Ticker

6/recent/ticker-posts

Jigon Tarbiyya A Wasu Waƙoƙin Alhaji Ɗahiru Musa Jahun Bauchi

Article Citation: Yankara, M. M. and Sifawa, H. S. (2018). Jigon Tarbiyya Cikin Wasu Waƙoƙin Alhaji Ɗahiru Musa Jahun Bauchi. Ɗunɗaye Journal of Hausa Studies, 2 (1). Department of Nigerian Languages. Sokoto: Usmanu Ɗanfodiyo University. P 161-176.

Jigon Tarbiyya A Wasu Waƙoƙin Alhaji Ɗahiru Musa Jahun Bauchi

DAGA

Muhammad Musa Yankara
Department of Registry,
Fedaral University Dutsin-Ma, Katsina.
esemwaiy12@gmail.com 

Da

Hadiza Salman Sifawa
Department of Languages,
Shehu Shagari College of Education, Sokoto.
dijeskk17@gmail.com

Tsakure

Tarbiyya kyakkyawar hanyar rayuwa ce da ake gina mutum kanta tun yana yaro. Tun a yarinta alamu ke fara bayyana na kyakkyawar tarbiyya ko akasin haka. Ita alama cikin kowane abu tana da muhimmanci. Sai ta bayyana sannan haƙiƙanin al’amari yake zuwa, Bunza (2016). Wannan maƙala za ta yi tsokaci ne a kan yadda Alhaji Ɗahiru Musa Jahun Bauchi ya yi amfani da hikima da basira da kuma dabaru a cikin waqarsa domin, tarbiyyantar da al’umma a kan rayuwa ta ƙwarai wadda kowa zai yi na’am da ita. Takardar za ta yi ƙoƙari ne wajen zaƙulo dukkan ɓangarori na rayuwa da ya shafi tarbiyya wanda ya zo a cikin waƙoƙin marubucin.

 

1.0               Gabatarwa

Waƙa muhimmin rukuni ne na adabi da ta cancanci a yi mata kirari da “Nagge daɗi goma”. Dalili kuwa shi ne, a kowane harshe na duniya waƙa ita ce kan gaba wajen bunƙasa da ɗaukakar adabin wannan harshe, domin ita ta nashe dukkan sassa na rayuwar al’ummar da ke magana da harshen. Waƙa takan yi ruwa da tsaki kusan a kowane fanni na rayuwar al’umma. Ana iya gyara al’umma ta zama masu kyawawan halaye da ita, ko kuma a gurɓata ta da ita; ana iya tunzura mutane ko a zuga su zuwa ga fusata ko kuma a kwantar masu da hankali da ita; ana iya ba su ilimi cikin sauƙi har su gwanance ko kuma a jawo hankalinsu zuwa ga muhimmin abu, a wayar musu da kai da ita; ana ƙwarzanta abu komin ƙanƙantarsa ko a ƙara masa gishiri ko a kushe shi a wulaƙanta shi da ita. Waƙa tana da asirin tilasta a yarda ko a amince da abu komai muninsa da ƙazantarsa ko cutarwarsa, kamar yadda take halasta a ƙyamaci abu duk kyawunsa da amfaninsa ko muhimmancinsa. Dukkan waɗannan darajojin baiwa ce da Allah ya hore wa mawaƙa domin bayar da gudummuwarsu ga al’umma tare da cin karensu ba babbaka wajen sarrafa kalmomin harshensu da gwanancewarsu yadda suke so.

Bahaushe kamar yadda sauran mutane suke, tun tale-tale mutum ne da bai iya zama sai da tarbiyya. Tarbiyyar nan kuwa ta jikinsa ce ko ta ruhinsa, wato rayuwarsa. Saboda haka, ba zai taɓa zama lafiya ba sai da tarbiyya, ta ƙashin kansa da ta iyalinsa da kuma jama’ar da yake rayuwa da su. Irin hakan ne ya sa tun kafin Bahaushe ya iya karatu da rubutu Allah ya yi masa baiwar hikimomi da dabaru na yi wa kansa, da ‘ya’yansa da sauran al’ummar da yake zama cikinta tarbiyya.

Daga cikin ire-iren waɗannan hanyoyi na tarbiyyar Bahaushe a gargajiyance, akwai tatsuniyoyi da waƙoƙin yara na mata da na maza. Lokacin da ya samu ilimi, sai ya ƙara samun wasu dabaru na yin tarbiyya ta hanyar rubutu wanda ya kai ga yana bayar da ita a litattafai, har ma aka samu rubutattun waƙoƙin Hausa su ma suka fara taka tasu rawar a wannan fagen duk da cewa dai ba su yawaita ba.

Tsinkayar tarbiyya a irin waɗannan rubutattun waƙoƙin ne ya sa wannan takarda yin kutse cikin diwanin Alhaji Ɗahiru Musa Jahun Bauchi, domin zaƙulo da fito da jigon don amfanuwar al’umma.

2.0               Taƙaitaccen Tarihin Alhaji Ɗahiru Musa Jahun Bauchi

An haifi Alhaji Ɗahiru Musa Jahun, a cikin shekarar 1942 a unguwar Jahun da ke cikin garin Bauchi. Bayan ya sauke Alƙur’ani da shekara takwas a makarantar Allo ta Malam Maigari, sai babban yayansa Liman Muhammadu Inuwa, wanda a hannunsa ya taso tun haihuwarsa kasancewar mahaifinsu ya rasu, ya tura shi Gombe domin ƙaro ilimi da sanin Alƙur’ani sosai. Alhaji Ɗahiru ya karanci litattafan addinin Musulunci da suka haɗa da Iziyya da Risala da Alburda, da kuma Ishiriniya a wajen Malam Aminu Murshidi a garin Gombe.

