Ta
Abu-Ubaida SANI
Department of Languages and Cultures
Federal University Gusau, Zamfara
Phone No: 08133529736
Email: abuubaidasani5@gmail.com
Abu-Ubaida SANI
Department of Languages and Cultures
Federal University Gusau, Zamfara
Phone No: 08133529736
Email: abuubaidasani5@gmail.com
Wanda ya ƙaga yawan mancewa.
Ba don zuci akan mance ba,
Da mu yau duka mun zama gawa.
Domin da tuni an ta bala’i,
Kowa na riƙe haushin kowa.
Ƙara salati gun Manzonmu,
Alaye da sahabbai kowa.
Ya Sarkin da ya yi mu mutane,
Masu kure hanyar kaucewa.
Ya Sarki da ya sa mana tuba,
Idan mun yi ta kake yafewa.
Ya Sarki da ka yi mu ajuzai,
Tsakanin juna muke saɓawa.
Ya Sarkin da ya yo mana hanya,
Domin mu bi ta ga sasantawa.
Ya Sarki da ya sa mana rauni,
Rayin juna muke É“atawa.
Ya Sarki da ya ba mu dabaru,
Na rarrashi da fararrantawa.
Ya Sarkin da ya sa dokoki-
Da in an bi su ake dacewa.
Ya Sarkin da ya sa mana doka,
Amma ga shi muna karyawa.
Ya Sarki da ya tanada tuba,
Saɓonninmu yana yafewa.
Ya Sarkin da ya ba mu farillai,
Sai ko mutane muke tsallakewa.
Ya Sarkin da ya yo hanyoyi,
Idan mun tuba yake ƙyalewa.
Ya Sarkin da ya turo manzo,
Wanda gare mu yake tausayawa.
Ya Sarkin da ya nuffi da manzo,
Don a gare mu ya yo roƙawa.
Ya Sarkin da ya amsa kiransa,
Ba a kife mu har ran tsaiwa.
Ya Sarkin da ya ce mu yi roƙo,
In mun roƙa yake amsawa.
Ya Sarkin da shi ya hane mu,
Gun wani nasa mu yo roƙawa.
Ya Rabbani, na goggode,
Baiwarka gare ni ba yadawa.
Farko dai baiwar Musulunci,
Babu kwabo nai yo fansowa.
Kana baiwar nan ta mutunci,
Sai da nufinsa ake dacewa.
Ya Sarkin da yake sa natsuwa,
Ga zucin wanda ya yo dogewa-
Kan bautarsa da bin dokoki,
Ga duk alfasha yai kaucewa.
Ga bayinsa da suke dogewa-
Kan hanyar daidai da É—abi’u,
Da halayen da suke nunawa.
Ya Sarkin da idan ya yarda,
Da É—an Adam ya yo dacewa.
Domin shi ne zai saka yarda,
Nasa ga zuci na kowa da kowa.
Ya Sarkin da yake bayarwa,
Babu waninsa da za ya hanawa.
Manzo ya ce ko an taru,
Duk al’umma kowa da kowa-
Don a rage ka da ƙwayar zarra,
To ko sam-sam ba a iyawa.
Hakka idan kowa ya taru,
Mutum har aljan dukkan kowa-
Don a daɗe ka da ƙwayar zarra,
To lallai ba a ko iyawa.
Sai dai in Allah ne yas so,
Shi É—ai ke mulkin badawa.
Idan dai kenan har mun yarda,
Mun yi imani ba mu raba-
Cewa Allah shi É—ai ke yi,
Waninsa da É—ai ba ya ko iyawa.
To ko ba za mu wurin boka ba,
Shirka ba ma ko farawa.
Ya Sarkin da ya sa littafi,
Kan kowa tun kan haihowa.
Ya Sarki mai Lauhil Mahfuz,
Wanda cikinsa ake adanawa-
Dukkan samu koko rashinmu,
An zana ba ya gogewa.
