akwai wani sata yakai da rana,

    Shi wannan ya zame muzuru×2

    Yara:   ‘Yan kaji bai bari su girma.

     

    Amshi: Sardaunan Hamma’ali zaki,

    Malami Maigandi bi da arna

     

    Jagora: Na sauka Kware don in ga ciyaman,

    Na tahi ofis sai nig gaisai,

    Sai ya ce ba ni kud’d’in mai,

    Da ya ce a ba ni kud’in mai,

    Ni yi jira ba a mik’a min ba,

    Ni mamaki ya kama ni,

    Ga rijiya ta ba da ruwanta,

    Yara:   Sai guga ta hana a d’ebo.

     

    Amshi: Sardaunan Hamma’ali zaki,

    Malami Maigandi bi da arna.

     

    https://www.amsoshi.com/2018/01/15/wakar-ciyaman-din-shagari-alhaji-madu-galadima-horo-ta-alhaji-musa-danbau-gidan-buwai/

    Jagora: A D’anmaliki na Kware dwatijo,

    Haji Hayatu na gode mai,

    Yara:   ‘Danba’u ya yaba da girma.

     

    Jagora: D’anmaliki na Kware mai nera,

    Ka ga ta kowa d’an dattijo,

    Sun kauce maka ko don dole,

    Im Haji Hayatu na gode ma,

    Yara:   ‘Danba’u ya yaba da girma.

     

    Jagora: A Alhaji Arziki D’ankwangila,

    Yara:   ‘Danba’u ya yaba da girma.

     

    Jagora: A D’annayintin ban rena mai ba,

    Yara:    ‘Danba’u ya yaba da girma.

     

    Jagora: Alhaji Aminu gaida D’ankabo,

    ‘Danba’u ya yaba da girma.

     

    Jagora: A ni D’ankabo Alhaji Aminu,

    Yara:    ‘Danba’u ya yaba da girma.

     

    Jagora: A ni Bello tihwa ba rana mai ba,

    Yara:    ‘Danba’u ya yaba da girma.

     

    Jagora: A ga Bushiya mai naman rago,

    Yara:    ‘Danba’u ya yaba da girma.

     

    Jagora: A Bagobiran nan ta D’antasakku,

    ‘Danba’u ya yaba da girma×2

     

    Jagora: A ni shugaba Raha na gode,

    Yara:   ‘Danba’u ya yaba da girma.

     

    Jagora: Rai ya dad’ewa mai tayoyi,

    Mai kamfanin taya na gode.

    Yara:   ‘Danba’u ya yaba da girma.

    No comments:

    Post a Comment

    ENGLISH: You are warmly invited to share your comments or ask questions regarding this post or related topics of interest. Your feedback serves as evidence of your appreciation for our hard work and ongoing efforts to sustain this extensive and informative blog. We value your input and engagement.

    HAUSA: Kuna iya rubuto mana tsokaci ko tambayoyi a ƙasa. Tsokacinku game da abubuwan da muke ɗorawa shi zai tabbatar mana cewa mutane suna amfana da wannan ƙoƙari da muke yi na tattaro muku ɗimbin ilimummuka a wannan kafar intanet.