Sakamakon gidansu Alhaji Ɗahiru Musa Jahun duk malaman addini ne, sai ya zama bai samu damar xanxanar zaƙin karatun boko ba, duk da sha’awa da ƙaunar da ya nuna gare shi domin kuwa, sai da ya taɓa saka kansa a furamare, bayan da aka gane yana zuwa ne aka fitar da shi.

Alhaji Ɗahiru Musa Jahun ya yi sana’o’i da dama bayan kammala karatunsa na addini da ya haɗa da ɗinki, da gini, da kuma gyaran keke. Sannan a lokaci ɗaya kuma yana koyon rubutun Hausa ta hanyar yaƙi da jahilci wanda da haka ya fara rubuta waƙoƙinsa.

Alhaji Ɗahiru Musa Jahun ya fara rubuta waƙoƙi ne tun yana ɗan shekara sha uku, a in da samari da ‘yan mata ke taruwa shi kuma yana rera masu suna saurare. Ya rubuta waƙoƙi masu tarin yawa a fannoni daban-daban na rayuwar al’umma, kamar siyasa, haɗin kai, bukukuwa, sarauta, da kuma tarbiyya. Sai dai waƙoƙin da suka fi fito da shi, su ne waɗanda ya ke yi domin, tarbiyyantar da jama’a. Haka kuma ya samu lambar yabo da jinjina a wurin mutane daban-daban, kamar irinsu Sarkin Bauchi Alhaji Sulaimanu Adamu, da kuma lambar yabo ta qasa-da-qasa da aka ba shi lokacin mulkin Shugaban Ƙasar Najeriya Olusegun Obasanjo.

Ya zuwa yanzu, Alhaji Ɗahiru Musa Jahun yana nan da rayuwarsa, zaune a Unguwar Jahun Layin Liman Mai rasuwa Bauchi, da kimanin shekaru 75 a duniya, kuma yana da mata 4 da ‘ya’ya 42 tare da jikoki masu yawa. Sannan har yanzu yana rubuta waƙoƙin tarbiyya da kuma waɗanda suka shafi rayuwar jama’a ta fuskoki daban-daban.

3.0               Ma’anar Tarbiyya

Kalmar tarbiyya abu ce wadda ta sha luguden ma’anoni daga bakunan masana da manazarta. Daga cikin waɗanda suka tofa albarkacin bakinsu dangane da ma’anar Kalmar akwai, Gusau (1999) da yake kallon tarbiyya a matsayin “wata hanya ce ta kyautata rayuwar ɗan Adam da shigar da shi ya zuwa halaye da ɗabi’u masu kyau da nagarta. Ta yin haka zai sa ya tashi da ƙima da ƙwarjini da ganin mutuncin abokan zamansa, sannan ya riƙa ba kowa haqqinsa daidai yadda ya kamata gwargwadon hali.

Yahya (2001) cewa ya yi “tarbiya kalma ce wadda Bahaushe ya aro daga Larabci kaitsaye watau kamar yadda take ba tare da wata sakayawa ba, wadda kuma ta Hausa gangariya take da ma’anar ‘reno’, domin wanda ake yi wa shi samu dukkan halaye da ɗabi’un da mai yin renon yake son gani.

Bunza (2002) ya tafi a kan cewa ‘tarbiyya tana nufin samun kyakkyawan horo ga mutum ya zama masanin kyawun abubuwa na ɗabi’un hulɗa da jama’a da ladabi, da biyayya, da kamun kai, da kasancewa mai jin kunya da kyakkyawan maƙasudi.

Tarbiyya ita ce koyar da hali nagari (CNH 2006).

Shehu (2011) ya tafi a kan cewa tarbiyya na nufin “aza wani mutum bisa wata hanya da zai koyi wani abu wanda zai amfane shi a rayuwarsa da ma sauran jama’arsa baki ɗaya.

Tarbiya ta shafi gina mutum a bisa halayen da al’ummarsa ta aminta da su na kunya da ƙwazo da ladabi da biyayya da girmama na gaba da kishin kai da riƙe iyali da taimakon juna da haɗin kai da son aikata alheri da nisantar kwaɗayi da rowa da sauransu (Bunza 2012).

Ita kuwa Bugaje (2013) cewa ta yi, “tarbiyya ta kasance ma’aunin gane darajar mutum da al’ummar da ya fito domin, haka ana tarbiyya da nufin a sami al’umma tagari, nagartatta.

Bunza (2016) ya ce “tarbiyya hanya ce ta gina yaro don kasancewarsa mutum nagari a lokacin kammalar tunaninsa da hankalinsa. Wannan zai sa ya ja linzamin rayuwarsa da na makusantansa a hanya madaidaiciya, ya amfani kansa a kuma amfana da shi.

Ta la’akari da ma’anoni na tarbiyya da masana da manzarta suka kawo a sama, nake ganin tarbiyya a matsayin dabarar gina rayuwa mai inganci don samun dukkan halayen kamalar mutuntaka da ɗabi’un dattaku domin, kasancewa abin yabawa da sambarka.

3.1               Jigon Tarbiyya a Cikin Waƙoƙin Alhaji Ɗahiru Musa Jahun

Tarbiyya wani babban jigo ne ga rayuwar Bahaushe wanda idan babu tsarin tarbiyya a rayuwa lallai mutum zai kasance tamkar dabba, kuma abin ƙyama wanda sauran jama’a ba za su so yin mu’amala da shi cikin kowane sha’ani ba.