Ya Sarki mai son Musulunci,
Cika-cikansa ya yo tsarawa.
ÆŠaya a cikinsu ko imani ne,
Da ƙaddara in tai aukowa.
Ko dai mai kyau ko mummuna,
Kadda su sa mana kafircewa.
Idan dai duk mun yarda da wannan,
To ko mu lura mu zam ganewa.
Cikinmu a bar samun mai zamba,
Ko cin hanci karɓar rashawa.
Don fa kuÉ—i ya yiwo tarawa.
Mai imani dole ya gane,
Wayo bai sa ai sauyawa.
Wayon bai ƙarar mu da komai,
Wai don dukiya mui tarawa.
Ba ya ko É—auke mana nauyi,
Sai ma gare mu ya zan ƙarawa.
Idan mun yarda da ikon Allah,
Neman tuwonmu muna gyarawa.
Mu nemi halal ziryan mu yi hamdan,
Kadan mun samu mun tarawa.
Idan ma babu mu dai ce hamdan,
Allah shi ne zai kawowa.
Idan muka doge kan wayonmu,
Ko da mali muna tarawa.
To mu tuna da hadisin manzo,
Sam Allah bai ko amsawa-
Ko da bawa ya yi du’a’i,
Idan dai haram yake taunawa.
Koko haram ya saka a jinkinsa,
Ko a haram yake kwantawa.
Ya Sarki da yai yi kashedi,
Kan bayin da ake cutarwa.
Mun ji batu bakin manzonsa,
Ya ce: “Allah na amsawa-
Du’a’in wanda ya sha zalunci,
Da ya yi Ilahu yake amsawa.”
In har dai mun yarda da ƙaulin,
Sata dole mu yo dainawa.
Dole muna tausan talakawa.
Dole mu lura da haƙƙin marayu,
Amanar tasu mu yo kamawa.
Dole mu daina ko tauye mudu,
Duk fannin ciniki kasuwa.
Dole uba ya kula ‘ya’yansa,
Ga su tarbiya ya yi bayarwa.
Dole mu’allim yab bi a sannu,
Ɗalibbansa ya rinƙa kulawa.
Kun ji mu lura mu bar zalunci,
Mu tsoraci Allah kan ran tsaiwa.
To ma in har mun tuna zance,
Ilahu da kansa yai furtawa.
Je ka ka duba cikin Kur’ani,
Alƙawari ne yai zanawa:
Dole Jahannama zai Æ™arewa.”
Sannan wataran mu muke gawa.
To da dole mu yo sauyawa.
Ba mu zama ‘yan kwakkwantarwa.
Yara dole mu bar sacewa.
Idan mun yarda muna shuÉ—ewa.
Mu sa natsuwa domin ganewa.
Ya wuce baki kawai furtawa,
Har ayyukanka suna nunawa.
Yanzu a ce an sa doka ne,
Kada mashin kowa ya hawowa.
An ba sojoji ko umarni,
Da an hau to su yiwo kamawa.
A nan to dole É—ayantar uku ne,
Ga su ko a jere ina ƙirgawa.
Ko dai ka ji tsoron wannan doka,
Hawan mashin ka yiwo dainawa.
Ko ka ji ba ka tsoron doka,
Ka hau kayinta ka yo takawa.
Koko ka zamto kana wasi-wasi,
Nan sa’arka ka yo jarabawa.
To in har mun yarda da Allah,
Mun ko aminta yana kamawa.
In mun yarda da akwai mutuwa,
Sannan raÉ—aÉ—inta akwai wahalarwa.
In mun yarda da kwanan kabari,
Mai ƙunci ko gwanin tsukewa.
In mun san da duhu na cikinsa,
Mai ban tsoro mai rikitarwa.
Har da kuna sukan tasowa.
In mun yarda yakan yo matsa,
Har awazu sai sun saɓawa.