Kasancewar mutum mai kammalalliyar tarbiyya, dole ne ya zama mai kunya, da gaskiya, da riƙon amana, da haƙuri, da tausayi, da kare mutuncin kai, da kishi, da neman ilimi, da abokai nagari, da haɗin kai, da taimakon mabuƙata, da tsafta, da ƙana’a, da tawali’u da kuma neman na kai da biyayya ko ɗa’a ga magabata da sauransu. Ire-iren waɗannan abubuwa kuwa, koyar da su ake yi domin, ganin an samar da mutum nagari a cikin al’umma tun yana ƙarami har zuwa girma. Alhaji Ɗahiru Musa Jahun gwani ne wajen tsara waƙoƙin da suka shafi gina tarbiyya tsantsa, wanda waƙoƙin nasa suna tattare da ire-iren waɗannan halaye da ake buƙatar gani a wurin mutanen kirki kamar yadda misalai za su nuna.

3.1.1        Gaskiya

Makaɗa Kassu Zurmi ya yi wa gaskiya take da cewa, “Gaskiya mugunyar magana, ba a sonki sai kin tsufa”. Abin da wannan makaɗi ke nufi bai wuce zancen nan na masu hikima ba da suke cewa, “Gaskiya ɗaci gareta”. Wato ita gaskiya ba ta da daɗi a lokacin da aka ji ta sai bayan an aikata ta sai a ji daɗi.

Mustapha, (2003:56-7) ya zayyano ma’anar gaskiya daga bakin masana kamar haka:

Yin abin da ya kamata ba tare da ƙari ko ragi ba, (Gusau 1984).

Gaskiya ita ce, aikata wani aiki ko furta wata magana da al’umma suka aminta da kasancewarsa gaskiya. Haka kuma, wannan aiki ko maganar ya kasance abu ne tabbatacce ga idon Bahaushe a ma’aunin al’adarsa, kuma ya zamo abu ne mai ɗorewa ba mai gushewa ba, domin a daɗe ana yi sai gaskiya, (Bunza 2002).

Gaskiya shi ne faɗin daidai a cikin tunanin ɗan Adam da aikata daidai a cikin harkokinsa, tare da neman gano ko rarrabe abin da ke tsakanin tunanin ɗan Adam da dabba, ko a da lokacin zaman gargajiya, ko a yanzu da addinin Musulunci tare da sauyawar zamani ta zo, (Mu’azu (…..)).

Bisa lura da abin da masana suka ambata dangane da gaskiya, za a iya cewa; Gaskiya shi ne faɗin abu yadda yake, ko ba da labari bisa tabbaci da haƙiƙa ba tare da shakka ko kokwanto ba.

Yin gaskiya ta kowace hanya abu ne mai kyau da amfani ga mutane a tsarin zamantakewa. Dangane da haka ne Alhaji Ɗahiru Musa Jahun ya duƙufa wajen ganin ya ɗora al’umma a kan turbar gaskiya, da faɗinta da kuma aikata ta komai ɗaci da wahalarta a tsarin rayuwa. Ga misalai a cikin wasu waƙoƙinsa kamar haka:

‘Yan kasuwa a yi ƙoƙari,

A yi gaskiya a yi hanƙuri,

Kwana da wayunwan gari,

 Wataran buƙata zai biya.

(Ɗahiru Jahun:Tarbiyya II)

 

Jama’a a bar yin maguɗi,

 A yi gaskiya a yi tarbiya.

 

Ku ɗalibai in gaya muku,

Ko ko in ƙara tuna muku,

Komai izan ya matsa muku,

 Ku faɗi ta hanyar gaskiya.

(Ɗahiru Jahun:Tarbiyya III)

 

9. Gyara kayanka domin sanin haƙƙi,

Mai riƙon gaskiya bai shiga kunya.

(Ɗahiru Jahun:Gyara Kayanka Bakandamiya)

 

Misalan da wannan marubuci ya kawo na koyar da tsayawa tsayin daka ne a kan gaskiya. Wato duk abin da mutum zai yi, to ya yi ƙoƙarin ganin ya yi gaskiya ya kiyayi maguɗi da mugunta a cikinsa domin, mai gaskiya bai shan kunya. Haka kuma duk abin da mutum zai faɗa, to ya yi ƙoƙari a ji gaskiya ce ta fito daga bakinsa.

 

3.1.2        Riƙon Amana

Ita dai kalmar amana asalinta daga harshen Larabci take. Hausawa suka aro ta suna amfani da ita kamar yadda take a cikin harshen Larabci. Kalmar tana nufin aminci, wato yarda. Yarda kuwa na iya kasancewa a kan kowace irin hulɗa da ake iya samu a tsakanin mutune. Wannan shi ya sa mutumin da ba ya da riƙon amana wato ba yardadde ba, yake kasancewa abin ƙyama a cikin al’umma.

Masana da dama sun tofa albarkacin bakinsu dangane da ma’anar amana a Hausa, daga cikin waɗannan masana akwai Bargery (1934:27), wanda ya bayyana ma’anar amana a matsayin kyakkyawar fahimta ko yarjewa mutum a kan wani abu. Haka kuma, ya ƙara da cewa amana na iya ɗaukar ma’anar dogara da ban gaskiya a kan abu.

Newman, (1997:289) an bayar da ma’anar amana da amincewa da yarda da mutum.

A cikin Ƙamusun Hausa (2006:15) an bayyana amana da ba mutum ajiyar kaya ko wani abu yadda zai adana shi kamar nasa ba tare da wani abu ya salwanta ko wani abu ya same shi ba.

A Hausance, Amana na nufin mutum ya kula da wani abu da aka damƙa masa kada ya bari ya lalace ko ya salwanta, (Ibrahim, 2013:186). Idan ya kasance mutum mai amana ne to al’amuransa sukan yi kyau. Idan aka ci amana kuma a sami akasi.

Buƙatuwar gina al’umma bisa tarbiyyar riƙon amana tasa Alhaji Ɗahiru Musa Jahun a cikin waqoqinsa ke cewa;

Kuma sai mu gaida ma’aikata,

Wasu na shiga wasu na fita

Dukkanku ƙwan ku da kwarkwata,

 Ku riƙe amanan gaskiya.

(Ɗahiru Jahun:Tarbiyya II)

 

58. Gyara kayanka duk wanda ke aiki,

 An fi son mai amana da tarbiyya.

(Ɗahiru Jahun:Gyara Kayanka Bakandamiya)

Waɗannan baitoci na Alhaji Ɗahiru na nuna cewa a cikin al’umma ba wanda aka fi so kamar mai riƙon amana, mai gaskiya. Don haka ya ke kiran mutane a kan riƙon amana cikin dukkan ayyukansu da suka sa gaba.

3.1.3        Kunya da Kawaici

Kunya kamar yadda Yahya da wasu (1992:82) suka bayyana “ta ƙunshi hana harshe yin munanan maganganu da ƙiya wa gaɓɓan jikin mutum aikata miyagun ayyuka.

A wata ma’anar kuma, Balbasatu (2009:62) cewa ta yi, “Kunya na nufin jin nauyi da girmamawa ko karamcin da ake yi wa wani na gaba da mutum ko masoyi ko ‘ya’ya ko surukai ko baƙo.

Kunya na nufin halin ɗa’a da kawaici ko a aikace ko a magance. Kunya ɗabi’a ce kyakkyawa da kan jawo wa mai ita daraja da girmamawa a cikin mutane, (Garba 2010:20).

Kunya tana matuƙar taka rawa wajen nuna zurfin kamala da halayen ƙwarai na mutum domin, siffa ce daga cikin siffofin da ake gane mutum mai tarbiyya. Alhaji Ɗahiru Musa Jahun a ƙoƙarinsa na tarbiyyantar da al’umma yin kunya, ya kawo baitoci masu nuni da kyawun kunya ga mutum a cikin waƙoƙinsa kamar haka:

Suturar jikinki ta yalwata,

Surar jikinmu ya ɗan ɓata,

Da wuya ace an kunyata,

 In an bi hanyar gaskiya.

(Ɗahiru Jahun:Tarbiyya II)

Tsiraici abu ne da ake buƙatar ɓoyewa. Duk mutum mai hankali da kunya ba zai so ya bayyanar da tsiraicinsa ba. Illar bayyanar da tsiraici ga mata ne baitukan Sha’irin ke ƙoƙarin nunawa da cewa, duk mace mai kunya ba za ta bar jikinta a buɗe ba kamar moɗar randar bakin kasuwa. A cikin wani baitin kuwa cewa yake:

49. ‘Yan acaɓa ku inganta halinku,

Mai biɗar arziƙi bai rashin kunya.

 

51. Don waɗansunku kan sa a zarge ku,

Ga rashin hankali ga rashin kunya.

 

53. Masu tuƙi na mota waɗansun su,

Kan gwada ba mutunci bare kunya.

 

85. Gyara kaya tuni ne ga matanmu,

Kar a faɗa tafarkin rashin kunya.

(Ɗahiru Jahun: Gyara kayanka: Bakandamiya)

Wato muddin ana son inganta sana’a dole sai an haɗa da kunya domin, rashin kunya na jawo zargi da tsana a wajen jama’a. Har ila yau marubucin ya sake bayyana yadda ake son mutum ya kasance mai kunya a cikin sana’arsa a cikin baitin da ya ke cewa:

Amma gyaran da za ku soma,

Farko ku rage yawan zalama,

Ko buɗe ido da nuna tsama,

Tsiwa da tsuma da nuna tsama,

 Da tsageranci cikin mutane.

(Ɗahiru Jahun: Sana’ar Acaɓa).

3.1.4        Haƙuri

Hausawa na cewa “mai haƙuri yakan dafa dutse har ya sha romonsa”. Haƙuri kamar yadda Adamawa (2007) ya bayyana, shi ne juriya ko shanye wani abu na ɓacin rai ko na rashin daɗi, wato haƙuri da ƙin maida martani don haifar da maslaha. Haƙuri yana yalwata zuciya da janyo soyayyar mutane, kuma yana hana yin nadama. Shi yasa ma Hausawa suka ce “Haƙuri maganin zaman duniya” domin, duk wanda ya laƙanci yin haƙuri to ya sami kyakkyawar shaida a rayuwa. Masu haƙuri su ke tabbatar da wanzuwar zaman lafiya a gida da gari da kuma al’umma baki ɗaya.

Tarbiyya tana ingantuwa ne da haƙuri, wanda hakan yasa Alhaji Ɗahiru Musa Jahun ya ke kwaɓar jama’a don tarbiyyantar da su haƙuri a cikin waƙoƙinsa kamar haka:

To dole sai mu yi yunƙuri,

Mu yi dauriya mu yi ƙoƙari,

Haɗa kanmu ƙauye ko gari,

 Da nufin a maido tarbiyya.

 

To ‘yan uwa mu yi ƙoƙari,

Mu yi dauriya mu yi hanƙuri,

A ƙasarmu daji ko gari,

 Kowa ya yarda da tarbiyya.

 

To ‘yan uwa mu yi ƙoƙari,

Mu yi dauriya mu yi hanƙuri,

Mu yi maganin mutakabiri,

 Daga nesa ba shi da tarbiyya.