In mun yarda yana da kaÉ—aici,
Kowa shi É—ai zai kwantawa.
In mun yarda da ba a motsi,
Ba a tashi ko juyawa.
Ba dama a yi numfasawa.
In mun yarda ƙaho za a busa,
Dukkaninmu mu yo tasowa.
In mun yarda da za a yi tsayuwa,
Har kowa sai ya ƙosawa.
Daidai kai za tai saukowa.
Da za mu karɓa ranar tsaiwa.
Idan da hagu mu kai amsawa.
In mun yarda da za ai hisabi,
Nan tambaya za mui amsawa.
In mun yarda da za a bi kadun,
Dukkan wanda mu kai cutarwa.
Sannan ta kansa ake takawa.
Tamkar haske suke gilmawa.
In sun hau shi suna faÉ—awa.
Sai sun jikkata za su wucewa.
Duk wani wanda ya yo kaucewa.
Har ya zarci gaban furtawa.
In mun yarda da din-din-din ne,
Bayan an mutu ba dawowa.
Har da bushasha ko holewa?
Mu fa mutane ne duka kowa.
To me ne zai sa mu yi ƙyashi?
Allah dai shi ke bayarwa
To me ne zai sa mu yi rowa?
Ilahu da ya so zai ƙwacewa.
Bayan Allah ya yi hanawa?
Tun da ko Allah na kamawa?
Kar mutuwarmu ta yo iskowa.
Tun da ko kullum mu kan hau titi,
Cikin motar da ake tuƙawa.
HaÉ—arin da ake yi har da macewa.
Wa ya sani ko mui gwabzawa!
Muna mota ta yiwo ƙwacewa!
Take ranmu a yo zarewa!
Ko gobara za tai tasowa!
Cikin ƙunci mu zamo ƙonewa!
Nan ajalin zai yo riskewa.
Take wuyanmu ya zam karyewa!
Da dukka Musulmi mai ganewa.
Amma hanyar tai saɓawa.
Wani ko a wahalce yake sheƙawa.
Sassauto mu yi daidaitawa.
Zuci ta ja ni na yo lulawa.
Har da su zagi nai ta sakawa,
Yanzu bayanin zan sauyawa.
Zuci da baki na yo gyarawa.
An ce ai na yo kwafsawa.
Na ga kurena nai gyarawa.
Na kuwa lura nai ganewa.
Lallai baki yai suɓucewa.
Na ga hakan ne nai amsawa.
Ni har ku mu yi daidaitawa.
‘Yammatan da suke tasawa.
Don ga samari kui burgewa.
Wanda gare ku yake turawa?
In kin bi shi yana zaɓowa.
Har dar in kin kama mutunci,
To na ƙwarai zai yo turowa.
Hakka matasa ‘yan holewa.
Kowane gaye zai yi matsowa.
Shi ma ya san ba shi da hali,
Don aurensa a yo É—aurawa.
Nan a gare ki yana bautawa.
Har zuciyarki ya zam kamewa.
Sai daga ƙarshe ya zam ya bar ki,
Da na sani ba ta maidowa.
Shigar banza ita ce wayewa.
A yanzu salo ne mai É“ullewa.
A gare ki ina son in faÉ—akarwa.
Babu na kirki ki yi dubawa.
Gane samari tantancewa.
Ki ce masa gidanku ya yo aikawa
Ba kya sake ga ya zagowa.
Gidanku a fari zai aikawa.
Duk wani mai son ki na haƙiƙa,
Ba ya bari ki shigar watsewa.
Don aurenki yake son yowa.
In fa tsiraici ki kai fiddawa.
Babu hijabi yai dubawa-
Ba ya son ki, ko farawa.
Sai dai a ce yana sha’awarki,
Alfasha ce yake tsarawa.
Da kin É—ora ya yo dubawa-
Zai ko ji kishi na tasowa.
Ko hannunki ya yo kamawa.