(Ɗahiru Jahun:Tarbiyya II)

Haƙuri a kan dukkan wani abu da mutum yasa gaba na rayuwa shi Sha’irin ke ƙoƙarin nunawa a cikin waɗannan baitoci. Sha’irin na nuna komai mutum zai yi to dole sai ya yi haƙuri a cikinsa matuƙar yana son cimma muradi. Haka kuma ya nuna ba a samun nasara a zamantakewa sai da haƙuri.

3.1.5        Wadatar Zuci

Wadatar zuci shi ne akasin kwaɗayi, rashin ƙwallafa rai kan samu ko mallakar abin da wani ya mallaka na rayuwar duniya. Wato gamsuwa da abin da ka mallaka komai ƙarancinsa, da rashin damuwa da abin da wasu suka mallaka komai yawansa shi ne wadatar zuci.

Wadatar zuci wani muhimmin makami ne na kyautata tarbiyyar al’umma. A duk lokacin da mutane suka kasance masu wadatar zuci, to sai kishin kai ya shige su, su zama ba su hassadar abin da ke hannun wani. Dukkan mutumin da Allah ya ba wadatar zuci, ya yi dace domin zai zama mai natsuwa da kwanciyar rai a koyaushe. Haka a duk lokacin da wadatar zuci ya bazu a zukatan jama’a, to lumana da zaman lafiya za su samu a tsakaninsu. Haka lalaci irin na sace-sace da ƙyashi da jiye wa juna za su ragu sosai in har ma ba su gushe ba gaba ɗaya. (Bunza, 2012).

A koyaushe a cikin al’umma a kan samu wasu jama’a da ke yin iya ƙoƙarinsu domin faɗakar da mutane su zama masu wadatar zuci dangane da abin da Allah ya hore musu domin kauce wa faɗawa a wata muguwar hanyar da za ta ɓata tarbiyyarsu, ta fitar da su daga gurbin mutane na gari.

Alhaji Ɗahiru Musa Jahun ya ƙoƙarta wajen tarbiyyantar da al’umma wadatar zuci a cikin waƙoƙinsa, kamar yadda ya ke cewa:

Najeriyanmu ƙasa ɗaya,

Kuma ga mu al’umma ɗaya,

Jama’a a bar son zuciya,

 Ɗa’a ta samu da tarbiyya.

 

Jama’a a nai mana gargaɗi,

Mu rage azabar son kuɗi,

Wasu na ta haddasa maguɗi,

 Sunansu ba su da tarbiya.

 

Ku saya ku saida halaliya,

Riba kaɗan mu yi godiya,

Duka sun ƙi gwamma haramiya,

 Ba sa da ɗa’a tarbiya.

 

Ba wai ka mallaki naka ba,

Ka fito ka handami namu ba,

Baka san kana kashe kan ka ba,

 Don son gwanintan duniya.

(Ɗahiru Jahun:Tarbiyya II)

Son zuciya kan haifar da maguɗi da hassada da handama da son duniya. Duba ga wannan da hanin jama’a kan yin su shi ne Sha’irin ya ke kiran jama’a a kansu cikin baitukan da suka gabata.

A cikin wata waƙar kuwa ga abin da yake cewa dangane da tallar da iyaye ke ɗorawa yara domin neman abin duniya:

Wasu gun talla ɗa’a takan rushe,

Har su koyo ɗabi’un rashin kunya.

(Ɗahiru Jahun: Gyara kayanka Bakandamiya).

Rashin haƙurin wasu iyaye kan jefa yara cikin miyagun ɗabi’un da ƙarshe za a zo ana da-na-sani wanda da sun sami wadatar zuciya da hakan bai faru da ‘ya’yansu ba kamar yadda baitocin waƙar ke nuni. Har wayau marubucin ya sake cewa:

7. shirin gyara kayanka ne ke faɗi,

Musamman a azure na yin gargaɗi,

A taso a barci a bar gyangyaɗi,

A yaƙi dukkan ayyukan maguɗi,

Na masu zalama da yunwar kuɗi,

Misali ta manya da ‘yan burbuɗi,

Na sa yara talla farautar kuɗi,

Ka gansu a lungu cikin turbuɗi,

Da ɗai ba karatu bare tarbiyya.

(Ɗahiru Jahun: Ceton ‘yar talla)

 

Idan aka dubi waɗannan misalai za a ga cewa babban saƙon da waqar take ƙarfafawa shi ne, mutum ya zama mai wadatar zuci watau ƙana’a. Haƙuri da kaɗan shi ne babbar nasara da nuna godiyar Allah, in kuwa aka ce sai an samu mai yawa to take-yanke za a faɗa cikin haramiya da kuma ɓarnar da ba ta da makari.

3.1.6        Zumunta

Ƙoƙarin kusantar ‘yan uwa da abokan arziƙi, da ziyartarsu a kai a kai, da riƙe dangi ba tare da zaɓunta ko son kai ba, wannan ita ce zumunta. (Zarruƙ da wasu, 1988). Tarbiyyar Hausa tana jaddada ziyarce-ziyarce tsakanin ‘yan uwa da abokan arziƙi. Har ma Hausawa suna cewa “Zumunta a ƙafa take”. A cikin kowace irin al’umma ana alfahari da mutum mai sa da zumunci. Wannan tasa Alhaji Ɗahiru Musa Jahun domin ƙarfafar zumunta a waƙarsa ta Tarbiyya II ya ke cewa:

Son ‘yan uwa shi ne gaba,

Ka so shi ba zai ƙi ka ba,

Ba ka nuna ka so kanka ba,

 Zai sa a zauna lafiya.

(Ɗahiru Jahun:Tarbiyya II)

Wato dai abin da Sha’irin yake nuna wa mutane a wannan baiti shi ne, su yi ƙoƙari su riƙe ‘yan uwansu domin, shi ne gaba ga komai da ke wanzar da zaman lafiya da son juna.

3.1.7        Kare mutumcin kai

‘Tsira da mutumci ya fi tsira da kaya’ inji masu hikimar zance. Sanin darajar kai da tsare kai da kuma tsare mutuncin sauran mutane yana daga cikin mutunci, musamman idan aka darajantasu saboda shekarunsu ko ilminsu ko kuma saboda kasancewar su mutane na ƙwarai. Mutunci shi ne mutum ya ji kunyar aikata duk wani abin da zai zubar masa da darajarsa. Mutunci shi ne mutum ya saba wa kansa da kiyaye halaye mafiya kyau da cika. Wato kada ka aikata wulaƙantaccen abu. Kada ka nuna halin ƙasƙanci wanda zai rage darajarka ka zama ba ka da girma wurin ‘ya’uwa (Abubakar 1966:21).

Mutunci abu ne mai kyau da kusan kowane mutum yake maraba da shi domin, yana taimaka wa zaman lafiya ya tabbata, tare da ɗaukaka darajar al’umma kamar yadda tufafi kan suturta mutum, abinci kan kyautata lafiyar jiki a sami kuzari. Mutunci yakan ƙarfafi darajar mutum da kuma al’umma baki ɗaya. Alhaji Ɗahiru Musa Jahun yana faxakar da al’umma dangane da kare mutuncin kai da sanin daraja da ƙima a cikin waƙoƙinsa. Misali

Dama mutunci ne mutun,

In ba mutunci ba mutun,

Mai hankali ka riƙe batun,

 Ladabi da ɗa’a tarbiya.

 

Bari nuna kai ɗan wane ne,

Ko don ace kai wane ne,

Kowanmu ai ɗan wane ne,

 Don kar ka ja mana tankiya.

(Ɗahiru Jahun:Tarbiyya II)

 

Har wayau, a wani wuri Marubucin a cikin waqar Gyara Kayanka yana cewa;

12. Gyara kayanka domin gudun sharri,

 Duniya lahira kar a sha kunya.

 

22. Gyara kayanka kan malam ilmu,

 Kar a koya wa yara rashin kunya.

 

23. lakcaran Jami’a ko mu ce tica,

 Mun yi fatan a inganta tarbiyya.

 

24. Don sifofi ɗabi’un waɗansun ku,

 Kan gwada ba su daidai da tarbiyya.

 

25. Tun da yara sukan ɗau sifar malam,

 Bar fitowa da siffar rashin kunya.

(Ɗahiru Jahun: Gyara kayanka Bakandamiya)

Da jin waɗannan kalamai na cikin baitocin wannan waqa za a fahimci cewa kashedi ne ake yi wa mutum ko hannunka mai sanda game da irin yadda ake so duk abin da zai yi, to ya yi ƙoƙarin kare mutumcinsa. Kar ya aikata abin da za a zarge shi domin, mutunci Hausawa sun ce “madara ne”. an kuwa yi amanna cewa madara idan ta zube ƙasa to ba kwasuwa take yi ba.

3.1.8         Haɗin kai da Zama tare

Hausawa sukan ce, “Mutum na mutane ne”. watau mutum in dai mai lafiya ne, to ya kamata a san shi tare da mutane, ba a ga yana janye jiki yana zama shi kaɗai ba. Da zarar aka samu jituwa a cikin al’amari, to za a tarar da komai na tafiya salin-alin ba kace-nace a cikin al’umma. Waƙoƙin Alhaji Ɗahiru Musa Jahun suna tarbiyyantar da jama’a muhimmancin haɗin kai, kamar yadda wasu misali za su nuna, in da marubucin ke cewa:

Ya ‘yan ƙasan nan ‘yan uwa,

Mu haɗe mu yarda da ‘yan uwa,

Mu zama muna son ‘yan uwa,

 Mu haɗe mu gyara Najeriya.

Zancen ƙabilanci kuwa,

Mai yinta zai shiga damuwa,

Shi zai ci kansa ya sha ruwa,

 Mun gane ba shi da tarbiya.

Kai mai ƙabilanci bari,

Ko nuna bambancin gari,

Mu dai muna maka shawari,

 Ka zama mutum mai tarbiya.

Muddin ba mu haɗa kanmu ba,

Ba za mu kai burinmu ba,

Ra’ayinmu in ya rarraba,

 Zai rarraba mana tarbiya.

(Ɗahiru Jahun:Tarbiyya II)

Ta lura da lafazin wannan Sha’ira, za a ga cewa ba qaramin fa’ida ke akwai ba na haxin kai. Don kuwa zaman lafiya ba zai tava wanzuwa ba idan har akwai rashin jituwa tsakanin al’ummar da ke rayuwa a wuri xaya, kuma ita kanta qasa ba yadda za ayi ta ci gaba, ballantana har jama’ar qasar su more amfaninta matuqar babu haxin kai da zaman lafiya tsakaninsu.

3.1.9        Tsafta

Cikakkiyar kula ga jiki, da tufafi, da wurin zama, da duk wani abin mu’amala mai alaƙa da mutum, ta hanyar gyara shi, da inganta shi da tsaftace shi zuwa ga mafi dacewar kama ko yanayin da ya fi ƙayatarwa da jan hankali, shi ne tsafta.