Wani shiri ne yake ƙullawa.
Marar bin Allah mai saɓawa.
Ko kallonsa yana gyarawa.
Balle taɓin ki, ko farawa.
Ba ƙima to ki yi ganewa.
Shirinsa daban ne ki yi dubawa.
Zai nunin hanyar É“ullewa.
Tattali ne hanyar dacewa.
Ga AC ya yiwo kullewa-
Mijin ƙwarai ba ya farawa.
Shi hirar shari’a aka yowa.
Da babu dalilin ai farawa.
Musulunci sosai ya yi hanawa.
Mutuncinki kike zubdawa.
Nufinsa bushasha rinƙa kulawa.
Burinsa Musulma mai kamewa.
Burinsa ya auro mai kyan nitsuwa.
Sai ya guje ki bai juyowa.
Don makaranta kin yi gamawa.
Gwanjo ce ki zanka tunawa.
Kuncen nan wa zai É—aurawa?
Sai ki ga aure ya zama aiki,
Sai da dabaru ai ta haÉ—awa.
Tun ma kafin tay yi gamawa-
Har sai ta yo tantancewa.
Auren nan ka ga ya É—orewa.
Shekarunki suna turawa.
Duk an san da kina zagawa.
Rayuwarki ta baya za ya tunawa.
Ya sister kin yarda da Allah,
Kan shi É—ai ne ke bayarwa?
Shin ko kin yarda haƙiƙa,
Jin daÉ—i shi ke samarwa?
Zama na ƙwarai shi ne ɓullewa-
Sai na ƙwarai kin yo zamtowa?
Riƙe Allah ɗai Sarkin kowa.
Miji na ƙwarai ko ki yo dacewa.
Har ‘ya’yanku su yo tasowa.
WanÉ—anda gare ki su kai haihowa.
Ko wata can ne zai riskewa.
Wanda ku girma ku tsofe tare,
Har mutuwarku ba ku rabewa.
To nan aƙ ƙarshen dacewa.
Alƙawari ne bar mantawa.
Dole gare ta a yo ramawa.
Gwara ka tuba ka zan gyarawa.
Ko da yaudara ce kai ƙullawa.
Sannan ne za kai ganewa.
Ya zama dole ku rinƙa kulawa.
Ciyar su halal da ka yo samowa.
Musulunci yadda ya yo nunawa.
Ba ta abinci kuÉ—in É“addawa.
In ka ƙi ita kan nemowa.
To É—aura mata babu tsayawa.
Babu sadaki ba shaidawa.
Nata ka bi su, ka ba ta kulawa.
Can a waje za ai ta biyawa.
‘Yar ki mutum ce tamkar kowa.
Sai an gamsu ake saidawa.
Idan ga riba ai sallamawa.
Ku da ita za kui faÉ—awa.
Nauyin kanki ki zam sauƙewa.
Dokar kana a tilastawa.
Na addini masu faÉ—akarwa.
Har ga du’a’i kui dogewa.
Albarka mu yiwo samowa.
Musamman jami’a nai leÆ™awa.
Ranar mutuwa ranar tsaiwa.
Kukan sa koko ku yi hanawa.
Lada ne za kai samowa.
Shiga laccar da kake koyarwa.
Kay yi nasiha cike da ƙwarewa.
Yadda batun za sui kamawa.
Da dai ku naka yi dattawa.
Su ke sa a riƙa gyarawa.
Tarbiya ta yi lalacewa?
Kowanenmu ya yo gyarawa.
Saura gare shi su zanka tunawa.
Wanda gabanmu yake shinkewa.
A kan hanyar da take É“ullewa.
Dukka kurenmu ka yo yafewa.
ÆŠan Sani nake mai dubawa.
Arba’in da shida sannan É—orawa.
Na yi addu’ar samun dacewa.
Da shi Allah sa mu yiwo ganawa.
wow! I like it
ReplyDelete