Ban da kasancewar tsafta cikon addini, takan jawo farin jini da ƙauna ga jama’a. Mutane kan yi na’am da maraba da mai tsafta, sannan takan sa masa farin jini da duk wani abu da ya dangance shi. Hakan yasa masana da manazarta suka duƙufa wajen tsawatarwa game da tarbiyyar tsafta. Alhaji Ɗahiru Musa Jahun na sahun gaba wajen ba da gudummuwarsa ta fuskar waƙa don kula da tsafta, kamar yadda misalan wasu daga cikin baitocin waƙoƙinsa ke nunawa kamar haka;

73. Tsaftace zuciya tsaftace aiki,

Gyara kayanka inganta tarbiyya.

 

75. Gyara kayanka tsafta cikin Ofis,

Har gidaje da gona da kan hanya.

(Ɗahiru Jahun: Gyara kayanka Bakandamiya)

Da farko ya nusar da mutane ne dangane da tsaftace niyya a cikin kowane irin aiki da mutum zai yi. Ma-da-mar ba a samu kyakkyawar niyya a cikin kowane irin aiki ba, to lallai za a iya fuskantar gajiyawa. Sannan kuma sai kiyaye ko kula da tsaftar jiki, da abinci da muhalli.

 

 6. ‘Yan karkara ƙauye ko birane,

Samun rashin tsafta kuskure ne,

 To gyara kayanka kar ka manta.

 

10. To gyara kayanka sai a lura,

Tsaftar jiki ɗaki ko ta shara,

 Sai masu Imani ke kula ta.

 

12. To gyara kayanka don kulawa,

Kan wanda ke tsafta sai daɗawa,

 Domin rashin tsafta ba a son ta.

 

13. Tsaftar jiki ita kam zahirun ne,

Farkon shirin tsafta ya mutane,

 Kowa ya ɗau tsafta can zukata.

 

39. Kowa da sunansa ya mutane,

To ko cikin ƙauye ko birane,

 Sunan marar tsafta mai ƙazanta.

(Ɗahiru Jahun: Tsaftar Muhalli da Kewaye)

Wannan Sha’iri ya tavo wasu muhimman sassa da tsaftar xan Adam ya kamata ta taka rawa a cikinsu, wanda ya haxa da jiki, da muhalli ko mazauni. Abin da Sha’irin ke qoqarin nunawa shi ne, matuqar ana son lafiya ta wanzu a cikin al’umma a daina cututtuka, to wajibi ne sai an kula da tsaftar jiki da kuma ta muhalli domin, tsafta ita ke samar da lafiya a jikin mutane.

3.1.10    Ladabi da Biyayya

Kyautatawa ta fuskar daɗaɗawa da faranta rai ta hanyar biyayya ga umurnin magabata ko hukuma, da aikata abin da suke so, wanda ya dace da shari’a, shi ne biyayya.

Ladabi da biyayya manyan ƙusoshi ne a cikin tarbiyyar Hausa. Watau muhimman halaye ne da Bahaushe yake so ya ga ana yi. Girmama na gaba da kyautata wa na baya, su ne halayen da ake kira ladabi da biyayya (Zarruƙ da wasu 1988). Jigon ladabi da biyayya ya fito a waƙoƙin Alhaji Ɗahiru Musa Jahun in da ya ke nuni da yi wa hukuma da iyaye biyayya kamar haka;

Dukkan hukumar gaskiya,

Tsarin mutan Najeriya,

Jama’a mu bi ta da gaskiya,

 Shi ne alamun tarbiya.

 

Tutan ƙasarmu mu girmama,

Taken ƙasarmu mu girmama,

Dokan ƙasarmu mu girmama,

 Shi ne alamun tarbiya.

 

Mulkin ƙasa dai dole ne,

Bin masu mulki dole ne,

Dokar ƙasa dokar mu ne,

 Ta haɗe ƙasan nan bai ɗaya.

(Ɗahiru Jahun:Tarbiyya II)

Duk xa nagari ba zai qi yi wa iyayensa biyayya ba. Biyayya ga umurnin na gaba kuwa alamun tarbiyya ce domin, Hausawa na cewa ‘Bin na gaba, bin Allah’. Wataqila wannan ne ya sa Alhaji Xahiru Musa Jahun yake faxakar da mutane muhimmancin yi wa Shugabanni da manya biyayya. Ba shakka a cikin waɗannan baituka akwai cusa tarbiyyar biyayya ga jama’a dangane da bin doka da oda. Wato yi wa hukuma biyayya a kan dokokin da ta shimfiɗa wa ƙasa don kiyaye lafiyarsu.

3.1.11     Taimako

Taimako shi ne agaji ko tayawa (Bargery, 1993:976).

Haka kuma, taimaka (taimako) ya ƙunshi taya aiki, ko taimakekeniya a harkokin rayuwa, ko gudunmuwa ko kuma bayar da tallafi ko agaji ga mutum (Newman, 1997:123).

Taimako wani muhimmin jigo ne da ke kyautata tarbiyyar rayuwa, kuma akan taimaki wanda suka sani da waɗanda ba su sani ba. Saboda muhimmancin taimako wajen ƙarfafa tarbiyya ne tasa Alhaji Ɗahiru Musa Jahun yake cewa,

Mu haɗe mu fidda kitse wuta,

Wani za a gyara ko wata,

Don gyara dukkan karkata,

 Jama’a a maido tarbiya.

 

In za ka nuna halin ƙwarai,

In ka ci nama ka ci ƙwai,

Wani bai da shi maza taimakai,

 In dukiyarka da tarbiya.

(Ɗahiru Jahun:Tarbiyya II)

Kowane mutum na duniya yana son a taimaka masa a duk lokacin da ya shiga wani hali na tsanani. Irin hakan ne ke sa mutum ya kasa mantawa da wannan wanda ya taimaka masa komai tsawon zamani. Shi kuwa taimako ba kowa ke yin sa ba, sai mai tarbiyya. Wannan ne yasa Sha’irin ke nuna wa jama’a muhimmanci da amfanin taimakon mabuqaci a cikin baitukan da suka gabata.

4.1              Kammalawa

Tarbiyya ita ce ruhin kafuwa da ɗorewar kowace al’umma, wanda ya zama wajibi ga kowa ya mallaka, musamman yara a lokacin samartaka domin, inganta rayuwa. Duk wani ‘yantaccen mutum da tarbiyya yake bugun gaba. Ɗabi’ar mai tarbiya ba ta zama cuta domin, zai zamo abin alfahari da soyuwa ga mutane.

Tarbiyya a idon Bahaushe ta ƙunshi dogara a kan kyakkayawan ƙuduri da magana mai daɗi da kuma kyautata wa mutane, wadda takan inganta zamantakewa har ta kai mutum ya zama ƙaƙƙarfan tubali na gina al’umma ta gari. Abin da ake so shi ne mutum ya zama mai son ‘yan’uwansa mutane da soyayya ta haƙiƙa, da gaskiya da riƙon amana, da gujewa zargi da munanan halaye, da ƙana’a da taimako ta fuskar yi wa al’umma kyauta, wato ba su wani abu da ya ragu daga abin hannunsa, bisa jin daɗi da yardar zuciya

Buƙatuwar al’umma su tashi da waɗannan halaye ne ya sa marubuta waƙoƙin Hausa suka yi ta amfani da alƙalumansu domin, kira da ganin an raya wannan ɗabi’a, kamar yadda wannan maƙala ta zaƙulo irin waɗannan jigogi, a cikin wasu waƙoƙin Alhaji Ɗahiru Musa Jahun.

 MANAZARTA

Abubakar, A. (2001). An Introductory Morphology. Nigeria: Faculty of Arts, University of Maiduguri.

Abubakar, S. M. (1966). Hali Zanen Dutse. Zaria: Northern Nigerian Publishing Company.

Adamawa, A. (2007). Sirrin Kamalah. Bauchi: Adamawa Media Link.

Bugaje, H. M. (2013). Tarbiyya da Zamantakewar Hausawa: Jiya da Yau. Cikin Excerpts of International Conference On (Taɓarɓarewar Al’adun Hausawa) The Deterioration of Hausa Culture Organized by Katsina State History and Culture Bureau in Collaboration with Umaru Musa ‘Yar’adua University, Katsina.

Bunza, A.M. (2002). Yaƙi Da Rashin Tarbiya, Lalaci, Cin Hanci Da Karɓar Rashawa Cikin Waƙoƙin Alhaji Muhammadu Sambo Wali Basakkwace. Lagos: Ibrash Islamic Publications Centre Ltd.

Bunza, U. A. (2013). Tarbiya a Cikin Adabin Hausa: Tsokaci Daga Karin Magana. Cikin KADA Journal Of Liberal Arts Vol. 7 No. 1. Faculty Of Arts, Kaduna State University, Kaduna Nigeria.

Bunza, U. A. (2016). Matakan Kyautata Tarbiyya A Cikin Ƙagaggun Labarai: Wata Matakala Ta Samun ‘Yan Ƙasa Nagari. Maƙalar da aka gabatar a taron ƙara wa juna sani na ƙasa na farko, Tsangayar Fasaha da Nazarin Addinin Musulunci. Sakkwato: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo.

Bunza, U. A. (2016). Alamomin Gurbatar Tarbiyya Yara: Nazari Daga Wasu Littattafan Ƙagaggun Labarai. Sashen Koyar da Harsunan Najeriya. Sakkwato: Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo

CNHN, (2006). Ƙamusun Hausa. Zaria: Ahmadu Bello University Press.

Gusau, S. M. (1984). Tarbiyya A Ƙasar Hausa Jiya Da Yau. Maƙalar Da Aka Gabatar A Taron Ƙaddamar Da Ƙungiyar Hausa, Jami’ar Sakkwato.

Kirk-Greene, da A. H. M. (1973). “Mutumin Kirki: The Concept of Good Man in Hausa”. (Hans Wolf Memorial Lecture) Bloomington Indian. African Studies Program.

Mustapha, S. (2003). “Gurbin Gaskiya Cikin Adabin Hausa”. M.A. Dessertation. Sokoto: Department of Nigerian Languages, Usmanu Ɗanfodiyo University

Newman P. (2000). The Hausa Language: An Encyclopedic Reference Grammar. U.S.A.: Yale University Press.

Newman, R. M. (1997). An English-Hausa Dictionary. Nigeria: Longman Nigeria PLC.

Skinner, N. (1965). Ƙamus Na Turanci Da Hausa. Zaria: Northan Nigerian Publishing Company, Ltd.

Skinner, N. (1980). An Anthology of Hausa Literature. Zaria: Northern Nigerian Publishing Company.

Umar, M. H. (1980). Nuni Cikin Nishaɗi. Northern Nigerian Publishing Company Ltd.

Yahya, A. B. (2001). Dangantakar Waƙa Da Tarbiyar ‘Ya’yan Hausawa. Cikin Mujallar Harsunan Najeriya, XIX. Centre For The Study Of Nigerian Languages, Bayero University, Kano Nigeria.

Yahaya, I. Y. (1979). ‘Folklore As An Educational Tool’. In Harsunan Nijeriya IX. Center For The Nigerian Languages, Kano: Bayero University.

Yahaya, I. Y. (2005). Labarun Gargajiya 1. University Press PLC.

Zarruƙ, R. M. da Musa, I. U. da Alhassan, H. (1988). Zaman Hausawa: Bugu Na Biyu. Lagos: Academy Press Ltd.

Post a Comment

0 Comments